Sashe 65
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kafin Azahar gida ya dinke da jama'a daga bangarenta har zuwa Na Khalil ta ko ina se bubbulowa sukeyi dole se wangale Get din gidan akayi suka saka kujeru tu daga waje har ciki dan daman an tanade su kafin yamma su koma cikin Wani Kango dake gefensu na Mijin Maman Hibban ne su Anty Hafsa suka roqi alfarma aka ara musu tunda taqi bari a fita a kama guri kamar yanda sukayi Na Nuratu sunce duk da haka se sun dakko Dj sunci uwar sabada yau Umaimah Qiriniya tayi Da.
Tunda tayi kwalliyar shaddar Anty Hafsa take baza ido taga ta saka sarqarta taga wayam se wata fashion me kyau ta saka se tayi tunanin ko ta bari ne da yamma idan tayi kwalliya sannan zata saka haka kuwa akayi bayan la'asar me kwalliyar da suka kira ta gama tsatsowa Umaimah kyanta dukda ba wata me yawa akayi mata ba, ta daura mata gwagwgwaronta fuskar nan ta fito tas kamar ranar ne auransu da Khalil tasha kwalliya da wani Dan ubansun Lace da akayi mata dinkin fitted Bubu ta cikata saboda qibar da tayi se hakan ya qara fitar da kyan dinkin da kwalliyarta.
A dakin Khalil ta qarasa shiryawa tana tsaka da saka dankunne Anty Hafsa ta shiga dakin cikin kwalliya tana kallonta tace
"Kai Umai kinyi kyau masha Allah daman ga Khalil can a waje bari a kirashi yazo kuyi hoto kar kwalliyar ta tafi a banza" harta juya idonta ya kai kan sarqar data saka seta dawo tana cewa
"Aa ya haka? Wai ina sarqar ki ne da kike ta fama da wasu fashion malama dakko ta ki saka ko kuwa daman dan ki ajiye aka siya miki"
"Kin rigani jira nakeyi in idar da Sallah nima nayi mata magana tun safe nake saka ido naga ta saka ban gani ba" Anty Laure data idar da sallah ta fada. Se Umaimah ta shiga zare ido, gaban Safe box din Khalil ta isa ta bude gurin security swta kalli Anty Hafsan tace
"Ya kulle kuma bansan password din ba"
"Se ki kirashi a waya ya gaya miki ai meye amfanin siyan ta idan bazaki saka a gani ba" Anty Laure ta sakw fada tana miqa mata wayarta,bata da mafita ta karba ta hau danne danne a ranta tana shirya yanda zata kufcewa wannan tuhunar tasu, to me zata ce musu? Kusan kwana goma kenan rabon da suyi magana da Maman Nihal, daman tunda tace mata ta tafi America suka dena waya a WhatsApp suke chatting tace mata Walid din ya koma makaranta daga baya kuma tace wai ta manta ta tafi da key din dakin nata sedai idan ta dawo kuma zasu biya Saudiyya suyi Umara a taqaice dai se nan da kusan wata daya take shirin dawowa daga baya ma ya zama idan tayi mata magana baya tafiya duk da har sannan Umaiman bata kawo komai a ranta ba, se jiya data kira layin Maman Hanif din taji ya shiga har ta daga se kuma ta kashe daga nan kuma take ta kira baya shiga abinda yasa hankalinta ya tashi kenan da rashin sanin abinda take nufi da ita kuma ta rasa dawa zatayi maganar tunda babu wanda yasan sanda akayi sedai idan ta tuna da tata a hannunta hankalinta yana kwanciya yanzun ma gudun tambayoyi ne ze hana ta saka ta Maman Hanif din.
"Anty yace baze iya ratso cikin mata ya shigo ba kuma fingerprint ne security din" Umaimah data gama qayar qarya ta fada, Anty Hafsa da Anty Laure suka kalli juna kafin suka fita suka barta ta qarasa shirinta a ranta ta qudure zuwa gobe idan bata samu Maman Hanifa gaskiya zata bada akai sarqar nan kasuwa a siyar, ta cire kudin tata ta siyi wata ragowar ta tura mata tunda tana da account number ta data karba ta tura mata da 20k a matsayin gudummawar bikin Hamida wanda dakyar ta turo matan.
Ansha taron suna an raqashe kkwa ya koma gida cikin farin ciki, daga gurin suna Anty Hafsa kaitsaye gida ta wuce gurin Mama dan ita bataje gidan sunan ba wai me zataje tayi duk ga sunan Hajiyar Khalil dai taje abinta da sauran yan uwanta. A taqaice Anty Hafsa tayiwa Maman Bayanin ita fa bata yarda da zancen Umaimah ba dan idan dagaske ne da tun safe zata saka ya bude mata ta dauki duk abinda zatayi amfani dashi ai Mama tace mata ta rabu da ita kar kuma tayiwa kowa magana ai gobe zata zo gidan ta sameta.
Haka kuwa akayi washe gari da wuri sukayi suyar nama suka raba kowanne bangare suka dauki nasu, daman sun gama shirin su tsaf Anty ta kira Khalil daya fita tun safe akan zasu tafi yace besan zance ba, kashe wayar tayi ta kira Hajiyarsa dan tuni sun gama magana da ita tace ba matsala su jira kusan minti Ashirin se gashi yana cika yana batsewa haka yaje ya kaisu gida. A tsohon dakinsu da yake a gyare dan anan Nuratu ta zauna, ana gobe Umaimah zata haihu tayi arba'in ta koma gidanta dan haka qara shareshi kawai akayi aka zuba musu nasu kayan.
Se dare Mama ta sameta a daki tana zaune tana shayar da Mu'ayyad suna magana da Khalil dake ta faman zuba qorafi a waya, jiranta tayi harta gama sannan ta kalleta tace
"Ranki ya dade banga kinsaka sarqarki a hotunan suna ba, bata tayi ko kinyi kyauta da ita"
"Mama nafa gayawa Anty Hafsa tana cikin safe box din Abban Mu'ayyad kuma lokacin akwai mutane yace baze iya shigowa ba amma tana nan babu inda taje hauka nake zan bada aro? Mantawa nayi ma dazu da mun taho da ita amma zance ya kawo mun" Umaiman ta fada tana zumbura baki, Mama tayi qwafa tace
"Zaki ci ubanki keda Safe box din, Allah ya kaimu goben ki kira Khalil din kice ya kawo mun da safe kafin ya wuce aiki"
"Haba Mama kamar wani abin tashin hankali, a bari dai da daddare idan ze zo ganin mu seya kawo" ta fada tan dan murmushi, Mama tayi qwafa ba tareda tace mata komai ba ta fita.
Seda aka kwashe sati biyu tsakani Mama bata sake yi mata magana ba itama kuma da ba gaskiya ce da ita ba daman bata tada zancen ba, kullum cikin gwada layin Maman Nihal takeyi amma amsar daya ce a kashe yake a group ma tayi cigiyarta aka ce tace ta tafi America har Rufaida na mata tsiyar ita da Aminiyarta ai ita za'ayi cigiyar Maman Nihal a gurinta.
Da safe ranar Mama ta sake tirketa da zancen, Umaimah tayi fiqi fiqi da ido dan qaryarta ta qare Mama waya ta dakko tace zata kira Khalil din, cikim muryar damuwa tace
"Mama dan Allah karki kirashi, abinda yasa kika ga ina tayi miki kwana kwana wallahi sarqar Khalil din ne ya karba. Wata kwangila yakeyi kudi suka yanke masa, shine ya karba yace idan an biyashi se ya mayar mun da wata".
Kallonta kawai Mama takeyi har ta kai qarshen maganar, kwata kwata zancen be shiga kanta ba amma kuma bazata ce bata yarda ba saboda yana iya zama gaskiya Khalil din ya karba se kawai ta miqe tana cewa
"Toh Allah ya rufa asiri tuntuni me yasa baki fada ba kika tsaya kina nuqu nuqu"
"Shi yace mun baya so kowa ya sani kawai idan ya samu kudi ze siyamun wani" Umaimah ta fada tana dauke kanta gefe, Mama ta kalleta, bata yarda da zancen nan ba amma koma yayanw zata bincika taji dan lamarin Umaimah babu Allah a ciki.
Hafsa ta kira take shaidawa yanda sukayi da Umaiman,
"Zata iya yuwuwa Mama tunda kinga yayi hidima sosai da sunan nan ze mayar matan kamar yanda yace" Anty Hafsa ta fada. Mama bata haqura ba ta kira Naziyya, tana shaida mata ta bushe da dariya tace
"Kuma kin yarda Mama, Khalil din ne ze karbar mata sarqa ya siyar idan zeyi haka me yasa tun farko ya siya mata, ai seya bar kudinsa ya gama kwangilar sannan duk abinda zeyi yayi ko? Qarya takeyi ki matsata zata fadi duk inda ta kaita sedai idan kuma itan ce ta siyar wannan se muji inda takai kudin. Nidai akwai ranar da naje gidanta ta rako wata baquwa idan dai ba idona bane to sak sarqar na gani a wuyan baquwar".
"Ai kuwa dole ma ta fadamun yanda tayi da ita dan sam hankalina be dauki cewar Khalil ne ya karba ba, amma zanyi maganinta, Khalil din zan tambaya da kaina duk ma yanda akayi zanji" Mama ta fada daga nan sukayi sallama. Barinta tayi seda aka kwana uku tsakani ranar Khalil yazo da daddare, yana zaune a dakin da Umaiman take yana cin tuwo, Mu'ayyad na hannunsa yaron yayi bulbul dashi tabarakallah bazakace dan kwana Talatin da wani abu bane.
Mama tayi sallama a bakin qofa suka amsa ta daga labule ta shiga, seda suka sakw gaisawa a zuciyar Umainah tana ayyana maganar qarin kwanaki akan Arba'in din sune dan yan gidansu duka zasuyi tafiya zuwa Qaraye bikin diyar wani Abokin wasan Abbansu kwana biyu bayan Arba'in dinta, shine tace Anty ta sa baki Mama ta yarda A tambayi Khalil ta qara sati daya suje tare.
Rigigib qirjinta ya buga sanda taji Mama na tambayar Khalil zancen sarqa, ko kusa bata taba zaton Maman zatayi haka ba shi yasa data tashi ta jona qaryar dashi, Khalil ya saki baki tsabar mamaki yana kallonta Mama dake kallonsu gaba daya tayi murmushin takaici dan yanayin fuskarsa ya fahimtar da ita besan zancen ba.
"Wallahi Mama ko naira hamsin ban taba ranta a hannun Umaimah ba ballantana na karbar mata sarqa na siyar, nifa kyauta na bata bayan haka ba kudi na ne kadai a ciki ba harda naki idan ma zan karba ai se nace tayi shawara dake sannan" Khalil ya fada yana kallon Umaimah data duqe kai qasa kamar ta fasa kuka.
Mama ta kalleta tace
"Zaki fadi inda kika kaita ko kuwa har yanzu kina da sauran qaryar da zaki fada?"
Tunda tayi kwalliyar shaddar Anty Hafsa take baza ido taga ta saka sarqarta taga wayam se wata fashion me kyau ta saka se tayi tunanin ko ta bari ne da yamma idan tayi kwalliya sannan zata saka haka kuwa akayi bayan la'asar me kwalliyar da suka kira ta gama tsatsowa Umaimah kyanta dukda ba wata me yawa akayi mata ba, ta daura mata gwagwgwaronta fuskar nan ta fito tas kamar ranar ne auransu da Khalil tasha kwalliya da wani Dan ubansun Lace da akayi mata dinkin fitted Bubu ta cikata saboda qibar da tayi se hakan ya qara fitar da kyan dinkin da kwalliyarta.
A dakin Khalil ta qarasa shiryawa tana tsaka da saka dankunne Anty Hafsa ta shiga dakin cikin kwalliya tana kallonta tace
"Kai Umai kinyi kyau masha Allah daman ga Khalil can a waje bari a kirashi yazo kuyi hoto kar kwalliyar ta tafi a banza" harta juya idonta ya kai kan sarqar data saka seta dawo tana cewa
"Aa ya haka? Wai ina sarqar ki ne da kike ta fama da wasu fashion malama dakko ta ki saka ko kuwa daman dan ki ajiye aka siya miki"
"Kin rigani jira nakeyi in idar da Sallah nima nayi mata magana tun safe nake saka ido naga ta saka ban gani ba" Anty Laure data idar da sallah ta fada. Se Umaimah ta shiga zare ido, gaban Safe box din Khalil ta isa ta bude gurin security swta kalli Anty Hafsan tace
"Ya kulle kuma bansan password din ba"
"Se ki kirashi a waya ya gaya miki ai meye amfanin siyan ta idan bazaki saka a gani ba" Anty Laure ta sakw fada tana miqa mata wayarta,bata da mafita ta karba ta hau danne danne a ranta tana shirya yanda zata kufcewa wannan tuhunar tasu, to me zata ce musu? Kusan kwana goma kenan rabon da suyi magana da Maman Nihal, daman tunda tace mata ta tafi America suka dena waya a WhatsApp suke chatting tace mata Walid din ya koma makaranta daga baya kuma tace wai ta manta ta tafi da key din dakin nata sedai idan ta dawo kuma zasu biya Saudiyya suyi Umara a taqaice dai se nan da kusan wata daya take shirin dawowa daga baya ma ya zama idan tayi mata magana baya tafiya duk da har sannan Umaiman bata kawo komai a ranta ba, se jiya data kira layin Maman Hanif din taji ya shiga har ta daga se kuma ta kashe daga nan kuma take ta kira baya shiga abinda yasa hankalinta ya tashi kenan da rashin sanin abinda take nufi da ita kuma ta rasa dawa zatayi maganar tunda babu wanda yasan sanda akayi sedai idan ta tuna da tata a hannunta hankalinta yana kwanciya yanzun ma gudun tambayoyi ne ze hana ta saka ta Maman Hanif din.
"Anty yace baze iya ratso cikin mata ya shigo ba kuma fingerprint ne security din" Umaimah data gama qayar qarya ta fada, Anty Hafsa da Anty Laure suka kalli juna kafin suka fita suka barta ta qarasa shirinta a ranta ta qudure zuwa gobe idan bata samu Maman Hanifa gaskiya zata bada akai sarqar nan kasuwa a siyar, ta cire kudin tata ta siyi wata ragowar ta tura mata tunda tana da account number ta data karba ta tura mata da 20k a matsayin gudummawar bikin Hamida wanda dakyar ta turo matan.
Ansha taron suna an raqashe kkwa ya koma gida cikin farin ciki, daga gurin suna Anty Hafsa kaitsaye gida ta wuce gurin Mama dan ita bataje gidan sunan ba wai me zataje tayi duk ga sunan Hajiyar Khalil dai taje abinta da sauran yan uwanta. A taqaice Anty Hafsa tayiwa Maman Bayanin ita fa bata yarda da zancen Umaimah ba dan idan dagaske ne da tun safe zata saka ya bude mata ta dauki duk abinda zatayi amfani dashi ai Mama tace mata ta rabu da ita kar kuma tayiwa kowa magana ai gobe zata zo gidan ta sameta.
Haka kuwa akayi washe gari da wuri sukayi suyar nama suka raba kowanne bangare suka dauki nasu, daman sun gama shirin su tsaf Anty ta kira Khalil daya fita tun safe akan zasu tafi yace besan zance ba, kashe wayar tayi ta kira Hajiyarsa dan tuni sun gama magana da ita tace ba matsala su jira kusan minti Ashirin se gashi yana cika yana batsewa haka yaje ya kaisu gida. A tsohon dakinsu da yake a gyare dan anan Nuratu ta zauna, ana gobe Umaimah zata haihu tayi arba'in ta koma gidanta dan haka qara shareshi kawai akayi aka zuba musu nasu kayan.
Se dare Mama ta sameta a daki tana zaune tana shayar da Mu'ayyad suna magana da Khalil dake ta faman zuba qorafi a waya, jiranta tayi harta gama sannan ta kalleta tace
"Ranki ya dade banga kinsaka sarqarki a hotunan suna ba, bata tayi ko kinyi kyauta da ita"
"Mama nafa gayawa Anty Hafsa tana cikin safe box din Abban Mu'ayyad kuma lokacin akwai mutane yace baze iya shigowa ba amma tana nan babu inda taje hauka nake zan bada aro? Mantawa nayi ma dazu da mun taho da ita amma zance ya kawo mun" Umaiman ta fada tana zumbura baki, Mama tayi qwafa tace
"Zaki ci ubanki keda Safe box din, Allah ya kaimu goben ki kira Khalil din kice ya kawo mun da safe kafin ya wuce aiki"
"Haba Mama kamar wani abin tashin hankali, a bari dai da daddare idan ze zo ganin mu seya kawo" ta fada tan dan murmushi, Mama tayi qwafa ba tareda tace mata komai ba ta fita.
Seda aka kwashe sati biyu tsakani Mama bata sake yi mata magana ba itama kuma da ba gaskiya ce da ita ba daman bata tada zancen ba, kullum cikin gwada layin Maman Nihal takeyi amma amsar daya ce a kashe yake a group ma tayi cigiyarta aka ce tace ta tafi America har Rufaida na mata tsiyar ita da Aminiyarta ai ita za'ayi cigiyar Maman Nihal a gurinta.
Da safe ranar Mama ta sake tirketa da zancen, Umaimah tayi fiqi fiqi da ido dan qaryarta ta qare Mama waya ta dakko tace zata kira Khalil din, cikim muryar damuwa tace
"Mama dan Allah karki kirashi, abinda yasa kika ga ina tayi miki kwana kwana wallahi sarqar Khalil din ne ya karba. Wata kwangila yakeyi kudi suka yanke masa, shine ya karba yace idan an biyashi se ya mayar mun da wata".
Kallonta kawai Mama takeyi har ta kai qarshen maganar, kwata kwata zancen be shiga kanta ba amma kuma bazata ce bata yarda ba saboda yana iya zama gaskiya Khalil din ya karba se kawai ta miqe tana cewa
"Toh Allah ya rufa asiri tuntuni me yasa baki fada ba kika tsaya kina nuqu nuqu"
"Shi yace mun baya so kowa ya sani kawai idan ya samu kudi ze siyamun wani" Umaimah ta fada tana dauke kanta gefe, Mama ta kalleta, bata yarda da zancen nan ba amma koma yayanw zata bincika taji dan lamarin Umaimah babu Allah a ciki.
Hafsa ta kira take shaidawa yanda sukayi da Umaiman,
"Zata iya yuwuwa Mama tunda kinga yayi hidima sosai da sunan nan ze mayar matan kamar yanda yace" Anty Hafsa ta fada. Mama bata haqura ba ta kira Naziyya, tana shaida mata ta bushe da dariya tace
"Kuma kin yarda Mama, Khalil din ne ze karbar mata sarqa ya siyar idan zeyi haka me yasa tun farko ya siya mata, ai seya bar kudinsa ya gama kwangilar sannan duk abinda zeyi yayi ko? Qarya takeyi ki matsata zata fadi duk inda ta kaita sedai idan kuma itan ce ta siyar wannan se muji inda takai kudin. Nidai akwai ranar da naje gidanta ta rako wata baquwa idan dai ba idona bane to sak sarqar na gani a wuyan baquwar".
"Ai kuwa dole ma ta fadamun yanda tayi da ita dan sam hankalina be dauki cewar Khalil ne ya karba ba, amma zanyi maganinta, Khalil din zan tambaya da kaina duk ma yanda akayi zanji" Mama ta fada daga nan sukayi sallama. Barinta tayi seda aka kwana uku tsakani ranar Khalil yazo da daddare, yana zaune a dakin da Umaiman take yana cin tuwo, Mu'ayyad na hannunsa yaron yayi bulbul dashi tabarakallah bazakace dan kwana Talatin da wani abu bane.
Mama tayi sallama a bakin qofa suka amsa ta daga labule ta shiga, seda suka sakw gaisawa a zuciyar Umainah tana ayyana maganar qarin kwanaki akan Arba'in din sune dan yan gidansu duka zasuyi tafiya zuwa Qaraye bikin diyar wani Abokin wasan Abbansu kwana biyu bayan Arba'in dinta, shine tace Anty ta sa baki Mama ta yarda A tambayi Khalil ta qara sati daya suje tare.
Rigigib qirjinta ya buga sanda taji Mama na tambayar Khalil zancen sarqa, ko kusa bata taba zaton Maman zatayi haka ba shi yasa data tashi ta jona qaryar dashi, Khalil ya saki baki tsabar mamaki yana kallonta Mama dake kallonsu gaba daya tayi murmushin takaici dan yanayin fuskarsa ya fahimtar da ita besan zancen ba.
"Wallahi Mama ko naira hamsin ban taba ranta a hannun Umaimah ba ballantana na karbar mata sarqa na siyar, nifa kyauta na bata bayan haka ba kudi na ne kadai a ciki ba harda naki idan ma zan karba ai se nace tayi shawara dake sannan" Khalil ya fada yana kallon Umaimah data duqe kai qasa kamar ta fasa kuka.
Mama ta kalleta tace
"Zaki fadi inda kika kaita ko kuwa har yanzu kina da sauran qaryar da zaki fada?"