Sashe 199
Gudun Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muna sayar da sabulan gyaran jiki dilka da man gyaran gashi, muna kuma bayar da sari a fad'in najeria da nijar muna tura kayanmu kowane gari da ikon Allah.*
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu.
Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
*Gudun aure littafin kudi ne complete 2k akan telegram normal What'sapp group 1k via 0542382124....
Binta Umar gtbank*
*07084653262*
*134*
Ina tsaka da mamakin abinda Hauwa ta aikata ya shigo dakin ransa a 'bace ganin haka ya sanya ni daidaita yanayin fuskata.
Fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba duk akan na d'auki magani na bawa Hauwa kamar zai mangareni da duka.
Na yi shiru kawai ina jinsa ban tanka masa ba ya gama da fad'in na tashi na je na kar'bo masa maganinsa.
Nan fa d'aya na ce ba zan je ba na nemi waje na kwanta raina gabad'aya a b'ace wai shin yaushe za mu samu zaman lafiya ne a gidan nan.
Ni a ganina abinda na yi shine daidai da adalci ban d'auka cewa zai zama lefi tunda ai shima yana son lafiyarsa
Me yasa ya amsawa mahaifiyarsa ya san bai shirya cigaba da zama da ita ba.
Ba ni so daidai da kwayar zarra hakkinta ya kama ni.
A yanayinta dai sulhu da sasanci take nema tunda har ta iya yin ado da kwalliya dominsa ta kuma bi shi dakinsa to ai sai ya yi hakuri ya yafe tunda zahiri shi ma yana yi mana lefin kuma ha'kuri yake yi da ita.
Ina kallonsa ya shiga toilet dina ya yi uzurinsa ya fito d'aure da alwala ya zauna saman dadduma ya bude Al'kur'ani mai girma yana karantawa daga tsakiya suratul-kahfi sai da ya kammala ya rufe al'kur'anin bai nade daddumar ba ya kwanta a samanta tare da takurewa kamar wani maraya.
Na tashi zaune ina duban bayansa da mamakin abinda ya yi akan ya yi wa Hauwa magana ko ya kwana d'aki daya da ita gwara ya kwanta a kasa bisa dadduma wace irin zuciya ce wannan ta riko da gaba mai tsanani.
Ina ta yi masa magana ya yi mini shiru kuma idonsa biyu tunda ina ganin haske wayarsa yana dubawa.
Na sauko daga gadon hijabina na sanya na bude d'akin na fita dole na kar'bo maganin na shafa masa tunda na lura shi akan hakan sai dai duk abinda zai faru ya faru ga lafiyarsa amma ba zai kwanar mini a d'aki ba balle ta fahimci haka ta ji haushi ko ta zarge ni.
Na bubbuga kofar d'akin nata ta zo ta bude mini ta yi sabon wanka cikin kayan bacci tana kamshi na ce." Maganin nan za ki ba ni."
Sai ta yi kasa'ke tana kallona cikin nazari na yi kasa da kaina ina jinta tana fad'in." Yanzu nan fa na gama shiri zuwa saman ya dawo ne?''
A tak'aice na ce." E, shine ya ce a bashi." Ta juya jikinta a sanyaye ta d'auko mini na kar'ba na ja mata kofar.
A zaune na same shi yana waya ya gama ya koma ya kwanta bai dube ni ba.
Na daura tare da furta." Ga maganin na kar'bo."
Ya yi mini shiru bai ce komai ba.
Shiru d'akin ya d'auka kusan minti goma sha biyar ba shi da niyyar tashi ya d'auki maganinsa ya fita.
Na ce." Ni fa wallahi ba zan yadda da wannan rayuwar ba.
Ba zan ta'ba amincewa na zalinci wata ba mu yi maganar gaskiya a tsakaninmu kada ka so zuciyarka akan duk abubuwa da suka faru Hauwa matarka ce kuma 'yar uwarka ni kuma na dauketa abokiyar zamana tunda ka ce na kar'bo maka maganinka gashi ka tashi ka tafi wajenka ta sameka a can shi yafi alheri."
Uffan bai ce mini ba sai ya mika hannu ma ya d'auko fillo daya daga cikin wad'anda suke jere a saman gadona ya gyara kwanciyarsa.
raina ya b'aci sosai na kwanta jikina a sanyaye ina kallon bayansa da tarin mamakin abinda yake yi.
Ni dai anan ban ga lefin da na yi ba kuma da zai tsiri jin haushina.
Damuwa ta cunkushe mini da fargaba domin yadda ya yi zuciya da kallon inda nake haka yake so ya yi wa lafiyarsa mugunta.
Kaina ya fara sarawa tsabar takaici na rintse idona domin kirkiro bacci amma nasan ba zai ta'ba zuwa ba.
Can na fara jin saukar numfashinsa alamar bacci ya d'auke shi.
Na tashi zaune da sauri da mamaki da gaske yake yi
Na zuro 'kafata kasa ina le'ka fuskarsa bacci yake sosai kuma cikin kwanciyar hankali.
Na tashi na je na d'auko kayan maganin na zauna kusa da shi tare da d'an bubbuga fillon da yake kwance ya bud'e Ido yana kallona da yanayin bacci.
Na ce." Ka tashi na shafa maka."
Ya tashi kamar yadda na umarce shi da kansa ya cire kayan jikinsa.
Ban ce komai ba na fara shafa masa yana ta bina da kallo har na gama bai yi magana ba ya mayar da rigarsa da wandonsa na ciki ya koma ya kwanta.
A haka muka kwana a d'akin kai da gindi.
Sai da asuba ya fita bai kuma kula ni ba.
Na kasance cikin mamaki sosai shikkenan daga gyara kayanka Allah Ya sawwa'ke.
A haka kwana biyun da Hauwa ya kamata ta yi da shi suka shud'e a banza ba ma ya yarda ya kwanta a dakinsa balle ta biyo shi sai ya taho nawa ya kwanta kuma ba zai mini magana sai dai idan na gaji na yi masa idan na zo na shafa masa maganin sannan yake amsa mini amma bai ri'ke mini hannu ba balle ya ce zai nemi wani abu.
ranar da na kar'bi girki da yamma na shiga kicin domin hada masa fruit-salad kamar yadda ya buk'ata.
Baba Tabawa da Taburni suna ta hidimar abinda za a ci daddare.
Muka gaisa kafin na ji maganar Baba tana fad'in.
" Ban da abinki Taburni ai ba ita ta d'auke ki aiki ba to me zai sanya ki damu da abinda ta ce don Allah ki yi hakuri me yasa za a yi ta maimaita magana d'aya."
Na ce." Menene kuma?''
Murmushi ta yi tana fad'in." Ita da Hajiya Hauwa da alama jininsu bai hadu ba tun bayan dawowarta kafin ku dawo ke da maigidan su ka d'an yi sa'insa abin dai babu arziki da b'angaran Hajiya Hauwa kamar yadda ki ka san halinta na cin mutunci wallahi har da zagi wai zamansu ba shi da amfani mun had'u har da ni munafurcin banza. daga lokacin ko Taburni ta gaisheta ba ta amsaw.........." To me zai sanya ni amsawa Tabawa"
Muryar Hauwa ta katse maganar Baba Tabawa gabad'aya muka juya muna kallonta.
Ni mamaki ne ma ya kama ni yadda yau ta kira Tabawa kai tsaye babu ma Baba dukkaninsu dattijai ne cikinsu babu wadda ba ta haife mu ba ai rashi ba hauka ba ne don suna masu aiki sai su zama wulakantattu."
Ta shigo kicin din sosai tana fad'in." Baba Tabawa tunda Amina ta dawo ki 'kara kuzarin gulma da munafurci yanzu don Allah ba ki ji nauyi da kunya ba da girmanki da shekarunki?
saboda ni ba ni da kudi ba na baki toshiyar hanci shiyasa ba ki d'auke ni a matsayin matar gida ba.
Matsiyaciyar matar can wadda ta yi mutuwar wulakanci tun tana raye kike maula da yi mata fadanci kada ki ce na manta duk abinda zai faru ba ki ta'ba goyon bayana ba Amina da Maryam sune mutane tunda suna sinna miki.
To a shirye na dawo na gaya miki kowane sakarai da sha'kiyyi zan daidaita masa zama wallahi na kuma fad'a Mairo da Taburni sai kun bar gidan nan domin duk wani abu da ya danganci matsafiyar matar can najasa ne ba za ku hana mala'ikun rahama shigo mana gida ba."
Baba Tabawa duk yadda ta kai ga daurewa sai da ta fashe da kuka ta sanya tafin hannunta ta 'kunshe bakinta hawaye share-share a kumatunta.
Tunda na d'auki baiwar Allah nan aiki tsayin shekaru kusan biyar tsakanina da ita alheri ne da kyautatawa da wasa da dariya amma yau Hauwa ta dubi tsabar idonta tana kiranta da munafukai shakiyya sakarai.
Taburni ta jingina a jikin wardrobe din kicin din tare da sunkuyar da kanta.
Bakincikin da nake ciki ya sake hauhawa ai na d'auka ta yi sanyi ta dawo ne domin ta gyara kuskuran da ta yi mu zauna lafiya ashe ba haka ba ne a zuciyarta da wani shirin ta zo.
Na dube ta sosai ina fad'in." A matsayinki na wa za ki sanya su barin gidan ko ke ce ki ka d'auke su aiki ki ke biyansu?"
Ta gyad'a kanta tana cewa." A matsayina na matar gida kamar yadda ki ke matar gida ko da bambanci ne a tsakaninmu."
Na ce." Da bambanci kwarai da gaske Hauwa Ina so na gaya miki ki gyara kalamanki akan wad'an nan dattijan Annabi Muhammadu s.a.w ya ce ka girmama furfura ko ta wacece ke yanzu don Allah ba ki ji kunyar duban tsabar idon Baba Tabawa kin gaya mata wannan maganganun ba."
Ta ta'be baki tana fad'in." Ita ba ta ji kunyar abinda take yi ba ai munafukar tsohuwa ce."
Na buga mata tsawa sosai ina fad'in." Wallahi tallahi Hauwa za mu yi ta dake gidan nan akan wad'an nan da suke tsaye na gaya miki."
Ta girgiza kanta tana fad'in.'' Na ji duka to Amina na ce ki rufe ni da duka."
Na ja tsaki kawai ban sake wata magana ba na juya bangaransu ina ba su ha'kuri zuwa lokacin itama Taburni kukan take yi tana fad'in." Shiyasa na ce fa tafiya zan yi cikin iyalina na yi abinda na yi Hajiya Amina ba na so a kaskantani ki yi hakuri ni ba ki yi mini komai ba amma don girman Allah ki sanya a mayar da ni k'auyenmu.
Na ji 'kwalla ta ciko kwarmin idona na dubi Baba Tabawa da take goye da Sultan a bayanta yana ta bacci idonta duk ya kumbura tsabar kukan da ta jima ba ta yi irinsa ba.
*Muna garin kano duk inda kake za mu aika maka da kayanmu.
Domin neman karin bayani sai a yi mana magana ta Whasap ga lambobin da za a same mu a kai.*
*07084653262 ko*
*08089965176*
*SIYAN NAGARI!!!!!!*
*A JARRABA A SAMU BIYAN BUKATA DA YARDAR ALLAH*
*Gudun aure littafin kudi ne complete 2k akan telegram normal What'sapp group 1k via 0542382124....
Binta Umar gtbank*
*07084653262*
*134*
Ina tsaka da mamakin abinda Hauwa ta aikata ya shigo dakin ransa a 'bace ganin haka ya sanya ni daidaita yanayin fuskata.
Fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba duk akan na d'auki magani na bawa Hauwa kamar zai mangareni da duka.
Na yi shiru kawai ina jinsa ban tanka masa ba ya gama da fad'in na tashi na je na kar'bo masa maganinsa.
Nan fa d'aya na ce ba zan je ba na nemi waje na kwanta raina gabad'aya a b'ace wai shin yaushe za mu samu zaman lafiya ne a gidan nan.
Ni a ganina abinda na yi shine daidai da adalci ban d'auka cewa zai zama lefi tunda ai shima yana son lafiyarsa
Me yasa ya amsawa mahaifiyarsa ya san bai shirya cigaba da zama da ita ba.
Ba ni so daidai da kwayar zarra hakkinta ya kama ni.
A yanayinta dai sulhu da sasanci take nema tunda har ta iya yin ado da kwalliya dominsa ta kuma bi shi dakinsa to ai sai ya yi hakuri ya yafe tunda zahiri shi ma yana yi mana lefin kuma ha'kuri yake yi da ita.
Ina kallonsa ya shiga toilet dina ya yi uzurinsa ya fito d'aure da alwala ya zauna saman dadduma ya bude Al'kur'ani mai girma yana karantawa daga tsakiya suratul-kahfi sai da ya kammala ya rufe al'kur'anin bai nade daddumar ba ya kwanta a samanta tare da takurewa kamar wani maraya.
Na tashi zaune ina duban bayansa da mamakin abinda ya yi akan ya yi wa Hauwa magana ko ya kwana d'aki daya da ita gwara ya kwanta a kasa bisa dadduma wace irin zuciya ce wannan ta riko da gaba mai tsanani.
Ina ta yi masa magana ya yi mini shiru kuma idonsa biyu tunda ina ganin haske wayarsa yana dubawa.
Na sauko daga gadon hijabina na sanya na bude d'akin na fita dole na kar'bo maganin na shafa masa tunda na lura shi akan hakan sai dai duk abinda zai faru ya faru ga lafiyarsa amma ba zai kwanar mini a d'aki ba balle ta fahimci haka ta ji haushi ko ta zarge ni.
Na bubbuga kofar d'akin nata ta zo ta bude mini ta yi sabon wanka cikin kayan bacci tana kamshi na ce." Maganin nan za ki ba ni."
Sai ta yi kasa'ke tana kallona cikin nazari na yi kasa da kaina ina jinta tana fad'in." Yanzu nan fa na gama shiri zuwa saman ya dawo ne?''
A tak'aice na ce." E, shine ya ce a bashi." Ta juya jikinta a sanyaye ta d'auko mini na kar'ba na ja mata kofar.
A zaune na same shi yana waya ya gama ya koma ya kwanta bai dube ni ba.
Na daura tare da furta." Ga maganin na kar'bo."
Ya yi mini shiru bai ce komai ba.
Shiru d'akin ya d'auka kusan minti goma sha biyar ba shi da niyyar tashi ya d'auki maganinsa ya fita.
Na ce." Ni fa wallahi ba zan yadda da wannan rayuwar ba.
Ba zan ta'ba amincewa na zalinci wata ba mu yi maganar gaskiya a tsakaninmu kada ka so zuciyarka akan duk abubuwa da suka faru Hauwa matarka ce kuma 'yar uwarka ni kuma na dauketa abokiyar zamana tunda ka ce na kar'bo maka maganinka gashi ka tashi ka tafi wajenka ta sameka a can shi yafi alheri."
Uffan bai ce mini ba sai ya mika hannu ma ya d'auko fillo daya daga cikin wad'anda suke jere a saman gadona ya gyara kwanciyarsa.
raina ya b'aci sosai na kwanta jikina a sanyaye ina kallon bayansa da tarin mamakin abinda yake yi.
Ni dai anan ban ga lefin da na yi ba kuma da zai tsiri jin haushina.
Damuwa ta cunkushe mini da fargaba domin yadda ya yi zuciya da kallon inda nake haka yake so ya yi wa lafiyarsa mugunta.
Kaina ya fara sarawa tsabar takaici na rintse idona domin kirkiro bacci amma nasan ba zai ta'ba zuwa ba.
Can na fara jin saukar numfashinsa alamar bacci ya d'auke shi.
Na tashi zaune da sauri da mamaki da gaske yake yi
Na zuro 'kafata kasa ina le'ka fuskarsa bacci yake sosai kuma cikin kwanciyar hankali.
Na tashi na je na d'auko kayan maganin na zauna kusa da shi tare da d'an bubbuga fillon da yake kwance ya bud'e Ido yana kallona da yanayin bacci.
Na ce." Ka tashi na shafa maka."
Ya tashi kamar yadda na umarce shi da kansa ya cire kayan jikinsa.
Ban ce komai ba na fara shafa masa yana ta bina da kallo har na gama bai yi magana ba ya mayar da rigarsa da wandonsa na ciki ya koma ya kwanta.
A haka muka kwana a d'akin kai da gindi.
Sai da asuba ya fita bai kuma kula ni ba.
Na kasance cikin mamaki sosai shikkenan daga gyara kayanka Allah Ya sawwa'ke.
A haka kwana biyun da Hauwa ya kamata ta yi da shi suka shud'e a banza ba ma ya yarda ya kwanta a dakinsa balle ta biyo shi sai ya taho nawa ya kwanta kuma ba zai mini magana sai dai idan na gaji na yi masa idan na zo na shafa masa maganin sannan yake amsa mini amma bai ri'ke mini hannu ba balle ya ce zai nemi wani abu.
ranar da na kar'bi girki da yamma na shiga kicin domin hada masa fruit-salad kamar yadda ya buk'ata.
Baba Tabawa da Taburni suna ta hidimar abinda za a ci daddare.
Muka gaisa kafin na ji maganar Baba tana fad'in.
" Ban da abinki Taburni ai ba ita ta d'auke ki aiki ba to me zai sanya ki damu da abinda ta ce don Allah ki yi hakuri me yasa za a yi ta maimaita magana d'aya."
Na ce." Menene kuma?''
Murmushi ta yi tana fad'in." Ita da Hajiya Hauwa da alama jininsu bai hadu ba tun bayan dawowarta kafin ku dawo ke da maigidan su ka d'an yi sa'insa abin dai babu arziki da b'angaran Hajiya Hauwa kamar yadda ki ka san halinta na cin mutunci wallahi har da zagi wai zamansu ba shi da amfani mun had'u har da ni munafurcin banza. daga lokacin ko Taburni ta gaisheta ba ta amsaw.........." To me zai sanya ni amsawa Tabawa"
Muryar Hauwa ta katse maganar Baba Tabawa gabad'aya muka juya muna kallonta.
Ni mamaki ne ma ya kama ni yadda yau ta kira Tabawa kai tsaye babu ma Baba dukkaninsu dattijai ne cikinsu babu wadda ba ta haife mu ba ai rashi ba hauka ba ne don suna masu aiki sai su zama wulakantattu."
Ta shigo kicin din sosai tana fad'in." Baba Tabawa tunda Amina ta dawo ki 'kara kuzarin gulma da munafurci yanzu don Allah ba ki ji nauyi da kunya ba da girmanki da shekarunki?
saboda ni ba ni da kudi ba na baki toshiyar hanci shiyasa ba ki d'auke ni a matsayin matar gida ba.
Matsiyaciyar matar can wadda ta yi mutuwar wulakanci tun tana raye kike maula da yi mata fadanci kada ki ce na manta duk abinda zai faru ba ki ta'ba goyon bayana ba Amina da Maryam sune mutane tunda suna sinna miki.
To a shirye na dawo na gaya miki kowane sakarai da sha'kiyyi zan daidaita masa zama wallahi na kuma fad'a Mairo da Taburni sai kun bar gidan nan domin duk wani abu da ya danganci matsafiyar matar can najasa ne ba za ku hana mala'ikun rahama shigo mana gida ba."
Baba Tabawa duk yadda ta kai ga daurewa sai da ta fashe da kuka ta sanya tafin hannunta ta 'kunshe bakinta hawaye share-share a kumatunta.
Tunda na d'auki baiwar Allah nan aiki tsayin shekaru kusan biyar tsakanina da ita alheri ne da kyautatawa da wasa da dariya amma yau Hauwa ta dubi tsabar idonta tana kiranta da munafukai shakiyya sakarai.
Taburni ta jingina a jikin wardrobe din kicin din tare da sunkuyar da kanta.
Bakincikin da nake ciki ya sake hauhawa ai na d'auka ta yi sanyi ta dawo ne domin ta gyara kuskuran da ta yi mu zauna lafiya ashe ba haka ba ne a zuciyarta da wani shirin ta zo.
Na dube ta sosai ina fad'in." A matsayinki na wa za ki sanya su barin gidan ko ke ce ki ka d'auke su aiki ki ke biyansu?"
Ta gyad'a kanta tana cewa." A matsayina na matar gida kamar yadda ki ke matar gida ko da bambanci ne a tsakaninmu."
Na ce." Da bambanci kwarai da gaske Hauwa Ina so na gaya miki ki gyara kalamanki akan wad'an nan dattijan Annabi Muhammadu s.a.w ya ce ka girmama furfura ko ta wacece ke yanzu don Allah ba ki ji kunyar duban tsabar idon Baba Tabawa kin gaya mata wannan maganganun ba."
Ta ta'be baki tana fad'in." Ita ba ta ji kunyar abinda take yi ba ai munafukar tsohuwa ce."
Na buga mata tsawa sosai ina fad'in." Wallahi tallahi Hauwa za mu yi ta dake gidan nan akan wad'an nan da suke tsaye na gaya miki."
Ta girgiza kanta tana fad'in.'' Na ji duka to Amina na ce ki rufe ni da duka."
Na ja tsaki kawai ban sake wata magana ba na juya bangaransu ina ba su ha'kuri zuwa lokacin itama Taburni kukan take yi tana fad'in." Shiyasa na ce fa tafiya zan yi cikin iyalina na yi abinda na yi Hajiya Amina ba na so a kaskantani ki yi hakuri ni ba ki yi mini komai ba amma don girman Allah ki sanya a mayar da ni k'auyenmu.
Na ji 'kwalla ta ciko kwarmin idona na dubi Baba Tabawa da take goye da Sultan a bayanta yana ta bacci idonta duk ya kumbura tsabar kukan da ta jima ba ta yi irinsa ba.