Sashe 18
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Miqewa tayi, dakyar take daga qafarta Nuratu tayi qoqarin kama mata hijab amma ina tuni ta fincike tayi waje gaba daya yan dakin suka rakata da ido.
"Ko jikin nata ne ya motsa?" Khalil ya fada yana kallon Nuratu, ta gyada kai dakyar tana hadiyar yawu dan ita tasan ba jiki bane sedai idan Baqin HALIN KISHIN nata ne ya motsa, Khalil ya fita da sauri yana cewa "Bari na dubata, idan jikin ne se mu ga likita a nan ya sake dubata" yayi waje da sauri ya bi bayanta.
PROMO
PROMO
PROMO
BEFORE 4K NOW 2500
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA 👇🏻
08162859027
AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA
INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO
SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 9
Hangota Khalil yayi ta doshi hanyar waje yabi bayanta da sauri kamarta sani ta qarawa tafiyarta sauri, cikin sassarfa ya bita ganin har ta kusa isa gate din Asibitin ya daga murya yana kiran sunanta amma bata juya ba jefa qafunta kawai take tana tafiya, ji take ina ma data rufe ido ta bude zata ganta a gida tsabar yanda ta tsani Asibitin da Duk wadanda suke ciki sa.
"Umaimah meye haka ne kina ji ina kiranki ina zakije ko jikin ne ya tashin miki?" Khalil ya fada bayandaya tararda ita yasha gabanta. Wani shegen kallo ta watsa masa, yanda ya ke washe baki yana riqe da hannun wannnan matar ya dawo mata seta kauce shi taci gaba da tafiyarta ya qara tare ta cikin fada fada yace
"Wai ke meyasa kike haka, ina miki magana shine zaki wuce kici gaba da tafiya ina zakije? Idan wani abun ne ya faru ki gaya mun mana se muje na kaiki"
"Allah ya kiyeye na sake shiga motar ka kaje dai kaci gaba da diban wadancan jakan marasa kamun kai da kake kulawa, tsabar rashin kunya a gaban uwar data haife ka da sauran mutane kake kama hannun wata qatuwa kuna dariya"
"Jamilar ce baki sani ba? Meyasa idan wulaqancinki ya tashi se kin nemi abinda zaki cimun mutunchi ko yan uwana?" Ya fada yana kallonta cikin ido saboda yanda kalmar Jaka data alaqanta da yar uwarsa. Seda ta harare shi kafin tace
"Toh dan Jamila ce se aka ce ku tsaya kuna iskanci a gaban mutane"
"Iskanci Umaimah, nine nake iskancin?" Ya sake katseta yana nuna kansa da yatsa.
Dauke kanta gefe tayi tana qunquni qasa qasa wanda tsaf ya jita "toh idab ba iskanci ba menene zaka wani kama mata hannu a tsakiyar mutane ita kuma se wani murmushi take tana yaqe haqora" ta fada. Seda Khalil ya hadiye malolon baqin cikin daya taso masa zuciyarsa tana ayyana masa rashin dacewarsa da wannan mara kunyar yarinyar qarara.
Dakyar ya iya bude baki yace "ki jira na yiwa Nuratu magana ta fito na mayar daku gida" dan ko babu komai shi ya dakko su daga qofar gidansu kuma seda Abba ya jaddada akan su dawo da wuri dan haka dole ya mayar dasu daga baya ze zauna ya yankewa kansa hukunnci akan ta, dan ya fara hango dalilan da suka saka har mutum uku fasa auranta, sannan yaga tasa wautar qarara da yake qoqarin daukar ta ya kaita nasa gidan.
"Ni? Ai wallahi bazan shiga motar ka ba ita dai da bata da zuciya taje ta zauna seka maida ita amma ni kaga tafiyata, kuma ka qaddara daga nan gurin babu ni babu kai kaje can cikin yan uwan naka ka auri daya idan zaka iya" Umaimah ta fada cikin tsananin rashin kunya kafin ta murguda masa baki tareda baza Hijabinta da yake har qasa ta tafi ta barshi a gurin kamar wanda aka dasa.
Dakyar ya iya jan qafafunsa da sukayi sanyi ya koma dakin, yana shiga suka hau tambayarsa ina take lafiya dai? Ya rasa me zece musu ga tunanin maganar data fada masa da ke neman ruguzashi haka ya daure ya tattaro yawun bakin sa yace "Amai ne ya taso mata, gata can A mota Nuratu muje na mayar daku gida tace akwai sauran magungunanta da bata gama shanyewa ba".
Nuratu da duk ta tsargu dan tun fitar sa wata daga cikin matan ta fara qananun maganganu akan taga wani kallon wulaqanci da Umaiman ta watsa musu kafin ta fita, aka samu wata ta goyi ganin zasu tada hayaniya Hajiya ta tsawatar musu, ita dai tayi tsuru, Jamilan ta zauna kusa da ita tana janta da magana amma ta kasa amsawa se murmushin yaqe kawai take tasan Allah kadai yasan yanda zasu kwashe a wajen nan, Allah yasa kar tayi rashin hankalin nata data saba ta tarawa kanta mutane har magana ta dawo dakin su samu nayi shigowar da Khalil yayi ya sakata sakin ajiyar zuciya dukda a kallo daya da tayi masa ta gane akwai matsala Umaimah tayi tsiyar, yana cewa ta tashi kuwa ta miqe tana qara yiwa Hajiya Addu'ar samun sauqi ta fice.
Dama bata saka ran ganin Umaimah a waje ba tasan kuma shima ya fada ne kawai dan haka suna shiga motar tun kafin yayi magana ta kalle shi tace
"Dan girman Allah Khalil kayi haquri, Al'amarin Umaimah se Addu'a se tayi abu kuma daga baya tazo tana nadama"
"Gaskiya I'm sorry to say amma Nuratu sam yar uwarki bata da tunani, could you believe ni ta kalla ta kira da dan iska a matsayina na mijin da zata aura? Ba tun yau ba take fada mun maganganu marasa dadi amma ina mata uzuri sedai naga a kullum a maimakon abin ya rage gaba ya ke qarayi.
Beside me nayi mata? Saboda kawai na gaisa da yar uwata shine ya bata damar da zata gayamun maganganu haka har tana fadin babu ni babu ita naje cikin yan uwana na nemi wata na aura me yake damun Kwakwalwar Umaimah? Ko kuma daman wannan rashin hankalin shine zafin kishin da take cewa tana dashi?.
Indai haka ne na godewa Allah daya nuna mun ainihinta tun kamin na aureta na aurar wa kaina damuwa, kuma banga laifin duk wadanda suka fasa auranta a baya ba saboda sam Umaimah ba macen aure ba. Macen da zata iya tsayawa a gabanka ta gaya maka duk maganar datazo baki ta ba tareda tayi shayi ko taga qimarka ba ai ba matar aure bace, dukda ma dai ta fada da bakinta babu ita babu ni Allah yasa hakan shi yafi Alkhairi, ki shiga ciki idan Abba yana nan kiyi mun sallama dashi dan Allah tunda wuri gara mu sama ma kanmu sauqi Allah ya hada kowa da rabonsa" Khalil da yau zuciyar yan maza ta motsa masa ya fada daidai sanda ya tsaya kofar gidan su Umaiman.
Ido kawai Nuratu ta saka masa tasan gaskiyar sa ya fada amma bata fatan yar uwarta ta rasa nagartaccen Namiji irinsa, shi kadai ne take tunanin ze iya chanza Umaiman gashi tun ba'aje ko ina ba shima ya sare da halinta yana zancen fasa aure.
Bude baki tayi dakyar tace "Kayi haquri Khalil nasan halin Umaimah sam idan ranta ya baci bata sanin me take fada..."
"Ranta ya baci da akayi mata me? Saboda na gaisa da yar uwata? Yayata ce fa uban mu daya. Haka kwanaki tayi mun saboda Jalila ta kirani twin sister na, ta ringa zagina har tana kirana da Mazina ci. A lokacin nayi mata uzuri a lokacin amma banda Yayi da babu wani abu da bata sani a kaina ba. Yan uwana mata babu wadda ban gaya mata sunanta na nuna mata hotunansu ta yanda ko a hanya suka hadu zata gane su ba.
Saboda gudun bacin ran Umaimah na chanza layin da nake harkokin kasuwancina dasu. Ba dan ina tsoro ta ba, kamar uwar data haifeni duk sanda ta raya mata zata ce nabata wayata tayi bincike ban taba nuna mata rashin jin dadi akan hakan ba ko babu komai waya sirfi ce nima ina da sirrikana da ya kamata ni kadai nasan dasu amma ko mai da ko ina na bata damar shiga ta duba a wayata, hakan ne ya bata damar da zata tsaya ta zageni duk a sunan kishi? Kishi ko hauka? To nidai na haqura taje kawai Allah ya bata wanda ze iya da halinta" Khalil yayi saurin katse Nuratun a fusace dan ransa qara baci yake yi duk idan ya tuna maganganun data yaba masa.
Bude baki tayi da niyyar sake magana ya bude motar yana cewa "kije dan Allah, ki bar Abban ma duk randa na sake biyowa nan haka nazo. Ki bawa Mama haquri nasan babu dadin amma hakan shi kadai ne abinda ze sama mun maslaha dukda ina son Umaimah amma bazan iya auranta ba, a waje tayi mun haka inaga na aureta na kai cikin gidana kinga wannan kome tayi ni na siya da kudina".
Jiki a mace Nuratu ta fita daga motar daidai sanda Adaidaita ya tsaya a qofar gidan Umaimah ta fito daga ciki, kallo daya tayi musu daga Nuratun har Khalil din kafin ta maida ido ta kan Nuratu tace "kuma da kika shiga motarsa ke kadai Allah ya isa bazan yafe ba, idan ma Amana aka ci mutum yaje shida Allah" ta sake fada tana kallon Khalil kafin fuuu ta shige gida. Murmushin zallar takaici Khalil ya saki, ya fara hasashen yarinyar nan bata da cikakkiyar lafiyar kwakwalwa ko kuma dai saitin kanta na gocewa ne lokaci lokaci.
"Ko jikin nata ne ya motsa?" Khalil ya fada yana kallon Nuratu, ta gyada kai dakyar tana hadiyar yawu dan ita tasan ba jiki bane sedai idan Baqin HALIN KISHIN nata ne ya motsa, Khalil ya fita da sauri yana cewa "Bari na dubata, idan jikin ne se mu ga likita a nan ya sake dubata" yayi waje da sauri ya bi bayanta.
PROMO
PROMO
PROMO
BEFORE 4K NOW 2500
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
KITURA SHEDAR BIYA 👇🏻
08162859027
AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA
INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK DATTIN MARA CIWON MARA CIWON JIKI HANA HAIHUWA RASHIN NI IMA RASHIN JIN SHA AWA FITAR FARIN RUWA KAIKAYI KURAJEN PP DA NA JIKI JIN ZAFI YAYIN SADUWA FITAR FARIN RUWA MAI WARI BASUR KOMAI DADEWARSHI CIWON NONO
SHIRYE NAKE ZANYI MAKU PROMO SABODA WA ANDA BASU SHA BA SU ZO SU DA DANA MAGANIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID DUK LABARIN DA AKE BAKU GASKENA MAGANINA KANKAT NE KOBAKISHA KOMAI BA YA ISHEKI
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 9
Hangota Khalil yayi ta doshi hanyar waje yabi bayanta da sauri kamarta sani ta qarawa tafiyarta sauri, cikin sassarfa ya bita ganin har ta kusa isa gate din Asibitin ya daga murya yana kiran sunanta amma bata juya ba jefa qafunta kawai take tana tafiya, ji take ina ma data rufe ido ta bude zata ganta a gida tsabar yanda ta tsani Asibitin da Duk wadanda suke ciki sa.
"Umaimah meye haka ne kina ji ina kiranki ina zakije ko jikin ne ya tashin miki?" Khalil ya fada bayandaya tararda ita yasha gabanta. Wani shegen kallo ta watsa masa, yanda ya ke washe baki yana riqe da hannun wannnan matar ya dawo mata seta kauce shi taci gaba da tafiyarta ya qara tare ta cikin fada fada yace
"Wai ke meyasa kike haka, ina miki magana shine zaki wuce kici gaba da tafiya ina zakije? Idan wani abun ne ya faru ki gaya mun mana se muje na kaiki"
"Allah ya kiyeye na sake shiga motar ka kaje dai kaci gaba da diban wadancan jakan marasa kamun kai da kake kulawa, tsabar rashin kunya a gaban uwar data haife ka da sauran mutane kake kama hannun wata qatuwa kuna dariya"
"Jamilar ce baki sani ba? Meyasa idan wulaqancinki ya tashi se kin nemi abinda zaki cimun mutunchi ko yan uwana?" Ya fada yana kallonta cikin ido saboda yanda kalmar Jaka data alaqanta da yar uwarsa. Seda ta harare shi kafin tace
"Toh dan Jamila ce se aka ce ku tsaya kuna iskanci a gaban mutane"
"Iskanci Umaimah, nine nake iskancin?" Ya sake katseta yana nuna kansa da yatsa.
Dauke kanta gefe tayi tana qunquni qasa qasa wanda tsaf ya jita "toh idab ba iskanci ba menene zaka wani kama mata hannu a tsakiyar mutane ita kuma se wani murmushi take tana yaqe haqora" ta fada. Seda Khalil ya hadiye malolon baqin cikin daya taso masa zuciyarsa tana ayyana masa rashin dacewarsa da wannan mara kunyar yarinyar qarara.
Dakyar ya iya bude baki yace "ki jira na yiwa Nuratu magana ta fito na mayar daku gida" dan ko babu komai shi ya dakko su daga qofar gidansu kuma seda Abba ya jaddada akan su dawo da wuri dan haka dole ya mayar dasu daga baya ze zauna ya yankewa kansa hukunnci akan ta, dan ya fara hango dalilan da suka saka har mutum uku fasa auranta, sannan yaga tasa wautar qarara da yake qoqarin daukar ta ya kaita nasa gidan.
"Ni? Ai wallahi bazan shiga motar ka ba ita dai da bata da zuciya taje ta zauna seka maida ita amma ni kaga tafiyata, kuma ka qaddara daga nan gurin babu ni babu kai kaje can cikin yan uwan naka ka auri daya idan zaka iya" Umaimah ta fada cikin tsananin rashin kunya kafin ta murguda masa baki tareda baza Hijabinta da yake har qasa ta tafi ta barshi a gurin kamar wanda aka dasa.
Dakyar ya iya jan qafafunsa da sukayi sanyi ya koma dakin, yana shiga suka hau tambayarsa ina take lafiya dai? Ya rasa me zece musu ga tunanin maganar data fada masa da ke neman ruguzashi haka ya daure ya tattaro yawun bakin sa yace "Amai ne ya taso mata, gata can A mota Nuratu muje na mayar daku gida tace akwai sauran magungunanta da bata gama shanyewa ba".
Nuratu da duk ta tsargu dan tun fitar sa wata daga cikin matan ta fara qananun maganganu akan taga wani kallon wulaqanci da Umaiman ta watsa musu kafin ta fita, aka samu wata ta goyi ganin zasu tada hayaniya Hajiya ta tsawatar musu, ita dai tayi tsuru, Jamilan ta zauna kusa da ita tana janta da magana amma ta kasa amsawa se murmushin yaqe kawai take tasan Allah kadai yasan yanda zasu kwashe a wajen nan, Allah yasa kar tayi rashin hankalin nata data saba ta tarawa kanta mutane har magana ta dawo dakin su samu nayi shigowar da Khalil yayi ya sakata sakin ajiyar zuciya dukda a kallo daya da tayi masa ta gane akwai matsala Umaimah tayi tsiyar, yana cewa ta tashi kuwa ta miqe tana qara yiwa Hajiya Addu'ar samun sauqi ta fice.
Dama bata saka ran ganin Umaimah a waje ba tasan kuma shima ya fada ne kawai dan haka suna shiga motar tun kafin yayi magana ta kalle shi tace
"Dan girman Allah Khalil kayi haquri, Al'amarin Umaimah se Addu'a se tayi abu kuma daga baya tazo tana nadama"
"Gaskiya I'm sorry to say amma Nuratu sam yar uwarki bata da tunani, could you believe ni ta kalla ta kira da dan iska a matsayina na mijin da zata aura? Ba tun yau ba take fada mun maganganu marasa dadi amma ina mata uzuri sedai naga a kullum a maimakon abin ya rage gaba ya ke qarayi.
Beside me nayi mata? Saboda kawai na gaisa da yar uwata shine ya bata damar da zata gayamun maganganu haka har tana fadin babu ni babu ita naje cikin yan uwana na nemi wata na aura me yake damun Kwakwalwar Umaimah? Ko kuma daman wannan rashin hankalin shine zafin kishin da take cewa tana dashi?.
Indai haka ne na godewa Allah daya nuna mun ainihinta tun kamin na aureta na aurar wa kaina damuwa, kuma banga laifin duk wadanda suka fasa auranta a baya ba saboda sam Umaimah ba macen aure ba. Macen da zata iya tsayawa a gabanka ta gaya maka duk maganar datazo baki ta ba tareda tayi shayi ko taga qimarka ba ai ba matar aure bace, dukda ma dai ta fada da bakinta babu ita babu ni Allah yasa hakan shi yafi Alkhairi, ki shiga ciki idan Abba yana nan kiyi mun sallama dashi dan Allah tunda wuri gara mu sama ma kanmu sauqi Allah ya hada kowa da rabonsa" Khalil da yau zuciyar yan maza ta motsa masa ya fada daidai sanda ya tsaya kofar gidan su Umaiman.
Ido kawai Nuratu ta saka masa tasan gaskiyar sa ya fada amma bata fatan yar uwarta ta rasa nagartaccen Namiji irinsa, shi kadai ne take tunanin ze iya chanza Umaiman gashi tun ba'aje ko ina ba shima ya sare da halinta yana zancen fasa aure.
Bude baki tayi dakyar tace "Kayi haquri Khalil nasan halin Umaimah sam idan ranta ya baci bata sanin me take fada..."
"Ranta ya baci da akayi mata me? Saboda na gaisa da yar uwata? Yayata ce fa uban mu daya. Haka kwanaki tayi mun saboda Jalila ta kirani twin sister na, ta ringa zagina har tana kirana da Mazina ci. A lokacin nayi mata uzuri a lokacin amma banda Yayi da babu wani abu da bata sani a kaina ba. Yan uwana mata babu wadda ban gaya mata sunanta na nuna mata hotunansu ta yanda ko a hanya suka hadu zata gane su ba.
Saboda gudun bacin ran Umaimah na chanza layin da nake harkokin kasuwancina dasu. Ba dan ina tsoro ta ba, kamar uwar data haifeni duk sanda ta raya mata zata ce nabata wayata tayi bincike ban taba nuna mata rashin jin dadi akan hakan ba ko babu komai waya sirfi ce nima ina da sirrikana da ya kamata ni kadai nasan dasu amma ko mai da ko ina na bata damar shiga ta duba a wayata, hakan ne ya bata damar da zata tsaya ta zageni duk a sunan kishi? Kishi ko hauka? To nidai na haqura taje kawai Allah ya bata wanda ze iya da halinta" Khalil yayi saurin katse Nuratun a fusace dan ransa qara baci yake yi duk idan ya tuna maganganun data yaba masa.
Bude baki tayi da niyyar sake magana ya bude motar yana cewa "kije dan Allah, ki bar Abban ma duk randa na sake biyowa nan haka nazo. Ki bawa Mama haquri nasan babu dadin amma hakan shi kadai ne abinda ze sama mun maslaha dukda ina son Umaimah amma bazan iya auranta ba, a waje tayi mun haka inaga na aureta na kai cikin gidana kinga wannan kome tayi ni na siya da kudina".
Jiki a mace Nuratu ta fita daga motar daidai sanda Adaidaita ya tsaya a qofar gidan Umaimah ta fito daga ciki, kallo daya tayi musu daga Nuratun har Khalil din kafin ta maida ido ta kan Nuratu tace "kuma da kika shiga motarsa ke kadai Allah ya isa bazan yafe ba, idan ma Amana aka ci mutum yaje shida Allah" ta sake fada tana kallon Khalil kafin fuuu ta shige gida. Murmushin zallar takaici Khalil ya saki, ya fara hasashen yarinyar nan bata da cikakkiyar lafiyar kwakwalwa ko kuma dai saitin kanta na gocewa ne lokaci lokaci.