Sashe 188
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Seda ya kalli bangaren da Umaimah take yaga hankalinta nakan Tv besan kunnuwanta na nan ta bazasu tana jiran taji dawa yake waya ba kafin yace
"Tafiyar nan an fasa babu ita Anwar se wani lokacin idan Allah ya kaimu"
"Toh, amma dai shikenan, Allah ya nuna mana lokacin yasa hakan shine mafi Alkhairi" Anwar da yayi niyyar yin magana ya fasa saboda tunawa da yayi da dabi'ar Khalil din kuma yaji maganar na dawo masa kar yaje ya kunno wutar da ba zata kasu ba. Sallama sukayi akan se gobe sa hadu a office idan yaji dadin qafarsa yaci gaba da cin Naman yana satar Kallonta be wani ci da yawa ba ya rufe ya wanke hannunsa ya koma cikin falon.
"Har ka cinye" ta fada tana kallonsa seya zauna yana cewa
"Aa kadan naci na rigada naci abinci gurin Hajiya, ko ajiye mun ragowar da safe se na qarasa".
Shiru sukayi na dan lokaci ya canza tashar labarai yana kallo yaji ta sake cewa
"Ka fasa tafiya goben kenan"
"Eh wlh saboda ciwon qafar nan bazan iya dogon zama a mota ba, daman wani aiki muka samu zamuje dubawa amma na basu uzuri idan naji sauqi se muje ko kuma Anwar da su Patrick suje kawai" ya bata amsa yana duba wayarsa da yaji saqo ya shigo, Humaira ce ta aiko masa da wani zazzafan Text na soyayya ya karanta ya sake karantawa ya tabbatar wannan aikin Unaizatu ne seya maida mata da martanin
"I love you, karkiyi bacci zan kiraki seki fadamun kalaman nan da bakinki bana son su a rubuce"
"Ni kashe wayat zanyi ma yanzu, i love you more Gud nyt" ta maida masa itama yana karantawa kuwa ya shiga kiranta amma a kashe kamar yanda yace din ya daga kai yana murmushi ze dauki remote karaf suka hada ido da Umaimah da tun fara dannan wayar tasa take kallonsa.
Duburburcewa yayi dan gaba daya ya manta da tana zaune a gun, ya saba zama a falonsa shi kadai shiyasa yanzu ma yaji kamar a can yake se ya shiga borin kunya dason kare kansa daga balahirar ta yace
"Wani abu na gani a Twitter ya bani dariya"
"Uhm" tace masa tana maida kanta kan tata wayar da suke chat da Safina tana gaya mata yaci naman, daman Yajin Maganin barbade kazar tayi dashi dan karma a samu akasi yace baze dan gwala da yaji ba dan haka yake wani lokacin.
Khalil kuwa satar kallonta ya ringayi ganin bata kulashi ba yasa ya shiga WhatsApp, saqon Anwar ya gani yana tambayarsa da gaske an fasa zuwa nan yayi masa bayanin Su Baba Abu zasuje
"I thought that bana so nayi subutar baki ko Sarautar tana kusa na tada Bomb shiyasa nayi shiru" Anwar ya tsokanesa, seya kalli Umaimah data dukufa tana danna waya kafin ya maida masa da cewa
"Aiko da sedai na taho gidanka na kwana dan tana kusa kuma yai kaga abin Allah har girki tayi mun alamun ta fara sakkowa kenan kafin azo ayi fadan qarshe"
Emojin dariya Anwar ya turo masa da cewar
"Ai ko fadan qarshe a kashe Boss, Ni'ima na nan tunda na gaya mata zaka qara aure wai jira kawai take ranar tazo ta qagu taji ana bada labarin Abinda Umaimah tayi ta ringa cewa ai ta santa matar Abokin Mijinta ce"
"Ni'imar nan taka is Sick Anwar, ka gaya mata babu abinda ze faru se Alkhairi jikina yana bani hakan"
"I pray so Bro, ka ci gaba da Addu'a Allah ya kawo komai cikin sauqi, bari naje na lallaba Baby na tayi bacci Bye" Anwar ya maido masa da Amsa. Murmushi Khalil yayi ya kashe Datansa ya kalli inda Umaimah take yaga bata nan ta shiga daki kenan.
Dakyar yaja qafarsa yana cije baki zaman da yayi yasa ta qara yi masa nauyi ya isa qofar dakin nata ya kwankwasa.
"Come in" ta bashi amsa ya tura qofar da Sallama, tana kwance har taja bargo ta rufe jikinta saboda uban Ac data warewa dakin seya qarasa ya zauna gefen gadon yana cewa
"Idan bazan takura miki ba zan kwanta a nan qafata ta matsa mun bazan iya hawa sama ba"
"Mutum da gidansa se ya nemi izinin inda ze kwanta" ta bashi amsa tana gyra kwanciyarta, baya ta juya masa yayi murmushi kawai yana kallonta seya miqe dakyar ya wuce bandaki, alwala ya dauro ya dawo dakin, seda ya rage qarfin Ac kafin ya kwanta a gefenta yana sauke numfashi gaba daya qamshin turaren data saka ya dameshi ya nemi saka shi a wani hali. Kanta zuwa Bayanta ya shiga shafawa a hankali Umaimah dake jinsa tayi laqwam kamar me bacci, a hankali ya juyo da fuskarta, ta bude idonta cikin nasa da sukayi laushi, be bari tayi magana ba ya hade bakinsu ya shiga aika mata Kiss me zare lakar jiki. Yafi minti goma yana kissing nata tareda kai hannunsa jikinta yana ya mutsata, yayi mamakin yanda ta saki jiki sosai tana maida masa da martani da alama itama tayi missing dinsa, mantawa yayi da wani ciwo da qafarsa takeyi suka gurji junansu kamar babu gobe seda komai ya lafa munafukar ta juya baya tana wani muzurai.
Haushin kanta ya kamata wai ya akayi ma ta wani sakar masa fuska har haka shi kuwa Khalil kallonta kawai yake yana murmushin rigimar Umaimah darunta se Allah. Haka ya doddogara yayi wanka yana jin yanda riqewar qafar ta sake haurawa har kusan qugunsa daya fito daga wankan kasa kwanciya yayi haka ya zauna yana shafa qafar, Umaimah data fito daga wanka itama ta kalle shi ganin yanda yake cije baki tace masa
"Sannu, ko na dakko Aboniki na shafa maka?"
"Da zaki iya akwai magani a dakina na shafawa ki dakko mun".
Seda ta saka kaya ta tafi Saman ta dakko masa maganin ta bude hanci tana shaqar wani qauri da bata san kona menene ba kamar dai na magani. Baki ta tabe ta dauki abinda ya kaita ta kashe fitilun daya bari a kunne ta sauka qasan. Da kanta ta shafa masa, sun dade a zaune seda yace mata ta kwanta kafin ta kwanta dukda na bacci takeyi ba tana ta kallon yanda yake juya kai yana cije baki sosai tausayinsa ya kamata duk ita ta janyo masa wannan Azabar ai kuwa gobe dole Safina ta kira Malam ya karya abin nan ba zata jure har kwana uku tana kallonsa cikin wannan Azabar ba.
Washe gari babu yabo babu fallasa ta ringa ayyukanta, ita ta shirya musu abin karyawa, ragowar Kazar ta sake dumama masa ta dafa shayi ta gasa masa buredi ita kuma ta dumama tuwo ta dama Koko dan yanzu su take jin dadin kari dashi. Falon qasan ma Sammani ta kira ya shiga ya share ya goge dan ba zata iya ba, tana ganin ma sedai ta nemo wata me aikin kawai tunda bata san sanda Ruqayya zata dawo ba. A gida Khalil ya wuni, tunda ya fita sallar Asuba ya dan tsaya bangaren Hajiya suka tattauna bayan sunyi waya dasu Baba Abu da suka dauko hanya se gurin bakwai ya koma bangarensu tun sannan kuma be sake fita ba seda zasu tafi Masallaci da Khalifa. Yaji dadin qafarsa harma ya manta da batun komawa Asibiti daya dawo daga Masallcin ma kuma gida ya sake zama saboda yau har yar hira sukeyi jifa jifa data kwanta bacci ne ya koma bangaren Hajiya se kusan qarfe biyar na Yamma su Baba Abu suka sauka Jalingo, sun yi waya dasu Khalil din ya sanar masa sun basu masauki yanzu sunce su huta, se zuwa dare zasu zauna da Waliyyan Humairan suyi abinda ya kawo su washe gari kuma suyi Asubanci su juyo Kano.
Qarfe takwas bayan ya dawo daga Sallar Isha suna zaune a falon Hajiya shida Jalilah data zo gidan babu dadewa wai tazo jin yanda akayi a Jalingo Hajiya natayi mata fadan ta cika Azarbabi idan bata fita daga sabgar maganar auran nan ba ranta ze baci ita dai tayi shiru bata ce komai ba.
Wayar Khalil dake ajiye kusa da ita ce ta dauki qara ta miqa masa tana cewa "Mansur na kira" ta bashi wayar seta miqe jin Hajiya na kiranta daga daki
Khalil dake cin tuwo ya miqa mata hannu bayan yace ta daga masa, ya kara wayar a kunnensa yana cewa
"Allah ya taimaki babban Yaya yau ka sauka daga fushin da kakeyi damu kenan ka kirani?"
"Malam ba surutu na kira muyi ba number Matarka zaka tura mun yanzu dukda I'm not in support of abinda ya faru amma Alqawari nayi kuma ina so na sauke dan na gaya maka in Allah ya yarda duk randa ka qara aure ni zan fara breaking ma Umaimah labarin nan maza ka turo mun kafin wani ya rigani"
Dariya Khalil yayi yace
"Toh ai duk mugun halinka ka bari lokacin auran yazo ba ka kunnamun wuta tun yanzu ba daman cikinta nake na samu Allah ya kashe zaka sake tadota, har sun gama maganar kenan wata nawa aka saka Yayanmu?"
"Wata ubanka aka saka dan iska kawai badai ka rantse seka saka qanwata a tashin hankali ba to kafin ta shigo kai zaka fara tarbar rabonka ni dallah turo mun number na kirata na gaya mata tun maganar da zafinta in yaso ta mutu aure dai an rigada an daura" Mansur ya sake fada se Khalil yace
"Aiko bazan baka number ta na kuma san babu inda zaka samu dan ta canza layi ba kowa yake dashi ba, auran wa kuma aka dauka naji kana magana?"
Tsaki Mansur yayi yace
"Ko ban gaya mata ba zata ji ai nasan kuma ni zan fara fado mata a rai ko haka aka tsaya burina ya cika kai kuma Allah baka ikon yin Adalci dan idan kuka cutar mun qanwar kaida ita duk se naci ubanku" yana gama fada be jira Khalil yayi magana ba ya kashe wayar dan daman a fusace yake.
Guda yaji an rangada saman kansa ya dago yana toshe kunnen Jalilah dake tsaye ta sake rangada wata gudar tana cewa
"Alqawarin Allah ya cika aure kuma ya dauru yan baqin ciki sedai su mutu Humairah da Khalil Allah yayi mun nema kuma an bamu" yanda kasan wata maroqiya haka take maganar.
"Tafiyar nan an fasa babu ita Anwar se wani lokacin idan Allah ya kaimu"
"Toh, amma dai shikenan, Allah ya nuna mana lokacin yasa hakan shine mafi Alkhairi" Anwar da yayi niyyar yin magana ya fasa saboda tunawa da yayi da dabi'ar Khalil din kuma yaji maganar na dawo masa kar yaje ya kunno wutar da ba zata kasu ba. Sallama sukayi akan se gobe sa hadu a office idan yaji dadin qafarsa yaci gaba da cin Naman yana satar Kallonta be wani ci da yawa ba ya rufe ya wanke hannunsa ya koma cikin falon.
"Har ka cinye" ta fada tana kallonsa seya zauna yana cewa
"Aa kadan naci na rigada naci abinci gurin Hajiya, ko ajiye mun ragowar da safe se na qarasa".
Shiru sukayi na dan lokaci ya canza tashar labarai yana kallo yaji ta sake cewa
"Ka fasa tafiya goben kenan"
"Eh wlh saboda ciwon qafar nan bazan iya dogon zama a mota ba, daman wani aiki muka samu zamuje dubawa amma na basu uzuri idan naji sauqi se muje ko kuma Anwar da su Patrick suje kawai" ya bata amsa yana duba wayarsa da yaji saqo ya shigo, Humaira ce ta aiko masa da wani zazzafan Text na soyayya ya karanta ya sake karantawa ya tabbatar wannan aikin Unaizatu ne seya maida mata da martanin
"I love you, karkiyi bacci zan kiraki seki fadamun kalaman nan da bakinki bana son su a rubuce"
"Ni kashe wayat zanyi ma yanzu, i love you more Gud nyt" ta maida masa itama yana karantawa kuwa ya shiga kiranta amma a kashe kamar yanda yace din ya daga kai yana murmushi ze dauki remote karaf suka hada ido da Umaimah da tun fara dannan wayar tasa take kallonsa.
Duburburcewa yayi dan gaba daya ya manta da tana zaune a gun, ya saba zama a falonsa shi kadai shiyasa yanzu ma yaji kamar a can yake se ya shiga borin kunya dason kare kansa daga balahirar ta yace
"Wani abu na gani a Twitter ya bani dariya"
"Uhm" tace masa tana maida kanta kan tata wayar da suke chat da Safina tana gaya mata yaci naman, daman Yajin Maganin barbade kazar tayi dashi dan karma a samu akasi yace baze dan gwala da yaji ba dan haka yake wani lokacin.
Khalil kuwa satar kallonta ya ringayi ganin bata kulashi ba yasa ya shiga WhatsApp, saqon Anwar ya gani yana tambayarsa da gaske an fasa zuwa nan yayi masa bayanin Su Baba Abu zasuje
"I thought that bana so nayi subutar baki ko Sarautar tana kusa na tada Bomb shiyasa nayi shiru" Anwar ya tsokanesa, seya kalli Umaimah data dukufa tana danna waya kafin ya maida masa da cewa
"Aiko da sedai na taho gidanka na kwana dan tana kusa kuma yai kaga abin Allah har girki tayi mun alamun ta fara sakkowa kenan kafin azo ayi fadan qarshe"
Emojin dariya Anwar ya turo masa da cewar
"Ai ko fadan qarshe a kashe Boss, Ni'ima na nan tunda na gaya mata zaka qara aure wai jira kawai take ranar tazo ta qagu taji ana bada labarin Abinda Umaimah tayi ta ringa cewa ai ta santa matar Abokin Mijinta ce"
"Ni'imar nan taka is Sick Anwar, ka gaya mata babu abinda ze faru se Alkhairi jikina yana bani hakan"
"I pray so Bro, ka ci gaba da Addu'a Allah ya kawo komai cikin sauqi, bari naje na lallaba Baby na tayi bacci Bye" Anwar ya maido masa da Amsa. Murmushi Khalil yayi ya kashe Datansa ya kalli inda Umaimah take yaga bata nan ta shiga daki kenan.
Dakyar yaja qafarsa yana cije baki zaman da yayi yasa ta qara yi masa nauyi ya isa qofar dakin nata ya kwankwasa.
"Come in" ta bashi amsa ya tura qofar da Sallama, tana kwance har taja bargo ta rufe jikinta saboda uban Ac data warewa dakin seya qarasa ya zauna gefen gadon yana cewa
"Idan bazan takura miki ba zan kwanta a nan qafata ta matsa mun bazan iya hawa sama ba"
"Mutum da gidansa se ya nemi izinin inda ze kwanta" ta bashi amsa tana gyra kwanciyarta, baya ta juya masa yayi murmushi kawai yana kallonta seya miqe dakyar ya wuce bandaki, alwala ya dauro ya dawo dakin, seda ya rage qarfin Ac kafin ya kwanta a gefenta yana sauke numfashi gaba daya qamshin turaren data saka ya dameshi ya nemi saka shi a wani hali. Kanta zuwa Bayanta ya shiga shafawa a hankali Umaimah dake jinsa tayi laqwam kamar me bacci, a hankali ya juyo da fuskarta, ta bude idonta cikin nasa da sukayi laushi, be bari tayi magana ba ya hade bakinsu ya shiga aika mata Kiss me zare lakar jiki. Yafi minti goma yana kissing nata tareda kai hannunsa jikinta yana ya mutsata, yayi mamakin yanda ta saki jiki sosai tana maida masa da martani da alama itama tayi missing dinsa, mantawa yayi da wani ciwo da qafarsa takeyi suka gurji junansu kamar babu gobe seda komai ya lafa munafukar ta juya baya tana wani muzurai.
Haushin kanta ya kamata wai ya akayi ma ta wani sakar masa fuska har haka shi kuwa Khalil kallonta kawai yake yana murmushin rigimar Umaimah darunta se Allah. Haka ya doddogara yayi wanka yana jin yanda riqewar qafar ta sake haurawa har kusan qugunsa daya fito daga wankan kasa kwanciya yayi haka ya zauna yana shafa qafar, Umaimah data fito daga wanka itama ta kalle shi ganin yanda yake cije baki tace masa
"Sannu, ko na dakko Aboniki na shafa maka?"
"Da zaki iya akwai magani a dakina na shafawa ki dakko mun".
Seda ta saka kaya ta tafi Saman ta dakko masa maganin ta bude hanci tana shaqar wani qauri da bata san kona menene ba kamar dai na magani. Baki ta tabe ta dauki abinda ya kaita ta kashe fitilun daya bari a kunne ta sauka qasan. Da kanta ta shafa masa, sun dade a zaune seda yace mata ta kwanta kafin ta kwanta dukda na bacci takeyi ba tana ta kallon yanda yake juya kai yana cije baki sosai tausayinsa ya kamata duk ita ta janyo masa wannan Azabar ai kuwa gobe dole Safina ta kira Malam ya karya abin nan ba zata jure har kwana uku tana kallonsa cikin wannan Azabar ba.
Washe gari babu yabo babu fallasa ta ringa ayyukanta, ita ta shirya musu abin karyawa, ragowar Kazar ta sake dumama masa ta dafa shayi ta gasa masa buredi ita kuma ta dumama tuwo ta dama Koko dan yanzu su take jin dadin kari dashi. Falon qasan ma Sammani ta kira ya shiga ya share ya goge dan ba zata iya ba, tana ganin ma sedai ta nemo wata me aikin kawai tunda bata san sanda Ruqayya zata dawo ba. A gida Khalil ya wuni, tunda ya fita sallar Asuba ya dan tsaya bangaren Hajiya suka tattauna bayan sunyi waya dasu Baba Abu da suka dauko hanya se gurin bakwai ya koma bangarensu tun sannan kuma be sake fita ba seda zasu tafi Masallaci da Khalifa. Yaji dadin qafarsa harma ya manta da batun komawa Asibiti daya dawo daga Masallcin ma kuma gida ya sake zama saboda yau har yar hira sukeyi jifa jifa data kwanta bacci ne ya koma bangaren Hajiya se kusan qarfe biyar na Yamma su Baba Abu suka sauka Jalingo, sun yi waya dasu Khalil din ya sanar masa sun basu masauki yanzu sunce su huta, se zuwa dare zasu zauna da Waliyyan Humairan suyi abinda ya kawo su washe gari kuma suyi Asubanci su juyo Kano.
Qarfe takwas bayan ya dawo daga Sallar Isha suna zaune a falon Hajiya shida Jalilah data zo gidan babu dadewa wai tazo jin yanda akayi a Jalingo Hajiya natayi mata fadan ta cika Azarbabi idan bata fita daga sabgar maganar auran nan ba ranta ze baci ita dai tayi shiru bata ce komai ba.
Wayar Khalil dake ajiye kusa da ita ce ta dauki qara ta miqa masa tana cewa "Mansur na kira" ta bashi wayar seta miqe jin Hajiya na kiranta daga daki
Khalil dake cin tuwo ya miqa mata hannu bayan yace ta daga masa, ya kara wayar a kunnensa yana cewa
"Allah ya taimaki babban Yaya yau ka sauka daga fushin da kakeyi damu kenan ka kirani?"
"Malam ba surutu na kira muyi ba number Matarka zaka tura mun yanzu dukda I'm not in support of abinda ya faru amma Alqawari nayi kuma ina so na sauke dan na gaya maka in Allah ya yarda duk randa ka qara aure ni zan fara breaking ma Umaimah labarin nan maza ka turo mun kafin wani ya rigani"
Dariya Khalil yayi yace
"Toh ai duk mugun halinka ka bari lokacin auran yazo ba ka kunnamun wuta tun yanzu ba daman cikinta nake na samu Allah ya kashe zaka sake tadota, har sun gama maganar kenan wata nawa aka saka Yayanmu?"
"Wata ubanka aka saka dan iska kawai badai ka rantse seka saka qanwata a tashin hankali ba to kafin ta shigo kai zaka fara tarbar rabonka ni dallah turo mun number na kirata na gaya mata tun maganar da zafinta in yaso ta mutu aure dai an rigada an daura" Mansur ya sake fada se Khalil yace
"Aiko bazan baka number ta na kuma san babu inda zaka samu dan ta canza layi ba kowa yake dashi ba, auran wa kuma aka dauka naji kana magana?"
Tsaki Mansur yayi yace
"Ko ban gaya mata ba zata ji ai nasan kuma ni zan fara fado mata a rai ko haka aka tsaya burina ya cika kai kuma Allah baka ikon yin Adalci dan idan kuka cutar mun qanwar kaida ita duk se naci ubanku" yana gama fada be jira Khalil yayi magana ba ya kashe wayar dan daman a fusace yake.
Guda yaji an rangada saman kansa ya dago yana toshe kunnen Jalilah dake tsaye ta sake rangada wata gudar tana cewa
"Alqawarin Allah ya cika aure kuma ya dauru yan baqin ciki sedai su mutu Humairah da Khalil Allah yayi mun nema kuma an bamu" yanda kasan wata maroqiya haka take maganar.