Sashe 136
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Sunana Fareeda Abdallah, a kaduna nake da zama. Amma muna aikawa da magungunanmu ko ina tsakanin Nigeria da Nijer, sai dai duk inda mai siyan magani take ita za ta biya kuɗin mota ko na delivery zuwa gidanta. A tuntuɓeni ta whatsapp ko a kira ni akan lambobin wayata 07039080978, 09077591726. Sai kun zo😍😍😍*
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 52
Tunawa yayi da furucin Dr na ya kirata ya bata haquri ko kuma ya manta da zancen kwangilar, wayarsa ya dauko takaici fal ransa, shi ta hada masa bala'i sannan kuma ya kirata ya bata haquri amma shikenan na dan lokaci ne. Kamar tana jira ringing daya ta daga wayar cikin shagwababbiyar muryarta da sam bata burgeshi tace
"Yanzu kawai dan na kiraka shine zaka rufeni da fada kana zagina akan matarka ko?"
"Oh daman cewa Dady kikayi na zageki kenan, yaushe na zageki? Ke baki ga abinda kika mun ba? Sau nawa zan gaya miki ki dena kirana qasa da qarfe goma na safe in dai bani ne na kiraki ba?
Kuma sannan duk abinda ya faru tsakanin mu se kin gayawa Dady a haka zamuyi aure duk abinda ya faru ki kwasa ki gaya masa ya kira waya ya ringa fada to wallahi ko ki canza ko kuma mu samu sabani dake haba da wanne mutum zeji" Khalil ya fada cikin bacin rai be idasha shaqar numfashi ba Zahran ta fasa masa kuka kamar wata qaramar yarinya. Takaici yazo masa wuya amma ya daure ya sassauta muryarsa yace
"To yanzu kuma me akayi da zaki yiwa mutane kuka uhm? Shikenan bazakiyi ba daidai ba a miki magana se kuka se tashin hankali?"
"To meyasa zaka ringayi mun ihu bayan ko Dady lallabani yake yi? Wallahi sena gaya masa ba yace zaka kira ka bani haquri ba shine kake mun ihu da fada se na gaya masa?" Ta fada cikin zallar sakarci, Khalil ya bawa kansa haquri kafin ya ce
"Toh kiyi haquri shikenan base kin sake gaya masa ba".
Banza tayi masa taci gaba da gunsheqar kuka, yana jiyo muryar mahaifiyarta na cewa ta tashi ta bar kusa da ita kafin ta maketa tunda ita bata da hankali da yaga dai bazata bar kukan ba dole ya sassauto ya shiga rarrashinta yana gaya mata kalamai masu dadi har ya samu ta haqura. Besan lokaci yaja ba seda suka kashe wayar ya duba Agogo tara harda rabi tayi yana tsaye a gefen hanya. Gabansa ya fadi sanda yaga Missed calk din Umaimah dan wallahi beji ma sanda ta kirashi ba yana fama da waccen psycho din yarinyar. Kiranta yayi back wayar ta qaraci ringing bata daga ba haka ya haqura ya cigaba da tafiya ya tabbatar dai yau kam Allah kadai ze fidda shi. A office dinma be iya yin wani abin kirki ba. Ga Zahra ta ishe shi da waya yaqi dagawa cibi ya zama qari haka dole yake biye mata qarshe tace ya biya idan ya tashi tana son ganinsa ba yadda ya iya haka yaje gashi sunyi da Umaimah idan ya taso ze biya ya dakkota su wuce gida dukda bashi da tabbacin bayan abinda ya faru zata jirashin amma haka ya wuce bayan ya gama da Zahran.
Yasha mamaki daya kirata ta dauka ya sanar da ita yana waje se gata ta fito fuskarta a washe suna sallama da Nuratu da itama zata wuce gida suka gaisa ta shige motarta kafin Umaiman ta bude bayan mota ta shiga fuskarta a dinke kai baka ce ita ta fito yanzu tana dariya ba. Bibi ce ta shiga gaba ya tada mota suka dauki hanya ta Rear mirror yake kallonta hankalinta naka wayarta da take dannawa har suka isa gida ya kasa ce mata komai dan gaba daya ya tsorata da yanayin fuskarta. Har suka kwanta batace masa qala ba abinda ya qara dugunzuma hankalinsa kenan dan shirun Umaimah ba Alkhairi bane, be manta yanda suka qare da Hadiza ba, bata yi masa magana ba seda komai ya lalace kafin ya tsinci zancen yanzun ma yana tsoron ta sake kwata wani da ze jefa su a bala'i gaba dayansu.
UMAIMAH
Yanda ta shiga gidan ya saka Maman Asad da Baba Talatu dake zuwar mata duk haihuwa suka juya suna kallonta. Mamakin zuwanta da sassafen ya kamasu ga yanayin data shigo da ko ba'a fada ba sun san ba lafiya ba. Dakin Maman Asad ta wuce kao tsaye Bibi ko daman kujera ta haye ta kwanta abinta dan bacci be isheta ba Baba Talatu ta kalli Maman Asad tace
"Hajiyayye leqata mana kiji lafiya irin wannan Asubanci bayan fitar safe ba halin uwar dakina bace".
A dakin ta sameta zaune a gefen gado ta zubawa qofar shigowa ido da gani tayi zurfi a tunani har Maman Asad din ta qarasa ta zauna gefenta tareda dafata sanann ta farga.
"Lafiya Umaimah, me ya faru?" Ta fada tana kallonta kamar tana jira kuwa ta fada jikin Hajiyayyen tareda fashe da kuka seda tayi me isarta gaba daya ta dagawa Hajiyayyen hankali kafin ta fara magana tana cewa
"Wallahi ko ni ko Khalil, se ya gayamun da shegiyar da yake cin amanata".
Numfashi Maman Asad ta sauke a zuciyarta tana yiwa Allah godiya da abin tsaya iya haka, yanda ta ganta da sassafen nan ga kuka ta dauka auren ne ya samu matsala ashe iskokan kishin ne suka motsa dan haka ta gyara zama tace
"Me kuma Khalil yayi keda bakya rabo da abin magana?"
"Wata yar iska ya samu take dauke masa hankali, daman na dade ina lura da ya canza taku se ya ringa wasu abubuwa irin na munafukai. Kwanaki na dauki wayarsa haka ya fitittike ya ringa mun fada akan me zan masa bincike saboda yasan akwai abinda yake aikatawa a boye da baya so na sani shiyasa se gashi yau Allah ya tona masa Asiri yanzun nan a qofar gidan nan mun tsaya Karuwar tasa ta kirashi" Umaimah ta fada cikin zafin rai. Harara Maman Asad ta balla mata kafin tace
"Umaimah ki iya bakinki, wai ke baki da hankali da zaki ringa danganta mijinki da karuwa ko kuwa an ce miki babu wata alaqa tsakanin mace da namiji seta iskanci? Wallahi samun Khalil din kikayi a bagas har yake takatsantsan da fushinki idan wani ne tunda ya fuskanci ke mahaukaciya ce bakisan abinda yake damunki ba ai sabgogin gabansa ze ci gaba dayi qarqari idan kin sani kiyi haukanki ki gama hakan bashi ze hana ya cigaba da yawon kula yammatan shi ba.
Kuma bari kiji, tun wuri idan zaki hada hankalinki guri daya ki kama kanki kiyi tun kafin ya kawo miki wata tazo taga ballagazancin da kikeyi da sunan kishi ta rainaki dan kinsan qarya kike kice ke kadai zaki zauna a gidan nan ko beyi niyya ba na tabbata se yan uwansa sun saka shi ya qara aure dan in kika cire Hajiyarsa a yanzu dai kaf cikinsu babu wadda takr ganinki da gashi kin zubar da qimarki a gabansu kuma ko mune matar dan uwanmu tayi abinda kikayi a baya wallahi baza'a rufe case din nan ba se mun masa aure muga qarshen tsiya, dan haka in zaki ajiye kishi ki fuskanci gaskiya kiyi dan na tabbatar da lokacin zuwan wata ne yayi ba kuma ki isa ki hana ba dan baki da hujjar hakan".
Kallonta kawai Umaimah take har ta kai aya yanda kasan ta kwashe ta da mari, yanzu ta kawo mata matsalarta a maimakon ta tayata jin haushi seta goyi bayansa harda qarin wani jafa'in take janyo mata to kuwa ya qare akanta, kishiya ba sedai ta ganta a gidanta ganin idonta wallahi.
Tsaki kawai tayi ta miqe ta bar MamanAsad da baki a bude tana kallonta, bandaki ta shiga ta wanko fuskarta haushin kanta ma data tsaya yiwa Hajiyayye bayani ya kamata bayan tasan tafi qaunar Khalil akan ta. Palour ta wuce dan neman abinda zata sakawa cikinta ta gaida Baba Talatu sama sama bata ko kula tsokanar da take mata ba ta shige musu kitchen a ranta tana ayyana wannan Yaqin tane ita zata kwatarwa kanta yanci, yanda ta rabashi da Hadiza ba tareda shawarar kowa ba wannan karon ma haka zatayi amma kafin ta san abinyi dole ta fara gano ita yarinyar a ina take da duk abinda ya kamata ace ta sani akanta.
Haka ta qarasa wuni a gidan bayan ta taushi zuciyarta ta saki ranta sukayi ta hidima bayan zuwan Nuratu, Anty Hafsa da Anty Zee.
Taga missed calls dinsa har biyu ta share saboda idan ta daga wayar danniyar datayi wa zuciyarta zata wargatse ta kokora masa Ashar shiyasa ta barshi dan bata san kiran me yake mata bama. Da yazo daukar su ma seda tayi da gaske ta iya shiga motar shiyasa ta zauna a baya har sukaje gida kuma bata ce masa komai ba.
Seda suka kwashe kwana uku tafi ka mutu bata ce masa ba, zatayi duk abinda ta saba a gidan girki da sauran ayyuka ammafa bazata shiga sabgarsa ba abin ya damu Khalil matuqa gashi baya so yayi mata wata doguwar magana ya kunnota Addu'a yakeyi abinda ya saka gaba ya kammalu kafin ta fashe, zuwa sannan yana da bakin yi mata bayanin komai game da Zahran amma yanzu kam akan tsini yake. Ita kanta Zahra da Mahaifinta sun taso shi a gaba akan ya turo magabatansa su shiga magana kullum cikin basu uzuri Yakeyi yana kuma Addu'ar Allah ya tabbatar da aikin nan su rabu kowa ya kama gabansa.
Gaba daya shima ya shiga rashin walwala, haka idan ya fita aiki ze kirata yanda ya saba dukda bazata dauka ba har lokacin dawowa ya rage ya zamana yana dawowa gidan da wuri kuma idan ya dawo sallah kadai take qara fitar dashi sedai ya zauna zuru a palour ko yayi ta yan tabe tabe a Laptop dan wayar kanta baya so ya dauka balle tayi zargin Chatting yake da wata.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 52
Tunawa yayi da furucin Dr na ya kirata ya bata haquri ko kuma ya manta da zancen kwangilar, wayarsa ya dauko takaici fal ransa, shi ta hada masa bala'i sannan kuma ya kirata ya bata haquri amma shikenan na dan lokaci ne. Kamar tana jira ringing daya ta daga wayar cikin shagwababbiyar muryarta da sam bata burgeshi tace
"Yanzu kawai dan na kiraka shine zaka rufeni da fada kana zagina akan matarka ko?"
"Oh daman cewa Dady kikayi na zageki kenan, yaushe na zageki? Ke baki ga abinda kika mun ba? Sau nawa zan gaya miki ki dena kirana qasa da qarfe goma na safe in dai bani ne na kiraki ba?
Kuma sannan duk abinda ya faru tsakanin mu se kin gayawa Dady a haka zamuyi aure duk abinda ya faru ki kwasa ki gaya masa ya kira waya ya ringa fada to wallahi ko ki canza ko kuma mu samu sabani dake haba da wanne mutum zeji" Khalil ya fada cikin bacin rai be idasha shaqar numfashi ba Zahran ta fasa masa kuka kamar wata qaramar yarinya. Takaici yazo masa wuya amma ya daure ya sassauta muryarsa yace
"To yanzu kuma me akayi da zaki yiwa mutane kuka uhm? Shikenan bazakiyi ba daidai ba a miki magana se kuka se tashin hankali?"
"To meyasa zaka ringayi mun ihu bayan ko Dady lallabani yake yi? Wallahi sena gaya masa ba yace zaka kira ka bani haquri ba shine kake mun ihu da fada se na gaya masa?" Ta fada cikin zallar sakarci, Khalil ya bawa kansa haquri kafin ya ce
"Toh kiyi haquri shikenan base kin sake gaya masa ba".
Banza tayi masa taci gaba da gunsheqar kuka, yana jiyo muryar mahaifiyarta na cewa ta tashi ta bar kusa da ita kafin ta maketa tunda ita bata da hankali da yaga dai bazata bar kukan ba dole ya sassauto ya shiga rarrashinta yana gaya mata kalamai masu dadi har ya samu ta haqura. Besan lokaci yaja ba seda suka kashe wayar ya duba Agogo tara harda rabi tayi yana tsaye a gefen hanya. Gabansa ya fadi sanda yaga Missed calk din Umaimah dan wallahi beji ma sanda ta kirashi ba yana fama da waccen psycho din yarinyar. Kiranta yayi back wayar ta qaraci ringing bata daga ba haka ya haqura ya cigaba da tafiya ya tabbatar dai yau kam Allah kadai ze fidda shi. A office dinma be iya yin wani abin kirki ba. Ga Zahra ta ishe shi da waya yaqi dagawa cibi ya zama qari haka dole yake biye mata qarshe tace ya biya idan ya tashi tana son ganinsa ba yadda ya iya haka yaje gashi sunyi da Umaimah idan ya taso ze biya ya dakkota su wuce gida dukda bashi da tabbacin bayan abinda ya faru zata jirashin amma haka ya wuce bayan ya gama da Zahran.
Yasha mamaki daya kirata ta dauka ya sanar da ita yana waje se gata ta fito fuskarta a washe suna sallama da Nuratu da itama zata wuce gida suka gaisa ta shige motarta kafin Umaiman ta bude bayan mota ta shiga fuskarta a dinke kai baka ce ita ta fito yanzu tana dariya ba. Bibi ce ta shiga gaba ya tada mota suka dauki hanya ta Rear mirror yake kallonta hankalinta naka wayarta da take dannawa har suka isa gida ya kasa ce mata komai dan gaba daya ya tsorata da yanayin fuskarta. Har suka kwanta batace masa qala ba abinda ya qara dugunzuma hankalinsa kenan dan shirun Umaimah ba Alkhairi bane, be manta yanda suka qare da Hadiza ba, bata yi masa magana ba seda komai ya lalace kafin ya tsinci zancen yanzun ma yana tsoron ta sake kwata wani da ze jefa su a bala'i gaba dayansu.
UMAIMAH
Yanda ta shiga gidan ya saka Maman Asad da Baba Talatu dake zuwar mata duk haihuwa suka juya suna kallonta. Mamakin zuwanta da sassafen ya kamasu ga yanayin data shigo da ko ba'a fada ba sun san ba lafiya ba. Dakin Maman Asad ta wuce kao tsaye Bibi ko daman kujera ta haye ta kwanta abinta dan bacci be isheta ba Baba Talatu ta kalli Maman Asad tace
"Hajiyayye leqata mana kiji lafiya irin wannan Asubanci bayan fitar safe ba halin uwar dakina bace".
A dakin ta sameta zaune a gefen gado ta zubawa qofar shigowa ido da gani tayi zurfi a tunani har Maman Asad din ta qarasa ta zauna gefenta tareda dafata sanann ta farga.
"Lafiya Umaimah, me ya faru?" Ta fada tana kallonta kamar tana jira kuwa ta fada jikin Hajiyayyen tareda fashe da kuka seda tayi me isarta gaba daya ta dagawa Hajiyayyen hankali kafin ta fara magana tana cewa
"Wallahi ko ni ko Khalil, se ya gayamun da shegiyar da yake cin amanata".
Numfashi Maman Asad ta sauke a zuciyarta tana yiwa Allah godiya da abin tsaya iya haka, yanda ta ganta da sassafen nan ga kuka ta dauka auren ne ya samu matsala ashe iskokan kishin ne suka motsa dan haka ta gyara zama tace
"Me kuma Khalil yayi keda bakya rabo da abin magana?"
"Wata yar iska ya samu take dauke masa hankali, daman na dade ina lura da ya canza taku se ya ringa wasu abubuwa irin na munafukai. Kwanaki na dauki wayarsa haka ya fitittike ya ringa mun fada akan me zan masa bincike saboda yasan akwai abinda yake aikatawa a boye da baya so na sani shiyasa se gashi yau Allah ya tona masa Asiri yanzun nan a qofar gidan nan mun tsaya Karuwar tasa ta kirashi" Umaimah ta fada cikin zafin rai. Harara Maman Asad ta balla mata kafin tace
"Umaimah ki iya bakinki, wai ke baki da hankali da zaki ringa danganta mijinki da karuwa ko kuwa an ce miki babu wata alaqa tsakanin mace da namiji seta iskanci? Wallahi samun Khalil din kikayi a bagas har yake takatsantsan da fushinki idan wani ne tunda ya fuskanci ke mahaukaciya ce bakisan abinda yake damunki ba ai sabgogin gabansa ze ci gaba dayi qarqari idan kin sani kiyi haukanki ki gama hakan bashi ze hana ya cigaba da yawon kula yammatan shi ba.
Kuma bari kiji, tun wuri idan zaki hada hankalinki guri daya ki kama kanki kiyi tun kafin ya kawo miki wata tazo taga ballagazancin da kikeyi da sunan kishi ta rainaki dan kinsan qarya kike kice ke kadai zaki zauna a gidan nan ko beyi niyya ba na tabbata se yan uwansa sun saka shi ya qara aure dan in kika cire Hajiyarsa a yanzu dai kaf cikinsu babu wadda takr ganinki da gashi kin zubar da qimarki a gabansu kuma ko mune matar dan uwanmu tayi abinda kikayi a baya wallahi baza'a rufe case din nan ba se mun masa aure muga qarshen tsiya, dan haka in zaki ajiye kishi ki fuskanci gaskiya kiyi dan na tabbatar da lokacin zuwan wata ne yayi ba kuma ki isa ki hana ba dan baki da hujjar hakan".
Kallonta kawai Umaimah take har ta kai aya yanda kasan ta kwashe ta da mari, yanzu ta kawo mata matsalarta a maimakon ta tayata jin haushi seta goyi bayansa harda qarin wani jafa'in take janyo mata to kuwa ya qare akanta, kishiya ba sedai ta ganta a gidanta ganin idonta wallahi.
Tsaki kawai tayi ta miqe ta bar MamanAsad da baki a bude tana kallonta, bandaki ta shiga ta wanko fuskarta haushin kanta ma data tsaya yiwa Hajiyayye bayani ya kamata bayan tasan tafi qaunar Khalil akan ta. Palour ta wuce dan neman abinda zata sakawa cikinta ta gaida Baba Talatu sama sama bata ko kula tsokanar da take mata ba ta shige musu kitchen a ranta tana ayyana wannan Yaqin tane ita zata kwatarwa kanta yanci, yanda ta rabashi da Hadiza ba tareda shawarar kowa ba wannan karon ma haka zatayi amma kafin ta san abinyi dole ta fara gano ita yarinyar a ina take da duk abinda ya kamata ace ta sani akanta.
Haka ta qarasa wuni a gidan bayan ta taushi zuciyarta ta saki ranta sukayi ta hidima bayan zuwan Nuratu, Anty Hafsa da Anty Zee.
Taga missed calls dinsa har biyu ta share saboda idan ta daga wayar danniyar datayi wa zuciyarta zata wargatse ta kokora masa Ashar shiyasa ta barshi dan bata san kiran me yake mata bama. Da yazo daukar su ma seda tayi da gaske ta iya shiga motar shiyasa ta zauna a baya har sukaje gida kuma bata ce masa komai ba.
Seda suka kwashe kwana uku tafi ka mutu bata ce masa ba, zatayi duk abinda ta saba a gidan girki da sauran ayyuka ammafa bazata shiga sabgarsa ba abin ya damu Khalil matuqa gashi baya so yayi mata wata doguwar magana ya kunnota Addu'a yakeyi abinda ya saka gaba ya kammalu kafin ta fashe, zuwa sannan yana da bakin yi mata bayanin komai game da Zahran amma yanzu kam akan tsini yake. Ita kanta Zahra da Mahaifinta sun taso shi a gaba akan ya turo magabatansa su shiga magana kullum cikin basu uzuri Yakeyi yana kuma Addu'ar Allah ya tabbatar da aikin nan su rabu kowa ya kama gabansa.
Gaba daya shima ya shiga rashin walwala, haka idan ya fita aiki ze kirata yanda ya saba dukda bazata dauka ba har lokacin dawowa ya rage ya zamana yana dawowa gidan da wuri kuma idan ya dawo sallah kadai take qara fitar dashi sedai ya zauna zuru a palour ko yayi ta yan tabe tabe a Laptop dan wayar kanta baya so ya dauka balle tayi zargin Chatting yake da wata.