Sashe 204
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har Hajiya ta dawo daga rakiyar yar uwarta Khalil na zaune inda yake, so yakeyi yaje yaga Humaira hankalinsa gaba daya ya koma kanta tun jiya rabon dayaji saga gareta gashi yanzu ance Kuka takeyi.
"Babana kana zaune ka tashi ka hau Saman ka sameta mana tana nan a dakina" Hajiya data dawo ta fada seya miqe yana sunkuyar da kai kamar wanda yake gaban surukai ya haye saman. A hankali ya tura qofar dakin Hajiya ya tsaya yana kallonta tana zaune a qasa ta sunkuyar da kai Habiba na tsugunne gabanta da Kofi fuskarta ta nuna damuwa yana jinta tana ce mata
"Dan Allah ki dena kukan haka kisha ko madarar nan ce tunda kinqi cin Abinci, kona kira miki Yaya?"
Qarasa shiga cikin dakin yayi da sallama qasa qasa Habiba ta amsa da sauri tana cewa
"Yawwa ga Yayan ma yazo" ta miqe tsaye tana gaishe shi ya amsa mata idanunsa akan Humaira data sake curewa guri daya saboda shigowar tasa. Habiba ta sake shagwabe fuska tace
"Yaya taqi cin abinci tunda aka kawota take kuka duk su Anty sunyi sunyi taqi haquri kuma komai aka bata taqi taci"
"Jeki abinki zataci" ya fada yana qarasawa inda take se Habiban ta ajiye kofin hannunta akan Bedside drawer ta fita daga dakin ta kulle musu qofa. Seda yaga fitar Habiban kafin ya qarasa a hankali ya durqusa a gabant, a sanyaye ya kira sunanta bata dago ba haka bata fasa kukan da takeyi ba sema qara masa qarfi da tayi. Khalil ya saki murmushi kafin ya janyota gaba daya ta fada jikinsa yana cewa
"Na sani nayi laifi amma ayi mun afuwa kiyi shiru yanzu i promise an jima zan rarrasheki har se kince kin haqura kinji".
Banza ta masa tana ci gaba da shashsheqar kukanta, ya janye mayafin data rufe fuskarta dashi kyakykyawar farar fuskarta me cike da quruciya ta bayyana, se yaga ta qara masa kyau ya saka hannu yana share mata hawaye yace
"Kin gani har idonki sun kumbura ki bari haka mana kuma kar kanki yazo yana ciwo". Rarrashinta ya ringayi ganin bata da alamar barin kukan dan idan tayi shiru kome take tunawa se ta sake fashewa da kukan dan haka ya miqe bayan ya maida ita kan Gadon Hajiya ta zauna yace yana zuwa. A qaramin falon dake sama ya samu Hajiya a zaune ta zabga tagumi, ta kalleshi tace
"Ya dai Babana"
"Hajiya taqi dena kukan" ya fada a hankali kamar shima zeyi kukan abin nasa ma ya bawa Hajiya dariya har seda ta murmusa kafin tace
"Toh ai se ka dauketa ku tafi can kayita rarrashi aiki ya sameka, Amina tace an gyara gurin nata ko dazu sun shiga se kayi qoqari a maida mata da abubuwan da suka baci kafin yan uwanta su fara zuwa ganin guri dukda dai dazu dasu Maimuna sukaje dakkota sun sanarwa da Hauwan komai kuma Alhamdulillahi ta fahimta daman kuma nasan ba za'a samu matsala da ita ba, ina fatan kuma Allah ya tsayar da rigimar haka. Allah yayi muku Albarka ya baku zaman lafiya kai kuma ina sakeyi maka addu'a Allah ya qara maka juriya ya kuma baka ikon yin Adalci a tsakaninsu, kuje ta samu ta huta nima magani na zansha na kwanta kaina yana ciwo"
"Hajiya ki cire duk wata damuwa daga ranki kodan saboda lafiyarki in sha Allahu babu abinda ze sake faruwa" Khalil ya fada a sanyaye se Hajiya ta sakeyi murmushi tace
"In sha Allah, ka kira ku tafi kar kazar tata tayi sanyi" sosa kansa yayi shima yana murmushi ya juya ya koma dakin. Tana nan inda ya barta ta dai yi shiru tana jan ajiyar zuciya ya qarasa ya kamo hannunta yana cewa
"Let's go wife"
"Ina?" Ta tambayeshi cikin muryar kuka seya miqar da ita tsaye yana cewa
"Gidanmu mana ko a nan kike so ki zauna?"
"Ni gidan Mama zan koma" ta sake fada tana shirin fashe masa da kuka yayi saurin cewa
"Muje na mayar dake shikenan" ta daga masa kai. Hannunsa cikin nata suka fita, a falon qasa suka tarar da Hajiya da Habiba harda Khalifa daya dawo daga kai Hajiya Maimuna dan babu nisa sosai.
Har qasa Humairan ta tsugunna tana yiwa Hajiya sallama ta dagota jikinta tana saka mata albarka tareda sake maimaita mata tayi haquri, Habiba ta rakasu har bakin qofar shigowa part din tana cewa Khalil
"Yaya bata ci abinci bafa"
"Kin fada mun Habiba zataci kinji" ya mayar mata yana murmushi itama tayi murmushi, sosai Humairan ta shiga ranta dukda ta dan girmeta amma ta samu qawa.
Humaira dai binsa takeyi ganin suna shirin shiga wani gidan a maimakon mota ta tirje ya juya ya kalleta ta fara qifta ido alamar zata ci gaba da kukan tana cewa
"Kace gida zaka mayar dani kuma naga zamu shiga wani gurin"
"To ai key din mota zan dakko ko a qafa kike so muje?" Ya bata amsa seta girgiza masa kai yace
"Good girl" kafin ya bude musu qofar falon suka shiga. Daga bakin qofar ta tsaya tana zare ido, Khalil ya kalleta yanda takeyi ya bashi dariya kamar wadda aka sato, ciki yayi ya barta tana rarraba ido se gani tayi hasken falonya dauke ba shiri ta fasa ihu tayi ciki da gudu inda taga yabi, Khalil daya kashe hasken yayi saurin kunna fitilar wayarsa yabi bayanta gudun karta bige da wani abun ta fadi tana ganinsa ta rungumeshi jikinta na rawa tace
"An dauke wuta"
"Anya kodai bulb din ne suka mutu kinga waje can da haske" wajen ta kalla kafin ta kalleshi ya saketa yana cewa
"Jirani Bari na dakko key din" bata ko kulashi ba yana daga qafa ta bishi, a tare suka hau saman tana riqe da hannunsa data qi saki suna shiga ya mayar da qofar falon Saman ya kulle ya murza key kafin ya zare ya jefa a aljihunsa seta saki hannunsa da sauri ta shiga buga qafa tana yarfe hannu, Khalil kuwa kasa riqe dariya yayi ganin abinda takeyi din ya wuce daki yana cewa
"Yarinya keda gidab Mama ai se dai idan gaisheta kika je yi".
Kuka riris ta zauna tanayi Khalil daya fito ya bude baki yana kallonta a ransa yace
"Ikon Allah" a fili kuwa ya qarasa kusada ita ya zauna tareda cire hularsa ya dagata cak ya dorata akan cinyarsa, qoqarin sauka ta shigayi ya saka hannu daya ya riqe fuskarta ta gane me yake sonyi dan haka tayi saurin damtse bakinta amma ina seda ya samu nasarar shigar da harshen sa cikin bakinta ya shiga nanata mata karatun data rigada ta haddace dan tun ranar da aka daura musu aure yake biya mata. Seda tayi laqwas daman tuni Kuka ya kama gabansa kafin ya saketa yana sauke numfashi a hankali kamar yanda ta lafe a jikinsa itama taana sauke numfashin.
Wayar sa tayi qara ya janyota ganin Khalifa ne yake kira ya amsa, da "ok" ya amsa abinda ya ce masa kafin ya maida wayar ya ajiye ya kalleta fuskarsa dauke murmushi yace
"Bari na dakko Miki Akwatinki a qasa se nazo na baki Abinci sabuwar qawarki nata nanata mun baki ci komai ba" ya sauketa ya miqe se itama ta miqe jikinta duk yayi sanyi tabi bayansa suka sauka qasan tare. Akwatunanta saiti daya ya gani a nan cikin falon ya dauki babbar ta kama qaramar ciki zata dauka yayi saurin tareta yana cewa
"Aa ban sakaki ba karki wahalar mun da jikinki" ya wuce sama ita kuma ta tsaya tana qarewa falon kallo yayi mata kyau sosai a ranta tana tunanin falon waye nan na sane kenan ko. Seda ya gama hawa da akwatunan kafin ya shiga kitchen ya dakko Abubuwan da zasuyi amfani dashi ta karbi wasu ta riqe masa suka hau Saman.
Cikin tattali da kulawa ya ringa ciyar da ita wani hadadden dankali da Khalifan ya siyo bayan ya dumama mata a microwave dake nan saman kazar kadan taci, seda ya tabbatar ta qoshi kafin ya cika mata Cup da tatacciyar madara me sanyi yace tasha sannan ya fara ciyar da nasa cikin seda ya qoshi shima kafin suka tattara komai suka sake sauka qasa dashi a sannan ta shiga kitchen din tabi ko ina da kallo dukda komai a tsaftace yake amma ta gane ba nata bane tunda beyi kala da sabo ba kenan nan kitchen din matarsa ne gabata ya yanke ya fadi data tuna Umaimah da kashedinta se ta matsa kusa dashi qasa qasa muryar ta na nuna alamun tsorata tace
"Tana ina?"
"Wa?" Ya waiwaya ya kalleta se tayi farfar da ido tace
"Matarka mana"
"Yanzu saboda matar tawa duk kika firgice haka kina shirin yin kuka toh tana dakinta yanzu zamu shiga ku gaisa".
Gwalo ido tayi Khalil ya fashe da dariya kafin yaja hancinta yace
"Matsoraciya kwantar da hankalinki bata nan tana Asibiti CS za'ayi mata gobe"
"Wayyo daman ciki ne da ita Allah ya raba lafiya toh" ta fada cikin jimami a ranta tana mamakinsa, yanzu matarsa na Asibiti zata haihu amma shi yana gida da wata matar lallai Namiji. Seda ya kashe fitulun kitchen din dana falon gaba daya kafin suka haye saman tana sake ce masa
"Ita a qasa take zama kenan?"
"Eh duka qasa da nan saman nata ne, ke ga bangarenki can" ya nuna mata qofarta tana cewa
"Key din ne ya fadi se gobe da safe zan saka a yanko wani".
Seda suka shiga falon ya lura da yanda tayi kicin kicin da fuska kamar zata fasa ihu ya janyota jikinsa yana cewa
"Meya faru kuma?"
Se hawaye sha ta shiga cewa
"Shine zaka kawoni dakin matarka da kasan ka yarda key din da ba seka bari se gobe idan an bude qofar a kawoni ba kawai dan ka nuna mun iyakata zaka kawoni dakin wata"
"Babana kana zaune ka tashi ka hau Saman ka sameta mana tana nan a dakina" Hajiya data dawo ta fada seya miqe yana sunkuyar da kai kamar wanda yake gaban surukai ya haye saman. A hankali ya tura qofar dakin Hajiya ya tsaya yana kallonta tana zaune a qasa ta sunkuyar da kai Habiba na tsugunne gabanta da Kofi fuskarta ta nuna damuwa yana jinta tana ce mata
"Dan Allah ki dena kukan haka kisha ko madarar nan ce tunda kinqi cin Abinci, kona kira miki Yaya?"
Qarasa shiga cikin dakin yayi da sallama qasa qasa Habiba ta amsa da sauri tana cewa
"Yawwa ga Yayan ma yazo" ta miqe tsaye tana gaishe shi ya amsa mata idanunsa akan Humaira data sake curewa guri daya saboda shigowar tasa. Habiba ta sake shagwabe fuska tace
"Yaya taqi cin abinci tunda aka kawota take kuka duk su Anty sunyi sunyi taqi haquri kuma komai aka bata taqi taci"
"Jeki abinki zataci" ya fada yana qarasawa inda take se Habiban ta ajiye kofin hannunta akan Bedside drawer ta fita daga dakin ta kulle musu qofa. Seda yaga fitar Habiban kafin ya qarasa a hankali ya durqusa a gabant, a sanyaye ya kira sunanta bata dago ba haka bata fasa kukan da takeyi ba sema qara masa qarfi da tayi. Khalil ya saki murmushi kafin ya janyota gaba daya ta fada jikinsa yana cewa
"Na sani nayi laifi amma ayi mun afuwa kiyi shiru yanzu i promise an jima zan rarrasheki har se kince kin haqura kinji".
Banza ta masa tana ci gaba da shashsheqar kukanta, ya janye mayafin data rufe fuskarta dashi kyakykyawar farar fuskarta me cike da quruciya ta bayyana, se yaga ta qara masa kyau ya saka hannu yana share mata hawaye yace
"Kin gani har idonki sun kumbura ki bari haka mana kuma kar kanki yazo yana ciwo". Rarrashinta ya ringayi ganin bata da alamar barin kukan dan idan tayi shiru kome take tunawa se ta sake fashewa da kukan dan haka ya miqe bayan ya maida ita kan Gadon Hajiya ta zauna yace yana zuwa. A qaramin falon dake sama ya samu Hajiya a zaune ta zabga tagumi, ta kalleshi tace
"Ya dai Babana"
"Hajiya taqi dena kukan" ya fada a hankali kamar shima zeyi kukan abin nasa ma ya bawa Hajiya dariya har seda ta murmusa kafin tace
"Toh ai se ka dauketa ku tafi can kayita rarrashi aiki ya sameka, Amina tace an gyara gurin nata ko dazu sun shiga se kayi qoqari a maida mata da abubuwan da suka baci kafin yan uwanta su fara zuwa ganin guri dukda dai dazu dasu Maimuna sukaje dakkota sun sanarwa da Hauwan komai kuma Alhamdulillahi ta fahimta daman kuma nasan ba za'a samu matsala da ita ba, ina fatan kuma Allah ya tsayar da rigimar haka. Allah yayi muku Albarka ya baku zaman lafiya kai kuma ina sakeyi maka addu'a Allah ya qara maka juriya ya kuma baka ikon yin Adalci a tsakaninsu, kuje ta samu ta huta nima magani na zansha na kwanta kaina yana ciwo"
"Hajiya ki cire duk wata damuwa daga ranki kodan saboda lafiyarki in sha Allahu babu abinda ze sake faruwa" Khalil ya fada a sanyaye se Hajiya ta sakeyi murmushi tace
"In sha Allah, ka kira ku tafi kar kazar tata tayi sanyi" sosa kansa yayi shima yana murmushi ya juya ya koma dakin. Tana nan inda ya barta ta dai yi shiru tana jan ajiyar zuciya ya qarasa ya kamo hannunta yana cewa
"Let's go wife"
"Ina?" Ta tambayeshi cikin muryar kuka seya miqar da ita tsaye yana cewa
"Gidanmu mana ko a nan kike so ki zauna?"
"Ni gidan Mama zan koma" ta sake fada tana shirin fashe masa da kuka yayi saurin cewa
"Muje na mayar dake shikenan" ta daga masa kai. Hannunsa cikin nata suka fita, a falon qasa suka tarar da Hajiya da Habiba harda Khalifa daya dawo daga kai Hajiya Maimuna dan babu nisa sosai.
Har qasa Humairan ta tsugunna tana yiwa Hajiya sallama ta dagota jikinta tana saka mata albarka tareda sake maimaita mata tayi haquri, Habiba ta rakasu har bakin qofar shigowa part din tana cewa Khalil
"Yaya bata ci abinci bafa"
"Kin fada mun Habiba zataci kinji" ya mayar mata yana murmushi itama tayi murmushi, sosai Humairan ta shiga ranta dukda ta dan girmeta amma ta samu qawa.
Humaira dai binsa takeyi ganin suna shirin shiga wani gidan a maimakon mota ta tirje ya juya ya kalleta ta fara qifta ido alamar zata ci gaba da kukan tana cewa
"Kace gida zaka mayar dani kuma naga zamu shiga wani gurin"
"To ai key din mota zan dakko ko a qafa kike so muje?" Ya bata amsa seta girgiza masa kai yace
"Good girl" kafin ya bude musu qofar falon suka shiga. Daga bakin qofar ta tsaya tana zare ido, Khalil ya kalleta yanda takeyi ya bashi dariya kamar wadda aka sato, ciki yayi ya barta tana rarraba ido se gani tayi hasken falonya dauke ba shiri ta fasa ihu tayi ciki da gudu inda taga yabi, Khalil daya kashe hasken yayi saurin kunna fitilar wayarsa yabi bayanta gudun karta bige da wani abun ta fadi tana ganinsa ta rungumeshi jikinta na rawa tace
"An dauke wuta"
"Anya kodai bulb din ne suka mutu kinga waje can da haske" wajen ta kalla kafin ta kalleshi ya saketa yana cewa
"Jirani Bari na dakko key din" bata ko kulashi ba yana daga qafa ta bishi, a tare suka hau saman tana riqe da hannunsa data qi saki suna shiga ya mayar da qofar falon Saman ya kulle ya murza key kafin ya zare ya jefa a aljihunsa seta saki hannunsa da sauri ta shiga buga qafa tana yarfe hannu, Khalil kuwa kasa riqe dariya yayi ganin abinda takeyi din ya wuce daki yana cewa
"Yarinya keda gidab Mama ai se dai idan gaisheta kika je yi".
Kuka riris ta zauna tanayi Khalil daya fito ya bude baki yana kallonta a ransa yace
"Ikon Allah" a fili kuwa ya qarasa kusada ita ya zauna tareda cire hularsa ya dagata cak ya dorata akan cinyarsa, qoqarin sauka ta shigayi ya saka hannu daya ya riqe fuskarta ta gane me yake sonyi dan haka tayi saurin damtse bakinta amma ina seda ya samu nasarar shigar da harshen sa cikin bakinta ya shiga nanata mata karatun data rigada ta haddace dan tun ranar da aka daura musu aure yake biya mata. Seda tayi laqwas daman tuni Kuka ya kama gabansa kafin ya saketa yana sauke numfashi a hankali kamar yanda ta lafe a jikinsa itama taana sauke numfashin.
Wayar sa tayi qara ya janyota ganin Khalifa ne yake kira ya amsa, da "ok" ya amsa abinda ya ce masa kafin ya maida wayar ya ajiye ya kalleta fuskarsa dauke murmushi yace
"Bari na dakko Miki Akwatinki a qasa se nazo na baki Abinci sabuwar qawarki nata nanata mun baki ci komai ba" ya sauketa ya miqe se itama ta miqe jikinta duk yayi sanyi tabi bayansa suka sauka qasan tare. Akwatunanta saiti daya ya gani a nan cikin falon ya dauki babbar ta kama qaramar ciki zata dauka yayi saurin tareta yana cewa
"Aa ban sakaki ba karki wahalar mun da jikinki" ya wuce sama ita kuma ta tsaya tana qarewa falon kallo yayi mata kyau sosai a ranta tana tunanin falon waye nan na sane kenan ko. Seda ya gama hawa da akwatunan kafin ya shiga kitchen ya dakko Abubuwan da zasuyi amfani dashi ta karbi wasu ta riqe masa suka hau Saman.
Cikin tattali da kulawa ya ringa ciyar da ita wani hadadden dankali da Khalifan ya siyo bayan ya dumama mata a microwave dake nan saman kazar kadan taci, seda ya tabbatar ta qoshi kafin ya cika mata Cup da tatacciyar madara me sanyi yace tasha sannan ya fara ciyar da nasa cikin seda ya qoshi shima kafin suka tattara komai suka sake sauka qasa dashi a sannan ta shiga kitchen din tabi ko ina da kallo dukda komai a tsaftace yake amma ta gane ba nata bane tunda beyi kala da sabo ba kenan nan kitchen din matarsa ne gabata ya yanke ya fadi data tuna Umaimah da kashedinta se ta matsa kusa dashi qasa qasa muryar ta na nuna alamun tsorata tace
"Tana ina?"
"Wa?" Ya waiwaya ya kalleta se tayi farfar da ido tace
"Matarka mana"
"Yanzu saboda matar tawa duk kika firgice haka kina shirin yin kuka toh tana dakinta yanzu zamu shiga ku gaisa".
Gwalo ido tayi Khalil ya fashe da dariya kafin yaja hancinta yace
"Matsoraciya kwantar da hankalinki bata nan tana Asibiti CS za'ayi mata gobe"
"Wayyo daman ciki ne da ita Allah ya raba lafiya toh" ta fada cikin jimami a ranta tana mamakinsa, yanzu matarsa na Asibiti zata haihu amma shi yana gida da wata matar lallai Namiji. Seda ya kashe fitulun kitchen din dana falon gaba daya kafin suka haye saman tana sake ce masa
"Ita a qasa take zama kenan?"
"Eh duka qasa da nan saman nata ne, ke ga bangarenki can" ya nuna mata qofarta tana cewa
"Key din ne ya fadi se gobe da safe zan saka a yanko wani".
Seda suka shiga falon ya lura da yanda tayi kicin kicin da fuska kamar zata fasa ihu ya janyota jikinsa yana cewa
"Meya faru kuma?"
Se hawaye sha ta shiga cewa
"Shine zaka kawoni dakin matarka da kasan ka yarda key din da ba seka bari se gobe idan an bude qofar a kawoni ba kawai dan ka nuna mun iyakata zaka kawoni dakin wata"