Sashe 195
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Anty Laure ta kawo mata ruwa da Lemo ta zauna tana cewa
"Bari na soya miki Kwai akwai ragowar Dankali yanzu muka gama karyawa amma Yaya irin wannan zuwa da safe babu sanarwa lafiya dai ko?"
"Ba lafiya na Laure, yanzu dai tashi ki cire wadan nan abun dan Allah ki saka suturar arziqi rakani gidan Umaimah zakiyi"
"Kin san dazu nake zancen yar banzar yarinyar nan a raina rabona da ita tun ranar daurin aure kowa yazo yaga gida ya mun murna banda ita halan ta haihu wannan ciki dai ko na Aljanu ne ya isa a haifeshi haka dai" Anty Laure ta fada se Mama ta miqe tana cewa
"Laure ki tashi idan kuma ba zaki samu zuwa ba in tafi ni kadai"
"Wai Yaya lafiya kuwa?" Anty Lauren ta sake fada ganin Maman na shirin tafiya ta wuce daki tana cewa
"Yi haquri bari na shirya, da dai Yallabai yace bacci zamu koma amma wata kusan ai tafi wata".
Tsaki Mama taja abin takaicin Laure yawa ne dashi, wani abu take yanda kasan ba ta taba aure ba ita idan ta kallesu daga ita har Mijin nata ma haushi suke bata. A motar Mijin Anty Laure suka fita, a taqaice Mama tayi mata bayani a hanya Anty Laure data kusan sakin sitiyari ta gangara gefen Titi tana salati tace
"Yaya kice Khalil ya taro mana yaqin duniya na uku ni Lauratu naga abinda ya isheni wannan wace kalar jaraba Khalil ya janyo mana yaje yayi aure bata sani ba dan ubansa a ina aka taba haka? Nidai wlh da kin gaya mun tun a gida daman bazab biyo ki ba, nifa nasan Tijarar Umaimah sarai kawai dan Yata ce yasa nake take gaskiya nake bin bayanta amma mara mutunchi ta qarshe yarinyar nan toh Allah kaga zuciyata dan zumunchi zan rakaki Allah kasa na fito da raina da lafiyata kar tayiwa Angona Asarar wani abun a jikina".
Tsabar baqin ciki har sukaje gidan Mama bata sake ce mata komai ba. A waje ta ajiye motar a cewarta kar wani tsautsayi ya afkaqa motar Mijinta ta shiga uku.
Bangaren Hajiya suka fara shiga sun tarar da falon cike da yan uwan Hajiyar da yayayensu ga Akwatuna saiti uku masu hurhudu a bude kaya maqil a ciki iya kallonka da alama su suke dubawa.
A mutunce suka gaisa da jama'ar falon wasu sun santa irinsu Jalilah wasu kuma kamanninta da Umaimah yasa suka fahimci ko wacece, Falon Sama Hajiya ta kaisu, seda ta saka Habiba da me aikinta suka cika musu gaba da kayan sha dana ciye ciye kafin ta zauna suka sake gaisawa. Maganar dai guda daya ce aka maimaita, Hajiya ta kalli Mama cikin Jimami tace
"Wlh Hajiya tun da abin nan ya faru na rasa sukuni nan kullum yake zuwa ya tasani gaba akan se ni in sameta na gaya mata na ce masa bazan iya ba akan me ni zan kwashi baqin jini shida aure nida fadar bakin saqo daman yaushe aka gama rikicin tasowar maganar ma se gashi daga zuwa tambaya kawai suka daura aure kayan can da kuka gani yan uwan ne suka hada wai yau zasu kai Lefen saboda Qanin Babansu yayi rantsuwa se Yarinyar ta tare a cikin satin nan tun jiya abin duniya ya isheni Hajiya ko baccin kirki na gagarayi saboda tsakani da Allah na sani bamu kyautawa yarinyar nan ba, kuma da ace na san zasu tada maganar tariyar da wuri da tun sanda aka daura auran nan za'a gaya mata, amma gaba daya lissafinmu wata uku ne nan gaba saboda gurin da ze ajiyeta ma be kammala ba yanzu Kawun nasu yace sedai su zauna nan gaba daya idanma daga baya ze canza mata gida yayi haka amma yanzu ya rigada ya sanarwa da Iyayenta a satin nan zata tare".
Numfashi Mama taja tace
"Babu komai Hajiya haka Allah ya tsara kuma in sha Allah hakan ze zamo musu Alkhairi baki daya Mahaifinta ma dayaji fada ya ringayi akan me yasa Amaryar bata tare ba har yanzun ai tunda an rigada an daura aure duk kuma wani abu daga bayane, zan sameta yanzu zan kuma yi mata bayani ta yanda zata fahimta in Allah ya yarda ba za'a samu ko wacce matsala ba zata karbi al'amarin da sauqi nasan Umaimah nada rigima amma idan aka tafida ita ta yanda ya kamata da izinin ubangiji komai zezo da sauqi"
"Toh Allah ya yarda Hajiya Allah ya yarda" Hajiya ta fada tana gyada kai Anty Laure dai daman bata ce musu komai ba saboda wani mugun haushi daya turnuqeta, gani tayi abin nasu ma rainin wayo ne ita yanzu bata ma yarda da cewar wani babu shiri aka daura auran ba da ma sun shiryi abinsu idan ba haka ba duk a cikin sati dayan ne suka hada wannan uban lefen sannan yanda suke raha suna jin dadinsu kana gani kasan daman abin shiryayye ne kawai so suke su raina musu hankali to abiyar kowa ta bishi kuma idan anyi dan a wulaqanta yar Yar uwarta ne mugun nufinsu ya koma musu kuma dukkansu Mata ne suma kuma sun haifa in har sunyi dan su Musguna mata Allah yasa su gani a kwaryarsu.
Tsaki taja a fili Hajiya da Mama suka kalleta seta miqe tana kallon Mama tace
"Ki tashi muje Yaya, aure dai sunrigada sun masa duk wani jaje da za'a zauna anayi da taraddadin meze faru daga bayane, in har zuciya da gaske an ga rashin kyautawar abinda akayi me yasa tun gabanin ya afku ba'a dauki mataki ba? Kawai anyi abinda akayi bisa son rai kuma in Allah ya yarda tozartar da ake so tayi ba za'a ganta a kanta ba ehe".
Basu da buqatar ta fadi dawa take dan maganace tayi ta a fili tana kuma gama fada ta fice ta sauka qasan tana mita ko yayar tata bata tsaya jira ba, a falon qasan tana sauka taji wata zaqaqura tana cewa
"Ai ni live zanyi, bazan ma iya tsayawa wani recording sannan nayi posting daga baya ba tun yanzu ma nayi sanarwa qarfe hudu zanyi Live kowa ya shirya kallon Tambelen Kishi dan wlh yau se an fasa kwan nan a tsakar gida kowa yaji warin sa" suka kwashe da dariya. Da daddaya Anty Laure ta kalle au fuskar nan tata kirtif yanda kasanita akayiwa kishiyar ma ba Umaimah ba ta nuna Lubna da tayi maganar tace
"Ko banza akan Mijinta zatayi tambelen kishin ke kuwa banida buqatar a gaya mun a kwalta kike an rasa me, ku kuma da kuka zauna kuna tayata duk a gidajen aure kuke kuma yanda kishiyar batayi sallama da zata diro gidan taba haka kuma kowa ta jirayi tata tana tafe".
Qugu Lubna ta riqe zatayi mata fitsara Jamila ta riqe hannunta tana girgiza mata kai Anty Laure ta ce
"Da kin barta in nadawa yar iska duka inga abinda za'ayi aikin banza kawai" fuuu tayi waje ta buga musu qofa duk suka bita da kallo.
"Tab kice abin nasu Gado ne" wata daga ciki ta fada daidai nan Hajiya da Mama suka sakko Hajiya dai bakinta ya kasa dena bada haquri, bugun da Anty Laure tayiwa qofar yasa ta cije taqi buduwa dan haka Hajiya tace suje ta qofar kitchen, seda Maman ta fita kafin ta sauke ajiyar zuciya ta koma ciki ta tarar dasu suna hayaniya akan abinda Anty Laure tayi ita dai sama ta wuce dan jininta ya rigada yayi sama tun ma kafin me afkuwar ta afku.
UMAIMAH
Qarfe tara na safe ta farka daga baccin data koma dalilin kiran da Safina tayi mata akan zatazo, seda tayi wanka ta shirya sannan ta fito Ruqayya dake goge kayan kallo ta kalleta da fara'a ta gaisheta ta amsa tana yamutsa fuska saboda yunwar da takeyi kai gaba daya ma bata jin dadi ita bata taba ji cikin jikinta ya dameta irin yau ba dan haka ma ta tashi da niyyar da dare zataje Asibiti ita ko Inducing ne su mata ta haihu amma banda CS tunda naqudar taqi tazo. Tuwonta taci da Koko da already Ruqayyan ta hada mata su, a bakinta taji cewar da wurwuri Khalil ya fita a falon ta zauna bayan ta cewa Ruqayya ta hada abin karyawa zatayi baquwa yanzu tana hanya.
Wuraren goma da yan mintina Safina ta isa gidan Afujajan da ita kamar wadda ta dawo daga qauye, Umaimah ta kalleta ganinta da qatuwar jaka tace
"Ke kuma daga ina haka ga wata qwanqwamemeiyar jaka kamar wadda zakiyi tafiya?"
Safina ta zauna tana sauke numfashi tace
"Daga gidan Malam nake fitar ce tazo mun babu shiri tun Asuba n fita kai mun jakar ciki toh saboda tsaro me kuka rage a gidan?"
"Kamar na sani nace a hada miki abinci bari ta kawo" Umaimah ta fada kafin ta shiga kiran Ruqayya.
A daki suka qule seda Safina taci tayi nak kafin ta fara fiddo da kayan cikin jakar tana kallon Umaimah tace
"In gaya miki jiya naga Suleiman namun wani gani gani na sakashi abu ya qiyi shine fa yau babu shiri na bazama ina zan zauna kallon ruwa kwado yayi mun qafa?
Kedai ai duniya ta samu hankalinki ya kwanta Khalil ya dawo hannunki se yanda kikayi dashi, to kema ga saqonki inji Malam wannan turaren ne kuma yace na jaddada miki ki kula dashi karki kuma nemansa ki rasa" Safina ta fada tana bata wani dan qullin baqar leda. Drawer gefen gadonta taja ta saka a ciki daga nan suka ci gaba dayi, Mu'ayyadya shiga dakin da Sallama yana tafiya a hankali, seda ya gaida Safina kafin ya qarasa jikin Umaimah ya jingina ta dagoshi jin jikinsa da zafi tace
"Zazzabin ne ya dawo?"
Kai ya daga mata kafin ta sake cewa
"Toh me yasa baka kwanta a gurin Hajiya ba ka fito?"
"Hayaniya akeyi Momy duk su Momyn Sharada ne sukazo harda su Maman Kaduna ma su da yawa" ya bata amsa yana kwanciya akan gadon. Mamaki ya kamata jin yace mutane a bangaren Hajiya, su Jalilah ba baqi bane daman kullum suna tafe amma Maman Kaduna Maman su Lubna kenan dayace sunzo da yawa su kuma me ya kawosu?
"Bari na soya miki Kwai akwai ragowar Dankali yanzu muka gama karyawa amma Yaya irin wannan zuwa da safe babu sanarwa lafiya dai ko?"
"Ba lafiya na Laure, yanzu dai tashi ki cire wadan nan abun dan Allah ki saka suturar arziqi rakani gidan Umaimah zakiyi"
"Kin san dazu nake zancen yar banzar yarinyar nan a raina rabona da ita tun ranar daurin aure kowa yazo yaga gida ya mun murna banda ita halan ta haihu wannan ciki dai ko na Aljanu ne ya isa a haifeshi haka dai" Anty Laure ta fada se Mama ta miqe tana cewa
"Laure ki tashi idan kuma ba zaki samu zuwa ba in tafi ni kadai"
"Wai Yaya lafiya kuwa?" Anty Lauren ta sake fada ganin Maman na shirin tafiya ta wuce daki tana cewa
"Yi haquri bari na shirya, da dai Yallabai yace bacci zamu koma amma wata kusan ai tafi wata".
Tsaki Mama taja abin takaicin Laure yawa ne dashi, wani abu take yanda kasan ba ta taba aure ba ita idan ta kallesu daga ita har Mijin nata ma haushi suke bata. A motar Mijin Anty Laure suka fita, a taqaice Mama tayi mata bayani a hanya Anty Laure data kusan sakin sitiyari ta gangara gefen Titi tana salati tace
"Yaya kice Khalil ya taro mana yaqin duniya na uku ni Lauratu naga abinda ya isheni wannan wace kalar jaraba Khalil ya janyo mana yaje yayi aure bata sani ba dan ubansa a ina aka taba haka? Nidai wlh da kin gaya mun tun a gida daman bazab biyo ki ba, nifa nasan Tijarar Umaimah sarai kawai dan Yata ce yasa nake take gaskiya nake bin bayanta amma mara mutunchi ta qarshe yarinyar nan toh Allah kaga zuciyata dan zumunchi zan rakaki Allah kasa na fito da raina da lafiyata kar tayiwa Angona Asarar wani abun a jikina".
Tsabar baqin ciki har sukaje gidan Mama bata sake ce mata komai ba. A waje ta ajiye motar a cewarta kar wani tsautsayi ya afkaqa motar Mijinta ta shiga uku.
Bangaren Hajiya suka fara shiga sun tarar da falon cike da yan uwan Hajiyar da yayayensu ga Akwatuna saiti uku masu hurhudu a bude kaya maqil a ciki iya kallonka da alama su suke dubawa.
A mutunce suka gaisa da jama'ar falon wasu sun santa irinsu Jalilah wasu kuma kamanninta da Umaimah yasa suka fahimci ko wacece, Falon Sama Hajiya ta kaisu, seda ta saka Habiba da me aikinta suka cika musu gaba da kayan sha dana ciye ciye kafin ta zauna suka sake gaisawa. Maganar dai guda daya ce aka maimaita, Hajiya ta kalli Mama cikin Jimami tace
"Wlh Hajiya tun da abin nan ya faru na rasa sukuni nan kullum yake zuwa ya tasani gaba akan se ni in sameta na gaya mata na ce masa bazan iya ba akan me ni zan kwashi baqin jini shida aure nida fadar bakin saqo daman yaushe aka gama rikicin tasowar maganar ma se gashi daga zuwa tambaya kawai suka daura aure kayan can da kuka gani yan uwan ne suka hada wai yau zasu kai Lefen saboda Qanin Babansu yayi rantsuwa se Yarinyar ta tare a cikin satin nan tun jiya abin duniya ya isheni Hajiya ko baccin kirki na gagarayi saboda tsakani da Allah na sani bamu kyautawa yarinyar nan ba, kuma da ace na san zasu tada maganar tariyar da wuri da tun sanda aka daura auran nan za'a gaya mata, amma gaba daya lissafinmu wata uku ne nan gaba saboda gurin da ze ajiyeta ma be kammala ba yanzu Kawun nasu yace sedai su zauna nan gaba daya idanma daga baya ze canza mata gida yayi haka amma yanzu ya rigada ya sanarwa da Iyayenta a satin nan zata tare".
Numfashi Mama taja tace
"Babu komai Hajiya haka Allah ya tsara kuma in sha Allah hakan ze zamo musu Alkhairi baki daya Mahaifinta ma dayaji fada ya ringayi akan me yasa Amaryar bata tare ba har yanzun ai tunda an rigada an daura aure duk kuma wani abu daga bayane, zan sameta yanzu zan kuma yi mata bayani ta yanda zata fahimta in Allah ya yarda ba za'a samu ko wacce matsala ba zata karbi al'amarin da sauqi nasan Umaimah nada rigima amma idan aka tafida ita ta yanda ya kamata da izinin ubangiji komai zezo da sauqi"
"Toh Allah ya yarda Hajiya Allah ya yarda" Hajiya ta fada tana gyada kai Anty Laure dai daman bata ce musu komai ba saboda wani mugun haushi daya turnuqeta, gani tayi abin nasu ma rainin wayo ne ita yanzu bata ma yarda da cewar wani babu shiri aka daura auran ba da ma sun shiryi abinsu idan ba haka ba duk a cikin sati dayan ne suka hada wannan uban lefen sannan yanda suke raha suna jin dadinsu kana gani kasan daman abin shiryayye ne kawai so suke su raina musu hankali to abiyar kowa ta bishi kuma idan anyi dan a wulaqanta yar Yar uwarta ne mugun nufinsu ya koma musu kuma dukkansu Mata ne suma kuma sun haifa in har sunyi dan su Musguna mata Allah yasa su gani a kwaryarsu.
Tsaki taja a fili Hajiya da Mama suka kalleta seta miqe tana kallon Mama tace
"Ki tashi muje Yaya, aure dai sunrigada sun masa duk wani jaje da za'a zauna anayi da taraddadin meze faru daga bayane, in har zuciya da gaske an ga rashin kyautawar abinda akayi me yasa tun gabanin ya afku ba'a dauki mataki ba? Kawai anyi abinda akayi bisa son rai kuma in Allah ya yarda tozartar da ake so tayi ba za'a ganta a kanta ba ehe".
Basu da buqatar ta fadi dawa take dan maganace tayi ta a fili tana kuma gama fada ta fice ta sauka qasan tana mita ko yayar tata bata tsaya jira ba, a falon qasan tana sauka taji wata zaqaqura tana cewa
"Ai ni live zanyi, bazan ma iya tsayawa wani recording sannan nayi posting daga baya ba tun yanzu ma nayi sanarwa qarfe hudu zanyi Live kowa ya shirya kallon Tambelen Kishi dan wlh yau se an fasa kwan nan a tsakar gida kowa yaji warin sa" suka kwashe da dariya. Da daddaya Anty Laure ta kalle au fuskar nan tata kirtif yanda kasanita akayiwa kishiyar ma ba Umaimah ba ta nuna Lubna da tayi maganar tace
"Ko banza akan Mijinta zatayi tambelen kishin ke kuwa banida buqatar a gaya mun a kwalta kike an rasa me, ku kuma da kuka zauna kuna tayata duk a gidajen aure kuke kuma yanda kishiyar batayi sallama da zata diro gidan taba haka kuma kowa ta jirayi tata tana tafe".
Qugu Lubna ta riqe zatayi mata fitsara Jamila ta riqe hannunta tana girgiza mata kai Anty Laure ta ce
"Da kin barta in nadawa yar iska duka inga abinda za'ayi aikin banza kawai" fuuu tayi waje ta buga musu qofa duk suka bita da kallo.
"Tab kice abin nasu Gado ne" wata daga ciki ta fada daidai nan Hajiya da Mama suka sakko Hajiya dai bakinta ya kasa dena bada haquri, bugun da Anty Laure tayiwa qofar yasa ta cije taqi buduwa dan haka Hajiya tace suje ta qofar kitchen, seda Maman ta fita kafin ta sauke ajiyar zuciya ta koma ciki ta tarar dasu suna hayaniya akan abinda Anty Laure tayi ita dai sama ta wuce dan jininta ya rigada yayi sama tun ma kafin me afkuwar ta afku.
UMAIMAH
Qarfe tara na safe ta farka daga baccin data koma dalilin kiran da Safina tayi mata akan zatazo, seda tayi wanka ta shirya sannan ta fito Ruqayya dake goge kayan kallo ta kalleta da fara'a ta gaisheta ta amsa tana yamutsa fuska saboda yunwar da takeyi kai gaba daya ma bata jin dadi ita bata taba ji cikin jikinta ya dameta irin yau ba dan haka ma ta tashi da niyyar da dare zataje Asibiti ita ko Inducing ne su mata ta haihu amma banda CS tunda naqudar taqi tazo. Tuwonta taci da Koko da already Ruqayyan ta hada mata su, a bakinta taji cewar da wurwuri Khalil ya fita a falon ta zauna bayan ta cewa Ruqayya ta hada abin karyawa zatayi baquwa yanzu tana hanya.
Wuraren goma da yan mintina Safina ta isa gidan Afujajan da ita kamar wadda ta dawo daga qauye, Umaimah ta kalleta ganinta da qatuwar jaka tace
"Ke kuma daga ina haka ga wata qwanqwamemeiyar jaka kamar wadda zakiyi tafiya?"
Safina ta zauna tana sauke numfashi tace
"Daga gidan Malam nake fitar ce tazo mun babu shiri tun Asuba n fita kai mun jakar ciki toh saboda tsaro me kuka rage a gidan?"
"Kamar na sani nace a hada miki abinci bari ta kawo" Umaimah ta fada kafin ta shiga kiran Ruqayya.
A daki suka qule seda Safina taci tayi nak kafin ta fara fiddo da kayan cikin jakar tana kallon Umaimah tace
"In gaya miki jiya naga Suleiman namun wani gani gani na sakashi abu ya qiyi shine fa yau babu shiri na bazama ina zan zauna kallon ruwa kwado yayi mun qafa?
Kedai ai duniya ta samu hankalinki ya kwanta Khalil ya dawo hannunki se yanda kikayi dashi, to kema ga saqonki inji Malam wannan turaren ne kuma yace na jaddada miki ki kula dashi karki kuma nemansa ki rasa" Safina ta fada tana bata wani dan qullin baqar leda. Drawer gefen gadonta taja ta saka a ciki daga nan suka ci gaba dayi, Mu'ayyadya shiga dakin da Sallama yana tafiya a hankali, seda ya gaida Safina kafin ya qarasa jikin Umaimah ya jingina ta dagoshi jin jikinsa da zafi tace
"Zazzabin ne ya dawo?"
Kai ya daga mata kafin ta sake cewa
"Toh me yasa baka kwanta a gurin Hajiya ba ka fito?"
"Hayaniya akeyi Momy duk su Momyn Sharada ne sukazo harda su Maman Kaduna ma su da yawa" ya bata amsa yana kwanciya akan gadon. Mamaki ya kamata jin yace mutane a bangaren Hajiya, su Jalilah ba baqi bane daman kullum suna tafe amma Maman Kaduna Maman su Lubna kenan dayace sunzo da yawa su kuma me ya kawosu?