Sashe 96
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A cikin gida kuwa bayan Aminu ya bi Mama cikin daki yake ce mata
"Haba Mama ya zaki fadi haka bayan kinsan halin Umaimah sarai duk abinda aka hanata shi tafi bada muhimmaci akai tayi, dan Allah ki janye maganarki, kin saka mata Albarka ma ya Allah ya cika ballantana kin fadi akasin haka akanta?"
"Aminu duk iskancin da Umaimah takeyi saboda tasan babu abinda za'a mata ne illah fada wanda baji takeyi ba, ai ba mahaukaciya bace ita taje tayi duk yanda taga shine daidai a gurinta nidai na gama magana ta" tana gama fada masa haka ta shige daki ta barshi.
Abba ma dai da Aminu yaje ya gaya masa yayi mata magana abi daya ta maimaita masa akan ba zata janye ba, kuma ta qara da in har ta cire cikin babu ita babu ita ta nemi wata uwar daban tunda bata isa ta gaya mata taji ba.
A bangaren Umaimah da Khalil dai ranar kwana tayi tana masa kuka shi kuma yana aikin bata haquri dan abin yazo da sauqin da beyi tsammani ba amma fafur taqi bawa Mu'ayyad Nono a daren seda safe daya dameta da kanta kuma ta jashi ta bashi bayan ta gama kuma ta fasa Kukan yanzu idan wani abu ya same shi fa ance idan yaro yasha ciki lalacewa yakeyi, dole ya kwasheta suka koma Asibiti, Likita ya tabbatar mata da babu komai taci gaba da shayar da shi har zuwa sanda taga zata Yaye shi, sannan ya rubuta mata magunguna da zata sha su qara taimaka mata, haka suka dawo gida a zuciyarta idan taji kamar tayi masa maganar cikin se ta tuna da kalaman Mama ta fasa sedai taci kuka ta godewa Allah yanzu kwanika zatayi? Tana zagin masu ciki da goyo ta ringa cewa sun fiya haihuwa kamar Awaki gashi yanzu itama ta zama Akuyar.
Dole ya dakko mata Habiba ta dawo gidan da zama dan wannan karon cikin nata me zafin laulayine, kusan kullum cikin jinya take ga quncindata sakawa zuciyarta dan har sannan ba wai ta gama aminta da tana son cikin bane shi yasa duk tabi ta lalace ta fita hayyacinta.
Khalil ya samu saqon Khausar da take zarginsa da yi mata zagon qasa ya kwace mata waya, ta sanar masa da cewar yaci nasara akanta wannan lokacin amma ya jirayi abinda ze biyo baya dan bazata saki ba kuma ya aika mata da layukanta.
Murmushi kawai yayi sanda yaga saqon ya saka lambar data turo a blacklist, ba ita ba Hadizar kanta yayi blocking number ta dan bayan faruwar wancan abin ta sake neman dawowa rayuwarsa tana kiransa da magiyar ya duba ya sama mata gurbi a rayuwarsa shi kuwa yanzu baya buqatar wata damuwa, shirye shiryen tafiyar da zasuyi ce a gabansa ga yanayin jikin Umaimah da yau lafiya gobe Asibiti duk hankalinsa akanta yake ga aikin ginin daya tattago dan tuni an Baje gidansu gaba daya Hajiya ta koma dakunan da yake ciki shida Khalifa a da an faro aikin ginin daga bangarenta dan so yakeyi idan Allah ya nufa a cikin shekara daya ya kammala ginin harda nasu bangaren su koma can.
A cikin wata biyu da suka biyo baya shirin tafiyarsu SouthAfrica ya tashi dan da maganar ta kwanta lokaci daya Babban Manager su ya kirashi akan ya fara shiri nan da sati daya zasu tafi, Kwangila ce suka samu daman kuma se ta nemi ta lalace saboda Manyan companies da suka fi nasu sun nemi su karbe da Allah kuma ya nufa ta tabbata tasu. Kwangila ce babba da suke saka ran jan manyan kudade idan ta kammala.
Tafiyarsu da Umaimah bazata yuwu ba saboda yanayin jikinta da yaqi dadi dole ya yanke shawarar ta koma gida kawai dan hakan zefi samun nutsuwa idan yaso zeyi qoqarin yaga yana samun damar zuwa duba su dan a qalla aikin da zasu je ze dauke su kusan wata shida ko sama da haka, duk idan ya gama da bangarensa na zane zane ze iya dawowa, amma dole yana da buqatar tsayawa dan tabbatar da duk abinda ya zana haka aka aiwatar dashi.
Yana ta shirin tafiya gaba daya yana cikin damuwar yanda ze tafi yayi watanni ba tareda iyalinsa ba sedai sam bega wata damuwa a tattare da Unaimah ba dan ita murnar komawa gida ma takeyi dan tuntuni taso Mama ta hana, shiyasa ma ta yaye Mu'ayyad, idan ya tafi Habiba zata wuce dashi gidan Hajiya ita kuma ta koma gidansu.
"Nikam naga murna kikeyi zan tafi na barku me yasa Umaimah" Khalil ya fada yana kallonta, Umaimah ta muskuta daga kwancen da take, cikin ta ya fito dan yana cikin wata na shida ne ta kalle shi tace
"Haba dai wani irin murna kuma"
"Eh mana, jifa ko a jikinki sabgogonki kawai kikeyi ni kuwa duk na damu i can't imaging me living for 3 months without you" ya sake fada yana janyo ta jikinsa seta narke masa tana cewa
"Daurewa kawai nakeyi nima amma nasan zanyi missing naka sosai"
"Toh mu tafi tare kawai, kinga kin Yayae Mu'ayyad zasu tafi gurin Hajiya muyi tafiyarmu kawai hankalina zefi kwanciya" ya fada yana kissing wuyanta ta noqe tana cewa
"Nidai Aa, kana kallon dai kullum bani da lafiya tunda na samu cikin nan"
"Kiyi addu'a Allah ya raba ki dashi lafiya bana son irin maganganun da kikeyi bana jin dadi idan kina cewa bakya son cikina kamar bakya so nane".
Baki ta tunzura gaba tace
"Kaima dan baka san wahalar da ake sha bane shiyasa"
"Shikenan tunda bakya so daga wannan kin gama ni kuma se na nemo wadda zatayi ta haifamun wasu yaran ba tareda tayi qorafi ba dan ni ina so na tara yara da yawa" Khalil ya fada yana saka kansa a wuyanta da qarfi ta ture shi ta tashi zaune tana harararsa, dariya abin ya bashi har ya kasa riqeta ai kuwa ta fasa masa kuka ta hau dukansa ganin abin nata da gaske ne ya saka ya riqeta yana rada mata magana a kunne daga nan labari ya canza.
Da yamma suka fita sukayi shopping sosai na kayayyakin buqatarta da wanda Mu'ayyad ze tafi dasu gidan hajiya, bayan sun gama suka biya gidan Maman Asad, Dambun Nama, kilishi, soyayyar Miya, yaji ja dana daddawa ga cake da cincin haka ta hada mata anyi packaging nasu tsaf yanda bazeyi masa wahalar dauka ba. Ita tayiwa Umaiman maganar ya kamata tayi masa dan a lissafinta ko gishiri batayi tunanin ya kamata ya tafi dashi ba suka karbo kayan a daren ya kai Habiba da Mu'ayyad gidan Hajiya kuma yayi mata sallama dan washe gari zasu tafi qarfe biyu na rana.
A daren ta tayashi ya hada kayansa tsaf itama ta hada nata. sunyi kwanan farinciki da soyayya me tsayawa a rai washe gari qarfe goma suka kulle gidan. Khalifa ne yazo ya dauke su, seda ya fara sauketa a gida yayiwa su Mama sallama kafin suka fito ta rako shi seda taga tabbacin tafiyar ze yi sannan zuciyarta ta karaya ta saka masa Kuka, Khalil da daman dauriya kawai yakeyi amma shi yasan ze azabtu ba kadan ba a wannan tafiyar ya rungumeta a jikinsa yana rarrashi ji yake kamar shima yayi kukan ko zeji sanyi a ransa.
Seda yayi dagaske tareda yi mata qaryar bayan wata daya ze dawo sannan ya samu ta haqura ya lallabata ya tafi dan Abokanan tafiyarsa suna ta yi masa waya.
"Kamar gaske, wanda be san halinki ba Umaimah kin sha dashi" Yaya Nuratu da suka tarar a gidan ta fada, Umaimah ta balla mata harara bata kulata bata shige cikin daki ta kwanta kewar Mijinta na damunta.
Bayan wata daya
Umaimah na kwance a qasan Dakin Anty duk maganar da taketa faman yi mata akan kwanciyar qasan taqi tashi, tace mata sanyi ze kamata tace ai sanyin take bi daman har ta gaji da magana ta qyaleta. Wayarta ce a hannunta tana dannanwa, basu dade da gama magana da Khalil ba dukda daman kusan kullum cikin waya suke, daya samu sarari z kirata Audio call ko Video call wani yammatanci sukeji haka zasuyi musayar kalaman soyayya masu tsuma zuciya a cewarsa ji yake yi kamar yayi tsuntsuwa ya dawo gida amma babu dama.
Saqo a turo mata ta WhatsApp da wata sabuwar number, bata fiya amsa baqin lamba ba tun abinda ya faru tsakaninta da Maman Nihal wanda se daga baya ta samu cikakken bayani ashe ita din Asalinta yar me aikin gidansu Maman Nihal ta gaskiya ce. Sun tashi sa'anni dan haka suke shiri kuma itama tana matsayin me aikin Maman Nihal din ce a haka tayi aure ta tafi tareda Abun saboda sun shaqu, takai ta kawo ko fita qasar waje zatayi har bayan Abu tayi aure idan tana buqatar me kular mata da yara zata kirata haka kuma batayi mata iyaka da komai nata shine har ya bata damar yin basaja da sunanta a gari tana janyo rigima.
Fita tayi daga WhatsApp din ba tareda ta bude saqon ba ta tashi dakyar saboda fitsarin da taji ya dameta. Bayan tayi ta dawo ta dauki wayarta data tarar da Missed call biyu akai still number babu suna amma ta kira data tuna akwai wanda Rufaida tace zata hada ta dashi me siyar da kayan Jarirai ko shine ya tura mata da hotuna ta gani.
Sallama tayi daga daya bangaren wata mace ta amsa sukayi shiru gaba dayansu kafin cikin jin haushi Umaimah tace
"Naga Missed calls na kira kuma anyi shiru wacece?"
"Yi haquri baiwar Allah, na tura miki da saqo ne ta WhatsApp naga baki bude ba shi yasa na kiraki, amma kije ki bude idan kinga abinda yake ciki seki kirani muyi magana" matar ta bata amsa daga dayan bagaren kafin ta samu damar magana ta kashe wayar.
Shiru tayi tana nazari, sam muryarta batayi mata kama data wanda ta sani ba amma haka nan zuciyarta ta kwadaitu dason ganin saqon menene da har zata kirata suyi magana bayan ta gani. Zeta koma kan Kujera ta zauna dakyau ta shiga WhatsApp din babu bata lokaci ta bude chat din nata hotunan sun rigada sun bude saboda wayar a auto download daman take.
"Haba Mama ya zaki fadi haka bayan kinsan halin Umaimah sarai duk abinda aka hanata shi tafi bada muhimmaci akai tayi, dan Allah ki janye maganarki, kin saka mata Albarka ma ya Allah ya cika ballantana kin fadi akasin haka akanta?"
"Aminu duk iskancin da Umaimah takeyi saboda tasan babu abinda za'a mata ne illah fada wanda baji takeyi ba, ai ba mahaukaciya bace ita taje tayi duk yanda taga shine daidai a gurinta nidai na gama magana ta" tana gama fada masa haka ta shige daki ta barshi.
Abba ma dai da Aminu yaje ya gaya masa yayi mata magana abi daya ta maimaita masa akan ba zata janye ba, kuma ta qara da in har ta cire cikin babu ita babu ita ta nemi wata uwar daban tunda bata isa ta gaya mata taji ba.
A bangaren Umaimah da Khalil dai ranar kwana tayi tana masa kuka shi kuma yana aikin bata haquri dan abin yazo da sauqin da beyi tsammani ba amma fafur taqi bawa Mu'ayyad Nono a daren seda safe daya dameta da kanta kuma ta jashi ta bashi bayan ta gama kuma ta fasa Kukan yanzu idan wani abu ya same shi fa ance idan yaro yasha ciki lalacewa yakeyi, dole ya kwasheta suka koma Asibiti, Likita ya tabbatar mata da babu komai taci gaba da shayar da shi har zuwa sanda taga zata Yaye shi, sannan ya rubuta mata magunguna da zata sha su qara taimaka mata, haka suka dawo gida a zuciyarta idan taji kamar tayi masa maganar cikin se ta tuna da kalaman Mama ta fasa sedai taci kuka ta godewa Allah yanzu kwanika zatayi? Tana zagin masu ciki da goyo ta ringa cewa sun fiya haihuwa kamar Awaki gashi yanzu itama ta zama Akuyar.
Dole ya dakko mata Habiba ta dawo gidan da zama dan wannan karon cikin nata me zafin laulayine, kusan kullum cikin jinya take ga quncindata sakawa zuciyarta dan har sannan ba wai ta gama aminta da tana son cikin bane shi yasa duk tabi ta lalace ta fita hayyacinta.
Khalil ya samu saqon Khausar da take zarginsa da yi mata zagon qasa ya kwace mata waya, ta sanar masa da cewar yaci nasara akanta wannan lokacin amma ya jirayi abinda ze biyo baya dan bazata saki ba kuma ya aika mata da layukanta.
Murmushi kawai yayi sanda yaga saqon ya saka lambar data turo a blacklist, ba ita ba Hadizar kanta yayi blocking number ta dan bayan faruwar wancan abin ta sake neman dawowa rayuwarsa tana kiransa da magiyar ya duba ya sama mata gurbi a rayuwarsa shi kuwa yanzu baya buqatar wata damuwa, shirye shiryen tafiyar da zasuyi ce a gabansa ga yanayin jikin Umaimah da yau lafiya gobe Asibiti duk hankalinsa akanta yake ga aikin ginin daya tattago dan tuni an Baje gidansu gaba daya Hajiya ta koma dakunan da yake ciki shida Khalifa a da an faro aikin ginin daga bangarenta dan so yakeyi idan Allah ya nufa a cikin shekara daya ya kammala ginin harda nasu bangaren su koma can.
A cikin wata biyu da suka biyo baya shirin tafiyarsu SouthAfrica ya tashi dan da maganar ta kwanta lokaci daya Babban Manager su ya kirashi akan ya fara shiri nan da sati daya zasu tafi, Kwangila ce suka samu daman kuma se ta nemi ta lalace saboda Manyan companies da suka fi nasu sun nemi su karbe da Allah kuma ya nufa ta tabbata tasu. Kwangila ce babba da suke saka ran jan manyan kudade idan ta kammala.
Tafiyarsu da Umaimah bazata yuwu ba saboda yanayin jikinta da yaqi dadi dole ya yanke shawarar ta koma gida kawai dan hakan zefi samun nutsuwa idan yaso zeyi qoqarin yaga yana samun damar zuwa duba su dan a qalla aikin da zasu je ze dauke su kusan wata shida ko sama da haka, duk idan ya gama da bangarensa na zane zane ze iya dawowa, amma dole yana da buqatar tsayawa dan tabbatar da duk abinda ya zana haka aka aiwatar dashi.
Yana ta shirin tafiya gaba daya yana cikin damuwar yanda ze tafi yayi watanni ba tareda iyalinsa ba sedai sam bega wata damuwa a tattare da Unaimah ba dan ita murnar komawa gida ma takeyi dan tuntuni taso Mama ta hana, shiyasa ma ta yaye Mu'ayyad, idan ya tafi Habiba zata wuce dashi gidan Hajiya ita kuma ta koma gidansu.
"Nikam naga murna kikeyi zan tafi na barku me yasa Umaimah" Khalil ya fada yana kallonta, Umaimah ta muskuta daga kwancen da take, cikin ta ya fito dan yana cikin wata na shida ne ta kalle shi tace
"Haba dai wani irin murna kuma"
"Eh mana, jifa ko a jikinki sabgogonki kawai kikeyi ni kuwa duk na damu i can't imaging me living for 3 months without you" ya sake fada yana janyo ta jikinsa seta narke masa tana cewa
"Daurewa kawai nakeyi nima amma nasan zanyi missing naka sosai"
"Toh mu tafi tare kawai, kinga kin Yayae Mu'ayyad zasu tafi gurin Hajiya muyi tafiyarmu kawai hankalina zefi kwanciya" ya fada yana kissing wuyanta ta noqe tana cewa
"Nidai Aa, kana kallon dai kullum bani da lafiya tunda na samu cikin nan"
"Kiyi addu'a Allah ya raba ki dashi lafiya bana son irin maganganun da kikeyi bana jin dadi idan kina cewa bakya son cikina kamar bakya so nane".
Baki ta tunzura gaba tace
"Kaima dan baka san wahalar da ake sha bane shiyasa"
"Shikenan tunda bakya so daga wannan kin gama ni kuma se na nemo wadda zatayi ta haifamun wasu yaran ba tareda tayi qorafi ba dan ni ina so na tara yara da yawa" Khalil ya fada yana saka kansa a wuyanta da qarfi ta ture shi ta tashi zaune tana harararsa, dariya abin ya bashi har ya kasa riqeta ai kuwa ta fasa masa kuka ta hau dukansa ganin abin nata da gaske ne ya saka ya riqeta yana rada mata magana a kunne daga nan labari ya canza.
Da yamma suka fita sukayi shopping sosai na kayayyakin buqatarta da wanda Mu'ayyad ze tafi dasu gidan hajiya, bayan sun gama suka biya gidan Maman Asad, Dambun Nama, kilishi, soyayyar Miya, yaji ja dana daddawa ga cake da cincin haka ta hada mata anyi packaging nasu tsaf yanda bazeyi masa wahalar dauka ba. Ita tayiwa Umaiman maganar ya kamata tayi masa dan a lissafinta ko gishiri batayi tunanin ya kamata ya tafi dashi ba suka karbo kayan a daren ya kai Habiba da Mu'ayyad gidan Hajiya kuma yayi mata sallama dan washe gari zasu tafi qarfe biyu na rana.
A daren ta tayashi ya hada kayansa tsaf itama ta hada nata. sunyi kwanan farinciki da soyayya me tsayawa a rai washe gari qarfe goma suka kulle gidan. Khalifa ne yazo ya dauke su, seda ya fara sauketa a gida yayiwa su Mama sallama kafin suka fito ta rako shi seda taga tabbacin tafiyar ze yi sannan zuciyarta ta karaya ta saka masa Kuka, Khalil da daman dauriya kawai yakeyi amma shi yasan ze azabtu ba kadan ba a wannan tafiyar ya rungumeta a jikinsa yana rarrashi ji yake kamar shima yayi kukan ko zeji sanyi a ransa.
Seda yayi dagaske tareda yi mata qaryar bayan wata daya ze dawo sannan ya samu ta haqura ya lallabata ya tafi dan Abokanan tafiyarsa suna ta yi masa waya.
"Kamar gaske, wanda be san halinki ba Umaimah kin sha dashi" Yaya Nuratu da suka tarar a gidan ta fada, Umaimah ta balla mata harara bata kulata bata shige cikin daki ta kwanta kewar Mijinta na damunta.
Bayan wata daya
Umaimah na kwance a qasan Dakin Anty duk maganar da taketa faman yi mata akan kwanciyar qasan taqi tashi, tace mata sanyi ze kamata tace ai sanyin take bi daman har ta gaji da magana ta qyaleta. Wayarta ce a hannunta tana dannanwa, basu dade da gama magana da Khalil ba dukda daman kusan kullum cikin waya suke, daya samu sarari z kirata Audio call ko Video call wani yammatanci sukeji haka zasuyi musayar kalaman soyayya masu tsuma zuciya a cewarsa ji yake yi kamar yayi tsuntsuwa ya dawo gida amma babu dama.
Saqo a turo mata ta WhatsApp da wata sabuwar number, bata fiya amsa baqin lamba ba tun abinda ya faru tsakaninta da Maman Nihal wanda se daga baya ta samu cikakken bayani ashe ita din Asalinta yar me aikin gidansu Maman Nihal ta gaskiya ce. Sun tashi sa'anni dan haka suke shiri kuma itama tana matsayin me aikin Maman Nihal din ce a haka tayi aure ta tafi tareda Abun saboda sun shaqu, takai ta kawo ko fita qasar waje zatayi har bayan Abu tayi aure idan tana buqatar me kular mata da yara zata kirata haka kuma batayi mata iyaka da komai nata shine har ya bata damar yin basaja da sunanta a gari tana janyo rigima.
Fita tayi daga WhatsApp din ba tareda ta bude saqon ba ta tashi dakyar saboda fitsarin da taji ya dameta. Bayan tayi ta dawo ta dauki wayarta data tarar da Missed call biyu akai still number babu suna amma ta kira data tuna akwai wanda Rufaida tace zata hada ta dashi me siyar da kayan Jarirai ko shine ya tura mata da hotuna ta gani.
Sallama tayi daga daya bangaren wata mace ta amsa sukayi shiru gaba dayansu kafin cikin jin haushi Umaimah tace
"Naga Missed calls na kira kuma anyi shiru wacece?"
"Yi haquri baiwar Allah, na tura miki da saqo ne ta WhatsApp naga baki bude ba shi yasa na kiraki, amma kije ki bude idan kinga abinda yake ciki seki kirani muyi magana" matar ta bata amsa daga dayan bagaren kafin ta samu damar magana ta kashe wayar.
Shiru tayi tana nazari, sam muryarta batayi mata kama data wanda ta sani ba amma haka nan zuciyarta ta kwadaitu dason ganin saqon menene da har zata kirata suyi magana bayan ta gani. Zeta koma kan Kujera ta zauna dakyau ta shiga WhatsApp din babu bata lokaci ta bude chat din nata hotunan sun rigada sun bude saboda wayar a auto download daman take.