Sashe 15
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A taqaice Abban yayi masa bayani, Dr yayi shiru yana saurarensa yana kallonta, yes she looks depressed kana ganinta kasan akwai abinda yake damunta. Seda Abbanya gama tsaf kafin ya kalle shi yace
"Ko zaku bamu some minutes nayi magana da daughter may be ni zata gaya mun abinda yake damunta daku ta kasa gaya muku" Miqewa sukayi suka koma wajen office din inda akwai kujeru se a sannan Mama take qorafin Yunwa takeji dan basu karya ba suka fito dan Haka Abbanya fita dubawa ko ze samo musu wani abinda zasu ci.
A ciki kuwa cikin lallami da dabara Dr Kabir ya samu Umaimah da yana fara mata tambayoyi ta saka kuka ta fara bashi amsa. Tambayarta yake akanme yake damunta? Wane yanayi take ji a jikinta da sauran abubuwa daya kamata likitan kwakwalwa kamar sa ya tambayi mara lafiyarsa.
Sosai mamaki ya qulle masa kai yanda take masa bayanin abinda takeji dangane da kishi akan wanda take so.
"Idanna ganshi da wata ko naji yayi maganar mace ji nake kamar zuciyata tana ci da wuta, kawai rayawa nake a raina zan iya kashe ko wacece ta shiga rayuwarsa kuma kome za'ayi mun bazan damu ba indai akan sa ne" Umaimah ta fada hankali kwance ba tareda shakku ko dar a zuciyarta.
"Uhm lallai kam akwai matsala" Dr kabir ya fada kafin yayi rubutu a wata takadda ya miqe tsaye yace mata yana zuwa.
Waje ya fita inda su Abba suke, a taqaice ya masa bayanin akwai gwajin da zasu mata guda uku, biyu zasuyi mata yanzu dayan kuma sedau suje Aminu Kano dan Injinsu na nan ya samu matsala. Abban yace ya bashi yaje ya biya kudin amma yaqi yace dai su bata abinci taci bari yaje ya gani idan gurin suna aiki.
Wasa wasa sega Umaimah a dakin gwajin kwakwalwa, gajin farko general check up ne na kwakwalwa dan a ga ko akwai wani ciwo data samu dalilin buguwa ko faduwa ko kuma an haifeta dashi ba'a sani ba se yanzu yake bayyana. Daga nan kuma akayi mata gwajin tunani.
Basu suka bar Dawanau ba se kusan la'asar, har suka isa gida jin kanta take wani gingirin kai yaji inji, dan dayan gwajin se wani satin ma sannan zasu samu saboda se da appointment. Wani lallaba ta Mama harma da sauran yan gidan suka shigayi kafin fitowar sakamakon gwaji tasan matsayinta.
Bayan sallar Magriba tana zaune ta jona wayarta da se lokacin ta tuna ashe tun jiyan a kashe take chaji, ta manta shaf data kashe ta jiyan qila shiyasa Khalil be kirata ba ya aiko yaro. Tuno sunansa da tayi nan da nan abinda take ji ya nemi dawo mata sabo, qoqarin kiran sunayen Allah ta shigayi kamar yanda Malam ya gaya mata amma shedan da ya rigada ya samu gurin zama me kyau a zuciyarya ya shiga bijiro mata da wasu tunanikan na banza raya mata yake yanzu fa jiya yaje neman aure gidan su wata qila ma an bashi ita, kai an bashi ma inane Khalil zeje neman aure ace za'a hana shi kawai seta shiga rera kuka mara sauti.
Qarar da wayar ta tayi ce ta sakata dagowa, sunan Khalil ta gani yana yawo akai, meya kira kuma ya gaya mata yanzu idan baso yake ya qarasa ta ba?
Da so samu ne bazata amsa wayar ba amma ina zuciyarta bazata iya ba, ta rigada ta yarda zuciyarta ta kamu da mummunan Son Khalil, So me tsanani irin wanda ka iya saka me yinsa ya zauce.
Tana can tana tunani bata san wayar ta katse ba sega wani kiran ya sake shigowa, ta miqa hannu ta dakkota ta saka a kunne ba tareda tayi magana ba.
"Hankalina ya tashi Umaimah, tun jiya nake kiran wayarki a kashe, dazu da safe nazo akace kun tafi Asibiti meya same ki daman baki da Lafiya ne?" Khalil ya jero mata tambayoyin ba tareda tsayawa ba. A maimakon ta bashi amsa sw kawai ta sakar masa sabon kuka me tafe da sheshsheqa,
"Yah salam Umaimah ki dena Kuka dan Allah kiyi mun magana ko jikin ne?" Ya fada yanda kasan shima ze fashe da kukan. Lallashinta ya ringayi amma kamar wanda yake qarawa wuta fetur haka ta ringa rusa masa kuka, bata san tsahon lokacin data dauka tana qona masa credit ba dan ta zata ma ya gaji ne ya ajiye wayar ba tareda ya kashe ba se ji tayi yace
"Zaki iya fitowa gani a qofar gida".
Da mamaki ta cire wayar ta duba, minti Arba'in da hudu ta kwashe tana masa kukan banza ashe tahowa yayi, seta miqe da zumbulelen Hijabin jikinta ta fito ta gani da gaske yake ko wasa ai kuwa ta hango shi a durqushe a qofar gidan suna gaisawa da Abba.
Rabewa tayi ta qi qarasawa har seda Abban yazo ze shiga gidan yace mata
"Ki bude masa sitting room ku zauna acan" zeta gyada kai ta juya ta dakko muqullin gurin ta bude kafinta leqa tayi masa iso.
Kallonta kawai yake kamar wanda ya samu Tv ita ko ta samu guri ta kame fuskar nan a hade kai kace wani mugun saqo ya kawo mata, sallamar Imran dan Anty Saratu ta katse musu shirun da sukayi, ya ajiye Try me daukeda ruwan roba da zobo se gireba a cikin wani dan bowl me kyau.
"Sannu nagode yaya sunanka?" Ya fada yana kama hannun yaron, Imran ya bashi amsa kafin ya zura hannu a aljihu ya zaro Yan dari biyar guda hudu ya bashi yace
"Maza jeka kasha sweet kaji" yaronya fita da gudunsa yana murna Umaimah ta raka shi da harara.
"Umaimah!!!" Ya kira sunanta da wani sauti da ya saka tsigar jiki ta zuba saboda yanda kiran ya shigeta, bata iya amsawa ba illah kyawawan idanunta data dagota zuba masa tana qare masa kallo. Khalil Kyakykyawa ne, irin kyan da kana kallonsa zaka ce wannan yanada kyau. Dukda baqi ne amma hakanbe boye kyansa ba, yana da hanci, ga bakinsa leben qasan yayi ja na saman baqi abinda yake qara matar da yammata akan sa kenan ga kuma wasu irin idanu da Allah yayi masa, koda yaushe ka kalli idonsa kamar mejin bacci, idan kuwa akayi sa'a ya budesu gaba daya akan ka mace ko namiji duk dakiyar ka se kaji wani abu me kama da tsoro ko kwarjininsa ya tsirga maka.
"Karki saka na komawa Hajiyata a rabi irin wannan kallo haka" ya fada yana waving hannayensa a gaban fuskarta ganin kamar ma bata gurin tsabar nisan da tayi a tunani.
"Oya tell me, meya sameki jiya gaba daya kin daga mun hankali gashi na kasa samunki a waya bare naji ya kike"
Kunya ce ta kamata amma ta kanne ta jefeshi da hararar wasa tace
"Wayace maka kallonka nakeyi? Me zan kalla mani itama wadda kaje gurin nata rufa ido kawai kayi mata tace tana sonka bawai dan ka hadu ba" ta fada cikin matuqar qarfin danne abinda take ji, so take ta bugi cikinsa taji ya ake ciki sannan taji view dinsa akanta dan bazata zauna a banza da wofi son sa ya kashe ta ba.
"Na hadu ko? Thank you for the complement, itama danaje jiya haka ta fada"
Yanda tayi da fuska dole ya fashe da dariyar dabe shirya ba, ya fuskanci yarinyar ta folla masa kamar yanda ya fada sonta ba tareda ya sani ba, yana kuma iya karantar tsananin kishinsa a kwayar idanunsa.
Dariyar da yayi ta qara qonawa Umaimah rai se kawai ta bude baki ta saka kuka,
"Allah ya baki haquri, waike baki san wasa ba komai kuka kamar wata Doll baby" ya fada yana zamowa gabanta. Hijab tasa ta rufe fuska taci gaba da shaqar kukanta, ta tabbata dagaske yana da wata ashe ba Nabila ce zata fara qirga kwanakin ta ba itace lokacin ta yayi.
Ganin da yayi dagaske fa take Kukan yasa ya sassauta murya ya shiga bata haquri,
"Wasa nake miki, kuma ko jiyan nan da kika ganmu ba dagaske nake miki ba Abokina Mansur na raka duba Maman budurwarsa bata da lafiya shine kwalliyar da kika ga munyi".
Dagowa tayi ta kalle shi irin kallon " ka tabbata?"
Da ido ya mayar mata da amsar "kiyarda dani" dole tayi qasa da kanta dan bazata iya jurewa kallon cikin idonsa ba, a haka ma tana ji kamar ta mutu saboda shi inaga yana mata wannan kallon me narkar da zuciya.
"Nifa bani da budurwa, gashi Hajiya ta takuramun aure take so nayi. Ranar fa da kika je gidan mu shikenan Hajiya ta saka ni a gaba akan ki ita a dole ke budurwa tace. Harfa ta gama gayawa sisters dina nayi mata. Harfa gurin Sister ki taje akan taso tazo nan gidan tayi magana kafin a turo maza dakyar fa na fahimtar da ita ni babu komai tsakanin mu, ta yarda amma ta kafa mun sharadin kafin qarshen shekarar nan dole nayi aure gashi ni ko budurwa bani da ita yanzu bansan yanda zanyi ba, ko kina da qawa ko qanwa data shirya aure ki hada ni da ita? Ni kinga tsoron yammata nake ban taba zuwa nace wa wata ina sonta ba".
PROMO
PROMO
PROMO
BEFORE 4K NOW 2500
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA 👇🏻
08162859027
AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA
INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO
SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 8
"Ko zaku bamu some minutes nayi magana da daughter may be ni zata gaya mun abinda yake damunta daku ta kasa gaya muku" Miqewa sukayi suka koma wajen office din inda akwai kujeru se a sannan Mama take qorafin Yunwa takeji dan basu karya ba suka fito dan Haka Abbanya fita dubawa ko ze samo musu wani abinda zasu ci.
A ciki kuwa cikin lallami da dabara Dr Kabir ya samu Umaimah da yana fara mata tambayoyi ta saka kuka ta fara bashi amsa. Tambayarta yake akanme yake damunta? Wane yanayi take ji a jikinta da sauran abubuwa daya kamata likitan kwakwalwa kamar sa ya tambayi mara lafiyarsa.
Sosai mamaki ya qulle masa kai yanda take masa bayanin abinda takeji dangane da kishi akan wanda take so.
"Idanna ganshi da wata ko naji yayi maganar mace ji nake kamar zuciyata tana ci da wuta, kawai rayawa nake a raina zan iya kashe ko wacece ta shiga rayuwarsa kuma kome za'ayi mun bazan damu ba indai akan sa ne" Umaimah ta fada hankali kwance ba tareda shakku ko dar a zuciyarta.
"Uhm lallai kam akwai matsala" Dr kabir ya fada kafin yayi rubutu a wata takadda ya miqe tsaye yace mata yana zuwa.
Waje ya fita inda su Abba suke, a taqaice ya masa bayanin akwai gwajin da zasu mata guda uku, biyu zasuyi mata yanzu dayan kuma sedau suje Aminu Kano dan Injinsu na nan ya samu matsala. Abban yace ya bashi yaje ya biya kudin amma yaqi yace dai su bata abinci taci bari yaje ya gani idan gurin suna aiki.
Wasa wasa sega Umaimah a dakin gwajin kwakwalwa, gajin farko general check up ne na kwakwalwa dan a ga ko akwai wani ciwo data samu dalilin buguwa ko faduwa ko kuma an haifeta dashi ba'a sani ba se yanzu yake bayyana. Daga nan kuma akayi mata gwajin tunani.
Basu suka bar Dawanau ba se kusan la'asar, har suka isa gida jin kanta take wani gingirin kai yaji inji, dan dayan gwajin se wani satin ma sannan zasu samu saboda se da appointment. Wani lallaba ta Mama harma da sauran yan gidan suka shigayi kafin fitowar sakamakon gwaji tasan matsayinta.
Bayan sallar Magriba tana zaune ta jona wayarta da se lokacin ta tuna ashe tun jiyan a kashe take chaji, ta manta shaf data kashe ta jiyan qila shiyasa Khalil be kirata ba ya aiko yaro. Tuno sunansa da tayi nan da nan abinda take ji ya nemi dawo mata sabo, qoqarin kiran sunayen Allah ta shigayi kamar yanda Malam ya gaya mata amma shedan da ya rigada ya samu gurin zama me kyau a zuciyarya ya shiga bijiro mata da wasu tunanikan na banza raya mata yake yanzu fa jiya yaje neman aure gidan su wata qila ma an bashi ita, kai an bashi ma inane Khalil zeje neman aure ace za'a hana shi kawai seta shiga rera kuka mara sauti.
Qarar da wayar ta tayi ce ta sakata dagowa, sunan Khalil ta gani yana yawo akai, meya kira kuma ya gaya mata yanzu idan baso yake ya qarasa ta ba?
Da so samu ne bazata amsa wayar ba amma ina zuciyarta bazata iya ba, ta rigada ta yarda zuciyarta ta kamu da mummunan Son Khalil, So me tsanani irin wanda ka iya saka me yinsa ya zauce.
Tana can tana tunani bata san wayar ta katse ba sega wani kiran ya sake shigowa, ta miqa hannu ta dakkota ta saka a kunne ba tareda tayi magana ba.
"Hankalina ya tashi Umaimah, tun jiya nake kiran wayarki a kashe, dazu da safe nazo akace kun tafi Asibiti meya same ki daman baki da Lafiya ne?" Khalil ya jero mata tambayoyin ba tareda tsayawa ba. A maimakon ta bashi amsa sw kawai ta sakar masa sabon kuka me tafe da sheshsheqa,
"Yah salam Umaimah ki dena Kuka dan Allah kiyi mun magana ko jikin ne?" Ya fada yanda kasan shima ze fashe da kukan. Lallashinta ya ringayi amma kamar wanda yake qarawa wuta fetur haka ta ringa rusa masa kuka, bata san tsahon lokacin data dauka tana qona masa credit ba dan ta zata ma ya gaji ne ya ajiye wayar ba tareda ya kashe ba se ji tayi yace
"Zaki iya fitowa gani a qofar gida".
Da mamaki ta cire wayar ta duba, minti Arba'in da hudu ta kwashe tana masa kukan banza ashe tahowa yayi, seta miqe da zumbulelen Hijabin jikinta ta fito ta gani da gaske yake ko wasa ai kuwa ta hango shi a durqushe a qofar gidan suna gaisawa da Abba.
Rabewa tayi ta qi qarasawa har seda Abban yazo ze shiga gidan yace mata
"Ki bude masa sitting room ku zauna acan" zeta gyada kai ta juya ta dakko muqullin gurin ta bude kafinta leqa tayi masa iso.
Kallonta kawai yake kamar wanda ya samu Tv ita ko ta samu guri ta kame fuskar nan a hade kai kace wani mugun saqo ya kawo mata, sallamar Imran dan Anty Saratu ta katse musu shirun da sukayi, ya ajiye Try me daukeda ruwan roba da zobo se gireba a cikin wani dan bowl me kyau.
"Sannu nagode yaya sunanka?" Ya fada yana kama hannun yaron, Imran ya bashi amsa kafin ya zura hannu a aljihu ya zaro Yan dari biyar guda hudu ya bashi yace
"Maza jeka kasha sweet kaji" yaronya fita da gudunsa yana murna Umaimah ta raka shi da harara.
"Umaimah!!!" Ya kira sunanta da wani sauti da ya saka tsigar jiki ta zuba saboda yanda kiran ya shigeta, bata iya amsawa ba illah kyawawan idanunta data dagota zuba masa tana qare masa kallo. Khalil Kyakykyawa ne, irin kyan da kana kallonsa zaka ce wannan yanada kyau. Dukda baqi ne amma hakanbe boye kyansa ba, yana da hanci, ga bakinsa leben qasan yayi ja na saman baqi abinda yake qara matar da yammata akan sa kenan ga kuma wasu irin idanu da Allah yayi masa, koda yaushe ka kalli idonsa kamar mejin bacci, idan kuwa akayi sa'a ya budesu gaba daya akan ka mace ko namiji duk dakiyar ka se kaji wani abu me kama da tsoro ko kwarjininsa ya tsirga maka.
"Karki saka na komawa Hajiyata a rabi irin wannan kallo haka" ya fada yana waving hannayensa a gaban fuskarta ganin kamar ma bata gurin tsabar nisan da tayi a tunani.
"Oya tell me, meya sameki jiya gaba daya kin daga mun hankali gashi na kasa samunki a waya bare naji ya kike"
Kunya ce ta kamata amma ta kanne ta jefeshi da hararar wasa tace
"Wayace maka kallonka nakeyi? Me zan kalla mani itama wadda kaje gurin nata rufa ido kawai kayi mata tace tana sonka bawai dan ka hadu ba" ta fada cikin matuqar qarfin danne abinda take ji, so take ta bugi cikinsa taji ya ake ciki sannan taji view dinsa akanta dan bazata zauna a banza da wofi son sa ya kashe ta ba.
"Na hadu ko? Thank you for the complement, itama danaje jiya haka ta fada"
Yanda tayi da fuska dole ya fashe da dariyar dabe shirya ba, ya fuskanci yarinyar ta folla masa kamar yanda ya fada sonta ba tareda ya sani ba, yana kuma iya karantar tsananin kishinsa a kwayar idanunsa.
Dariyar da yayi ta qara qonawa Umaimah rai se kawai ta bude baki ta saka kuka,
"Allah ya baki haquri, waike baki san wasa ba komai kuka kamar wata Doll baby" ya fada yana zamowa gabanta. Hijab tasa ta rufe fuska taci gaba da shaqar kukanta, ta tabbata dagaske yana da wata ashe ba Nabila ce zata fara qirga kwanakin ta ba itace lokacin ta yayi.
Ganin da yayi dagaske fa take Kukan yasa ya sassauta murya ya shiga bata haquri,
"Wasa nake miki, kuma ko jiyan nan da kika ganmu ba dagaske nake miki ba Abokina Mansur na raka duba Maman budurwarsa bata da lafiya shine kwalliyar da kika ga munyi".
Dagowa tayi ta kalle shi irin kallon " ka tabbata?"
Da ido ya mayar mata da amsar "kiyarda dani" dole tayi qasa da kanta dan bazata iya jurewa kallon cikin idonsa ba, a haka ma tana ji kamar ta mutu saboda shi inaga yana mata wannan kallon me narkar da zuciya.
"Nifa bani da budurwa, gashi Hajiya ta takuramun aure take so nayi. Ranar fa da kika je gidan mu shikenan Hajiya ta saka ni a gaba akan ki ita a dole ke budurwa tace. Harfa ta gama gayawa sisters dina nayi mata. Harfa gurin Sister ki taje akan taso tazo nan gidan tayi magana kafin a turo maza dakyar fa na fahimtar da ita ni babu komai tsakanin mu, ta yarda amma ta kafa mun sharadin kafin qarshen shekarar nan dole nayi aure gashi ni ko budurwa bani da ita yanzu bansan yanda zanyi ba, ko kina da qawa ko qanwa data shirya aure ki hada ni da ita? Ni kinga tsoron yammata nake ban taba zuwa nace wa wata ina sonta ba".
PROMO
PROMO
PROMO
BEFORE 4K NOW 2500
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA 👇🏻
08162859027
AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA
INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO
SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 8