Sashe 45
Gudun Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita anti Yagana haka take idan ranta ya baci duk abinda ya zo bakinta fad'a take ko ka mutu ko kayi rai bai dameta ba.
Cikin kumfar baki da tayar da jijiyar wuya don har sai da Anti Sakina ta fito daga d'akin ta tsaya a dokin kofa jin hayaniya na tashi.
Hadiza cigaba da cewa." To anti Yagana da kike cewa duk abinda ya same ni na gaya miki ko an fada miki ni ma haka zan zauna a tsiyace, bari fa ki ji arzikin nan Allah ne yake bayar dashi ba wani d'an iska ba, itama Aminar ai takarsa tayi bata gada a wajan uwa da uba ba.
Kuma wanda ta yi kafin aure ai na zina ne wanene bai sani ba, fasikanci tayi tana tallata surar jikinta a duniya wanene ya san iya adadin manyan mutanan da suka nema ta har ta tara dukiyar.
Idan lokacina ya yi wallahi daka ke har ita sai kun jira aikin banza aikin......Ai ba ta jira ta k
rasa ba ta kashe wayarta jikinta yana 'bari ta zauna a saman kujera tana kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! wai Hadiza ce take kiran Amina da karuwa saboda abin duniya.
Ba ta yi mamaki ba domin dama can sun nuna mata kiyayya.
Tunda take bata ta'ba nuna bambanci tsakanin 'yan uwanta ba, duk ta daukesu daya da Aminar da suka fito ciki daya.
Ko yau Amina ta yi lefi kwatankwacin irin wanda Hadizan ta yi sai ta ci mutuncina wata'kila ma nata ya fi na Hadizan, amma ta girgiza mutuka da gaske da jin wannan furucin daga bakinta..
Ba ta ha'kura ba dai ta kira Fati a waya suka gaisa sosai nan ta fara tambayata yanayin ciwon nata.
Fati ta ce." Typhoid ne ya matsa mini anti wallahi har sai da naje gida akayi mini 'karin ruwa kwanana biyar sannan na dawo.
Amma yanzu da sau'ki sosai jikin."
Anti Yagana ta girgiza kai cikin damuwa ta ce.' Allah ya kara sauki Fati ki yi hakuri da yadda kika samu rayuwa kowane bawa akwai kaddarsa ki zauna ki kula da yaranki ki basu tarbiya sosai tunda duk rintse ko babu dad'i mijinki zai baku ku ci to kiyi ha'kuri kada ki yi sha'awar fitowa domin lamarin ba zai miki kyau ba, duk abinda kike buk'ata ki gaya mini ta waya muddin bai fi karfina ba zan yi miki in sha Allahu rabbi."
Cike da jin dadi ta ce." To na gode sosai anti Allah ya saka da alheri.
Su kayi sallama bayan ta yi mata al'kawarin tura mata kudi a daran ranar tunda tana da lambar asusunta wanda dama sa'i da lokaci tana yi mata alheri.
Wayarsu da Fati ya tabbatar mata cewa itama bata san abinda Hadizan ta shirya ba wanda har ta jingina mata ciwo.
B'angaran ita Fatin din kuwa Hadiza ta bukaci asusunta aro inda ta ce mata mijin Amina ne zai bata jarin Amma ita Fati din bata ganin alert sakamakon matsalar da asusun ya samu sai dai duk sanda aka tura mata kudi a kira ta a gaya mata an tura abu kaza dama ba wani ajiya take yi dashi ba shiyasa ma bata ta'ba transfer ba.
Yanzu ATM din yana hannun Hadiza tana ta zurga-zurgar zuwa banki domin fitar da kudin.
Anti Sakina ta fashe da dariya tana daga tsaye a dokin kofar dakinta ta ce ." Yau dai karshen kumbiya-kumbiya ya kare kunnena ya ji abinda kuke ta boyewa.
Ke yanzu don Allah Hadiza ba ki ji kunya ba.
Shi fa sharri dan aike ne, duk inda ya je zai dawo.
Ki ci ki sha daga taskar Amina amma kike bin ta da kazafi irin na zina.
Kin je gidanta kin share watanni kin yi bul bul hakan bai ishe ki ba sai da ki ka damfaro makudan kudi da karyar ciwo, amma saboda 'kin gaskiya kin zo kina kumfar baki wallahi duk wanda ya ce tukunyar wani ba zata tafasa ba tasa ma ko d'umi ba zata yi ba, kun ji kunya daka ke har uwarki kuma wallahi tallahi sai na gayawa babanku abinda kuka yi."
Hadiza cikin fitsara ta ce." To ki gaya masa mana sai me idan kin gaya masa aikin banza da wofi 'yar b'akinciki ai mun fi kusa da ita tunda uba muka had'a ke kuwa fa."
Anti Sakina ta ce." Sakarai kawai haka zakiyi ta zagari a gari tunda zuciyarki bata da kyau."
Ummantasu tana ji suna cacar baki ba tace komai ba, ba kuma ta da niyyar tsawatarwa da Hadizan akan ta yi shiru tunda duk lalacewarta ai matar ubanta ce.
Daga karshe dai anti Sakinar ita ta gaji ta yi shiru hakan ma ya faru ne sakamakon shigowar Usaini shine babban d'anta, ya hanata magana tare da tura ta d'aki ya fito bai kalli inda Hadizan take tsaye ba tana ta zuba ruwan ashariya kamar 'yar maguzawa.
Dama basa magana sakamakon yana jin haushin rashin kunyar da takewa babarsu shiyasa kawai ya fita daga harkarta.
Saminu ne idan yana gidan bai fita yawon gwangwan d'insa ba yake shigarwa Umman tasu har akwai ranar da ya d'auko d
utse irin na wuta daga waje ya saita Hadizan ya jefa mata Allah ya kiyaye ya sauka a gefan kafarta.
Ta kama shi da duka kuwa shi kuma yana ta d'ura mata ashariya, da k'yar Ummansu ta kwace shi daga hannunta.
Wani irin zaman lafiya muke yi kamar ba sabon ango ba sai wani lallaba ni yake yi yana ji da ni.
Ban yi mamaki ba domin duk namijin da zai kara aure indai mai ilimi da hankali ne yakan fito da dabaru domin tausar zuciyar uwar gida.
Aka ba ni kudin dannar kirji miliyan sha biyu da kujerar umara.
Na dinga godiya kuwa ina ta Tsallen murna sam na ki nuna damuwata duk kuwa da cewa abin yana ta damuna.
Na ji dadin kujerar umarar dana samu hankalina zai fi kwanciya idan na dan yi nesa har su gama cin amarcinsu tukkuna.
Sahura ta dame ni akan lallai ni ma fa sai na kara gyarawa da muna waya kwanaki na ce mata ni koyaushe a cikin gyara nake ni kaina na sheda ni'ima ta wadace ni.
Ina Kuma jimanta yadda zan yi tsayin kwana bakwai ba tare da shi ba domin kuwa Allah ne da kullum duk dare sai mun yi, a wasu lukutan ma har breakfast muke yi kafin na sakko daga samansa nasa shine kawai idan na tuna yake damuna domin kuwa na yi mugun sabon da zan ji jiki mutuka da gaske.
Inna Uwani tuni ta tafi tunda d'aurin auran ya rage sati daya ta tattara ta tafi bayan ta kwamushi kudi a wajensa, shi dai Allah ya taimakeshi abin duniyarsa bai rufe masa ido ba, gashi bai iya kyauta ba da yawa yake bayarwa.
Yau saura kwana biyu d'aurin aure mai kitso da k'unshi ta zo har gida ta yi mini ja da baki.
Kitson kuwa cewa na yi tayi mini irin na mu na bare bari na gaba tayi mini tunda ba lefi akwai sumar.
Ya kuwa burge shi sosai saboda rashin abinyi har sai da ya lissafa kitson tamaninin da daya ne.
Ni dai dariya kawai nake yi masa.
Duk kiran da Hauwa za ta yi masa baya d'agawa a gabana, sai ma ya sanya wayar a jirgi ya share.
Cikin zuciyata na yi ta jin dad'i ganin babu boka babu Malam na kame zuciyar abina wanda ni kad'ai na san sirrin faruwar hakan.
Wato kishi bala'i ne ban ta'ba gazgatawa ba sai da maigidan ya kira ni a waya yake tabbatar mini da cewa an dauransa da Hauwa yanzu amma ba zai sake kwana ba komai dare a gida zai dawo.
A lokacin k'irjina nauyi ya yi mini bayana ya rike ulcerta tana neman tashi wadda tun ina budurwa rabon data motsa mini.
Na daure zuciyata sosai domin Ina so na cigaba da nuna masa Ina maraba da zuwan amaryarsa amma har cikin zuciyata na ji dad'in jin ya ce ba zai sake kwana ba, domin kuwa babu abinda ya zo mini a raina da ya gaya mini an dauran auran sai zai iya nemanta tunda ai ta zama mallakinsa.
Cikin 'yar dariya dana kalato na furta." Kai kuwa ranka ya dad'e ka kwana ma gobe da wuri sai ka taso."
Ya furta."A a zan dai dawo domin Ina da damuwa ke kanki kin sani hidimar nan ce ta d'auke mini hankali amma tunda an d'aura alhmdullhi itama gobe zasu kawota......
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/3, 8:38 PM] matar mijinta: *Wannan littafin na kudi ne 1k akan telegram.
Normal What'sapp group #700 hanyar da za a biya kudin ita ce wannan...0542382124...Binta Umar gtbank ko kuma 7084653262...Binta Umar Opey bank.
'Yan nijar dala dari katin airtel za ku tura mini bayan kun kankare hoton.
A tura da sheda ta wannan lambobin iya What'sapp kawai.*
*07084653262*
*08089965176*
*V-VIP AREWA PEN
*TALLAH!*
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa.
Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono.
To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba.
Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu.
Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya.
Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne.
To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji.
Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba.
Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu.
In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi.
Cikin kumfar baki da tayar da jijiyar wuya don har sai da Anti Sakina ta fito daga d'akin ta tsaya a dokin kofa jin hayaniya na tashi.
Hadiza cigaba da cewa." To anti Yagana da kike cewa duk abinda ya same ni na gaya miki ko an fada miki ni ma haka zan zauna a tsiyace, bari fa ki ji arzikin nan Allah ne yake bayar dashi ba wani d'an iska ba, itama Aminar ai takarsa tayi bata gada a wajan uwa da uba ba.
Kuma wanda ta yi kafin aure ai na zina ne wanene bai sani ba, fasikanci tayi tana tallata surar jikinta a duniya wanene ya san iya adadin manyan mutanan da suka nema ta har ta tara dukiyar.
Idan lokacina ya yi wallahi daka ke har ita sai kun jira aikin banza aikin......Ai ba ta jira ta k
rasa ba ta kashe wayarta jikinta yana 'bari ta zauna a saman kujera tana kiran Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un! wai Hadiza ce take kiran Amina da karuwa saboda abin duniya.
Ba ta yi mamaki ba domin dama can sun nuna mata kiyayya.
Tunda take bata ta'ba nuna bambanci tsakanin 'yan uwanta ba, duk ta daukesu daya da Aminar da suka fito ciki daya.
Ko yau Amina ta yi lefi kwatankwacin irin wanda Hadizan ta yi sai ta ci mutuncina wata'kila ma nata ya fi na Hadizan, amma ta girgiza mutuka da gaske da jin wannan furucin daga bakinta..
Ba ta ha'kura ba dai ta kira Fati a waya suka gaisa sosai nan ta fara tambayata yanayin ciwon nata.
Fati ta ce." Typhoid ne ya matsa mini anti wallahi har sai da naje gida akayi mini 'karin ruwa kwanana biyar sannan na dawo.
Amma yanzu da sau'ki sosai jikin."
Anti Yagana ta girgiza kai cikin damuwa ta ce.' Allah ya kara sauki Fati ki yi hakuri da yadda kika samu rayuwa kowane bawa akwai kaddarsa ki zauna ki kula da yaranki ki basu tarbiya sosai tunda duk rintse ko babu dad'i mijinki zai baku ku ci to kiyi ha'kuri kada ki yi sha'awar fitowa domin lamarin ba zai miki kyau ba, duk abinda kike buk'ata ki gaya mini ta waya muddin bai fi karfina ba zan yi miki in sha Allahu rabbi."
Cike da jin dadi ta ce." To na gode sosai anti Allah ya saka da alheri.
Su kayi sallama bayan ta yi mata al'kawarin tura mata kudi a daran ranar tunda tana da lambar asusunta wanda dama sa'i da lokaci tana yi mata alheri.
Wayarsu da Fati ya tabbatar mata cewa itama bata san abinda Hadizan ta shirya ba wanda har ta jingina mata ciwo.
B'angaran ita Fatin din kuwa Hadiza ta bukaci asusunta aro inda ta ce mata mijin Amina ne zai bata jarin Amma ita Fati din bata ganin alert sakamakon matsalar da asusun ya samu sai dai duk sanda aka tura mata kudi a kira ta a gaya mata an tura abu kaza dama ba wani ajiya take yi dashi ba shiyasa ma bata ta'ba transfer ba.
Yanzu ATM din yana hannun Hadiza tana ta zurga-zurgar zuwa banki domin fitar da kudin.
Anti Sakina ta fashe da dariya tana daga tsaye a dokin kofar dakinta ta ce ." Yau dai karshen kumbiya-kumbiya ya kare kunnena ya ji abinda kuke ta boyewa.
Ke yanzu don Allah Hadiza ba ki ji kunya ba.
Shi fa sharri dan aike ne, duk inda ya je zai dawo.
Ki ci ki sha daga taskar Amina amma kike bin ta da kazafi irin na zina.
Kin je gidanta kin share watanni kin yi bul bul hakan bai ishe ki ba sai da ki ka damfaro makudan kudi da karyar ciwo, amma saboda 'kin gaskiya kin zo kina kumfar baki wallahi duk wanda ya ce tukunyar wani ba zata tafasa ba tasa ma ko d'umi ba zata yi ba, kun ji kunya daka ke har uwarki kuma wallahi tallahi sai na gayawa babanku abinda kuka yi."
Hadiza cikin fitsara ta ce." To ki gaya masa mana sai me idan kin gaya masa aikin banza da wofi 'yar b'akinciki ai mun fi kusa da ita tunda uba muka had'a ke kuwa fa."
Anti Sakina ta ce." Sakarai kawai haka zakiyi ta zagari a gari tunda zuciyarki bata da kyau."
Ummantasu tana ji suna cacar baki ba tace komai ba, ba kuma ta da niyyar tsawatarwa da Hadizan akan ta yi shiru tunda duk lalacewarta ai matar ubanta ce.
Daga karshe dai anti Sakinar ita ta gaji ta yi shiru hakan ma ya faru ne sakamakon shigowar Usaini shine babban d'anta, ya hanata magana tare da tura ta d'aki ya fito bai kalli inda Hadizan take tsaye ba tana ta zuba ruwan ashariya kamar 'yar maguzawa.
Dama basa magana sakamakon yana jin haushin rashin kunyar da takewa babarsu shiyasa kawai ya fita daga harkarta.
Saminu ne idan yana gidan bai fita yawon gwangwan d'insa ba yake shigarwa Umman tasu har akwai ranar da ya d'auko d
utse irin na wuta daga waje ya saita Hadizan ya jefa mata Allah ya kiyaye ya sauka a gefan kafarta.
Ta kama shi da duka kuwa shi kuma yana ta d'ura mata ashariya, da k'yar Ummansu ta kwace shi daga hannunta.
Wani irin zaman lafiya muke yi kamar ba sabon ango ba sai wani lallaba ni yake yi yana ji da ni.
Ban yi mamaki ba domin duk namijin da zai kara aure indai mai ilimi da hankali ne yakan fito da dabaru domin tausar zuciyar uwar gida.
Aka ba ni kudin dannar kirji miliyan sha biyu da kujerar umara.
Na dinga godiya kuwa ina ta Tsallen murna sam na ki nuna damuwata duk kuwa da cewa abin yana ta damuna.
Na ji dadin kujerar umarar dana samu hankalina zai fi kwanciya idan na dan yi nesa har su gama cin amarcinsu tukkuna.
Sahura ta dame ni akan lallai ni ma fa sai na kara gyarawa da muna waya kwanaki na ce mata ni koyaushe a cikin gyara nake ni kaina na sheda ni'ima ta wadace ni.
Ina Kuma jimanta yadda zan yi tsayin kwana bakwai ba tare da shi ba domin kuwa Allah ne da kullum duk dare sai mun yi, a wasu lukutan ma har breakfast muke yi kafin na sakko daga samansa nasa shine kawai idan na tuna yake damuna domin kuwa na yi mugun sabon da zan ji jiki mutuka da gaske.
Inna Uwani tuni ta tafi tunda d'aurin auran ya rage sati daya ta tattara ta tafi bayan ta kwamushi kudi a wajensa, shi dai Allah ya taimakeshi abin duniyarsa bai rufe masa ido ba, gashi bai iya kyauta ba da yawa yake bayarwa.
Yau saura kwana biyu d'aurin aure mai kitso da k'unshi ta zo har gida ta yi mini ja da baki.
Kitson kuwa cewa na yi tayi mini irin na mu na bare bari na gaba tayi mini tunda ba lefi akwai sumar.
Ya kuwa burge shi sosai saboda rashin abinyi har sai da ya lissafa kitson tamaninin da daya ne.
Ni dai dariya kawai nake yi masa.
Duk kiran da Hauwa za ta yi masa baya d'agawa a gabana, sai ma ya sanya wayar a jirgi ya share.
Cikin zuciyata na yi ta jin dad'i ganin babu boka babu Malam na kame zuciyar abina wanda ni kad'ai na san sirrin faruwar hakan.
Wato kishi bala'i ne ban ta'ba gazgatawa ba sai da maigidan ya kira ni a waya yake tabbatar mini da cewa an dauransa da Hauwa yanzu amma ba zai sake kwana ba komai dare a gida zai dawo.
A lokacin k'irjina nauyi ya yi mini bayana ya rike ulcerta tana neman tashi wadda tun ina budurwa rabon data motsa mini.
Na daure zuciyata sosai domin Ina so na cigaba da nuna masa Ina maraba da zuwan amaryarsa amma har cikin zuciyata na ji dad'in jin ya ce ba zai sake kwana ba, domin kuwa babu abinda ya zo mini a raina da ya gaya mini an dauran auran sai zai iya nemanta tunda ai ta zama mallakinsa.
Cikin 'yar dariya dana kalato na furta." Kai kuwa ranka ya dad'e ka kwana ma gobe da wuri sai ka taso."
Ya furta."A a zan dai dawo domin Ina da damuwa ke kanki kin sani hidimar nan ce ta d'auke mini hankali amma tunda an d'aura alhmdullhi itama gobe zasu kawota......
*GARKUWAR MATA.*
*BINTA UMAR ABBALE*
[6/3, 8:38 PM] matar mijinta: *Wannan littafin na kudi ne 1k akan telegram.
Normal What'sapp group #700 hanyar da za a biya kudin ita ce wannan...0542382124...Binta Umar gtbank ko kuma 7084653262...Binta Umar Opey bank.
'Yan nijar dala dari katin airtel za ku tura mini bayan kun kankare hoton.
A tura da sheda ta wannan lambobin iya What'sapp kawai.*
*07084653262*
*08089965176*
*V-VIP AREWA PEN
*TALLAH!*
*DA MAGANI A GONAR YARO!!*
*08089965176*
*07084653262*
*Dayawa akwai matan da suke da matsala ta lalacewar nono yamushewa da kuma fad'uwarsa.
Wasu ma 'yan mata ne basu kai ga matakin aure da shayarwa ba amma sai su samu matsalar faduwar nono.
To gaskiya akwai magani sai dai kawai idan ba a yi dace ba.
Wasu zasuyi ta faman kashe kudi amma buk'ata bata biya ba, wasu kuma zasuyi ta fargaba kada su je garin neman gira a rasa Ido, ma'ana su sayi abinda zai cutar dasu da kudinsu.
Kuma yanzu dai tsakani da Allah rijalu sun riga sun gama nuna abinda suka fi karkata a kansa a jikin 'ya mace kirji da kuma baya.
Wasu Allah ya hallice su dashi har ya yi musu yawa, wasu kuwa basu dashi kuma mai saurin zubewa ne.
To mu dai duk wanda ya san maganinmu ya san ingantacce ne, kuma Yana aiki kwarai da gaske wurin dawo da daraja da martabar nono da izinin Ubangiji.
Sahihin magani ne da ya samu sheda da lambar yabo, kuma Islamic ne da akayi masa hadi mai inganci domin gyara jikin mace ba ma iyakacin nono kawai ba.
Babu nadama haka zalika babu dana sani da asarar dukiya wurin sayan maganinmu.
In sha Allah matsalar ki zata gushe idan kin jarraba amfani dashi.