Sashe 222
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mama tace ki fito ki dora Tuwan dare"
"Na rantse da Allah se naci kutumar ubanki idan na riqeki" ta fada cikin tsananin fushi tana tashi zaune muryar Abba ta jiyo daga waje yana cewa
"Gani a kusa fito kici uban nata kuma karki fito kiyi abinda tace kinji".
Kuka daya riga ya zema mata jiki ta fasa amma bame qara irin na jiya ba, jikinta kamar ana sarata haka take ji bata warke daga jinyar dukan data ci jiyan ba ga Azabar aiki an tasota a gaba. Harta sauke tuwon tana kuka, Miyar dai yanzu ta saka musu maggi dukda bata dan dana taji yanda yayi ba gurin kadin ne daman ita hannunta baya yauqi dan haka kubewar ta tsinke kamar Romo, ta Jibge Tuwon a Kula gaba daya ba tareda ta Malmala ba danma na Semovita ne amma dukda haka jikinta ya gaya mata gurin tuqin tana gamawa ta tsallake komai a inda yake ta wuce daki harda kwanukan data wanke tun dazun bata kau dasu ba. Seda ta shiga dakin Mama dake lura da duk abinda takeyi ta fito.
Ta bude tukunyar Miyar ta dandana, kai kawai ta girgiza ta maidata kan wuta ta qara abinda ya kamata ta kuma daureta sannan ta sauke ta shiga rabon tuwon dan Goma ake nema a lokacin daman badan Abba daya ce setayi girkin ba batayi niyar sake jira ta kwashi takaicin Umaimah ba da tuni ta gama girkinta.
Guraren sha daya tuni tayi nisa a bacci dan tana shiga dakin ta kife tana kukan takaici a haka baccin ya kwasheta kiran sunanta taji anayi tareda bubbuga qafarta ta bude ido dakyar dan bata da Nauyin bacci taga Ummu-Salma tsaye, seda ta tashi zaune da kyar kafin Ummu-Salman tace
"Anty Umaimah kije inji Abba"
"Inje kuma Me zanyi masa?" Umaiman ta fada tamkar zata fasa kuka wannan wane kalar bala'ine?
Ita dai Ummu-Salma na tsaye a gefe, bata dade da shigowa gidan ba ta taho daga makaranta Dutse take FUD tana Final Semester dinta Motarsu ta lalace se goma ta iso tana shirin kwanciya Abban ya ce ta kirawo masa Umaiman.
Seda ta gama qunquninta da qananun hawaye kafin ta miqe tana layi ta fita, tsoronta karya sake mata irin dukan jiya da babu inda zata wlh haka ta isa falon Abban suna zaune tareda Mama da Anty ga Kular abincin ranar da tayi a gabansa tana kallon fuskarsa gabanta ya fadi saboda fushin data gani akanta wai shi da Bashi da lafiya dan Allah baze sararawa zuciyarsa haka ya dena fushi ba? Qasa ta samu ta rabe idonta har sannan yana yajin bacci Abban ya fara magana cikin fada yana cewa
"Wato saboda ki nuna ke bakya ji duk kuma abinda aka ce kiyi sekin bata wa mutane rai shiyasa kikayi haka ko? To bari kiji daga yau kamar yanda na fada miki zan sake jaddadawa aikin gidan nan kaf ya rataya a wuyanki kuma Tilas kiyishi akan lokaci sannan a mutunce yanda kikaga iyayenki sunayi.
Karki kuskura qarfe bakwai tayi baki gama abin karyawa ba a ranakun makaranta sannan duk rintse karki wuce biyu ba tareda kin sauke na rana ba haka na dare kin sani kafin na dawo daga Sallar Isha'i an ajiye mun abinci. Sannan maganar wanke wanke da shara bana so na sake maimaita miki daga yanzu kinsan yanda akeyinsu Kwanukan da kika ajiye tun Yamma kuma suna nan suna jiranki ki gyara su yau kin samu yan uwanki sun rage miki aiki gobe basa nan ke zakiyi komai kuma ki yarda kiyi wani abu da ba haka ya kamata ba zamu gauraya a cikin gidan nan maganar wannan abincin kuma( ya nuna kular gabansa yace) daga yau har zuwa sanda ze qare shine abincinki a cikin gidan nan Umaimah koda ace zeyi tsutsa Wallahi se ya qare zan ci gaba da baki abinci a cikin gidan nan idan kuma kika ci wani abu nawa ba tareda umarnina ba Allah ya isa"
A firgice suka kalleshi gaba dayansu Anty tayi saurin cewa
"Haba Alhaji me yayi zafi zakayi mata Allah ya isa akan Abinci?"
"Sharadi na bata idan kuma idan har ta qi bi na maimaita Ban yafe ba" ya sake fada cikin tabbatarwa se aka rasa wadda zata sake magana a cikinsu se Umaimah data rushe da sabon kukan tashin hankali dan lamarin kam ya girmama ya zarce tunaninsu, Abba kuwa ko a jikinsa yaci gaba da cewa
"Sannan komai ruwa komai Iska da Itace zakiyi girki ban yarda ki sake kunna mun Gas a gida ba tunda bada kudinki na siya ba wanda kikayi amfani dashi yauma se kin biyani".
Anty da Mama dai sun rasa ta cewa Umaimah ko kallonsu takeyi a qoqarinta nason su roqa mata sassauci akan wannan lamari ina zata kai wannan shinkafa da ta ranar ma dakyar ta iyaci muguntarta ta qare akanta kenan ai wlh gara yace ta biyashi kudin shinkafar kawai da wannan tsatstsauran hukunci ita zancen karta kuma ci masa abinci ma be dameta ba tana da yan kudadenta zata iya ciyar da kanta na tsahon lokacin da yace amma zancen tayi ta cin shinkafa ai bema taso ba. Ganin Abban ya miqe Alamar zeje ya kwanta kuma har sannan Anty da Mama basu roqa mata sassauci ba yasa ta zabura cikin kuka me tsanani tace
"Dan girman Allah Abba kayi haquri wlh bazan iya ci ba na yarda ayi lissafi zan biyq duk kudin amma ka barni na fita dashi na bawa Almajirai" s Abban ya dakata ya juya ya kalleta fuskarsa babu yabo babu fallasa yace
"Wato saboda su basu da uwa da uba a kusa shine zaki basu abinda kika kasa ci ko? To ban yarda ba kuma ban janye maganata ba" daga haka ya shige cikin dakinsa ya barsu. Anty tayi tsaki qasa qasa ta miqe ta fice daga falon Mama ta bita da kallo a ranta tana ayyana idan ba'ayi wasa ba Umaimah na shirin rusa zaman lafiyar da sukeyi a cikin gidan dab tun a daren jiya ta lura da Anty ta kai maqura da Al'amuran Umaiman dan a daren jiya da Abban ya yanke jiki ya fadi bayan ya fito daga wanka Allah ya rufa Asiri Antyn na tsaye ta kai masa ruwan shayi ita ta tareshi tana kuka take cewa Maman
"Gaskiya kija mata kunne ta dena dagawa Alhaji hankali haka dan idan ya mutu bata da Asara ke kanki kukanki kadan ne dan duka yayanki kin aurar kuma suna da Madafa nice me qananan yara" tun a daren Jiyan maganar take nuqurqusarta amma ta shanye ko su Nuratu bata gayawa ba ta kuma tabbatar dalilin da ya saka dazu har Sharifa take sake maimaitawa Umaiman cewar karta kashe musu uba kenan qila ita Antyn tayi zancen da yayanta.
Gajiya da kukan da Umaiman takeyi ya saka Maman miqewa ita ma se ta zabura ta bita har suka je bakin qofar Maman bata dena gunjin kukan ba ganin tana shirin shigewa daki ta barta yasa cikin kuka tace
"Dan Allah Mama dan darajar Manzon Allah kisa baki Abba ya haqura na bawa Almajirai abincin wlh bazan iya ci ba ni na yarda kar a bani abinci har tsahon lokacin daya kamata na cinye wannan din".
Yanda take kukan da magiya abin Da da Mahaifi se zuciyar Maman ta kamu da tausayinta dan haka cikin sanyi tace mata
"Ki samu Robobi ki juye ki saka a Freezer idan ta kitchen din bata dauke ba ki kawo nan ki saka a Fridge dare yayi yanzu da Safe maga yanda za'ayi" daga haka ta shige daki ta barta babu yanda ta iya ta koma ta dakko Kular abincin tayi yanda Maman tace dan tasan idan ma ta barshi ya lalace qarin laifi ne a gurinta. Seda ta gama Adana abincin tas ta kwashe kwanukan wanke wanken data bari bakin famfo ta shigar dasu kitchen kafin ta koma daki tana ci gaba da kuka, daren bata iya runtsawa ba tunanin yanda zata cinye shinkafar nan safe rana dare harta qare takeyi idan Abban be haqura ba seda Asuba ta gabato bacci ya fara fizgarta, motsin shigowar Abba dasu Salman daga Masallaci ya farkar da ita kamar wadda aka koro fit ta fice daga dakin ta tsaya gaban Abban tana muzurai so takeyi ta sake kafa masa magiya amma yanda taga fuskarsa a daure ya hanata iya bude baki tace masa komai se hawaye suka fara mata tsere Abba kuwa yayi wucewarsa ciki ba tareda yabi ta kanta ba indai juninta rashin ji yana da hanyoyin dafata cikin ruwan sanyi har tayi laushi kuwa.
Ciki ta koma tana sharar kwalla tayi Alwala tayi sallah, harta kishingida tana ci gaba da share Hawayen ta tuna da zancen girke seta fashe da kuka me sauti harda sheshsheqa musamman data tuna itace zata hura kai wannan bala'i da me yayi kama? Sanda tana gidanta iyanzu tana kan Royal Bed cikin Turkish Duvet ga sanyin Ac da qamshin freshner suna ratsata, tana kwance Ruqayya zata shigo mata da abin kari har kan gado ta shiga Jacuzzi tayo wanka taci a yangance ta sake kwanciya amma yanzu Murhune yake jiranta da Itace kai Allah ka kawo mata dauki. Kuka tasha bana wasa ba kafin ta lallabi kanta ta fita dan zaman ba amfani ze mata ba bandama ta sake ja wa kanta wata shiga ukun.
A qofar falon Mama ta durqusa ta gaisheta ta daga mata kai kawai a hakan ma taji dadi dan tunda ta dawo Maman bata taba amsa gaisuwarta ba, murya na rawa tace
"Me za'a dafa Mama?"
"Kunun tsamiya da Alala, wake yana nan an jiqa seki wanki ki bawa Yasir ya kai markade shima qullin kunun yana nan a Kitchen idan kinga dama ki bata ke zakiyi taci harsu qare" Maman ta bata amsa ba tareda ta kalleta ba harta miqe kuma ta koma murya na rawa tace
"Mama kinsan idan na dama kunu tsinkewa yakeyi, sedai na dafa Abba kuma baya so a dafa".
"Na rantse da Allah se naci kutumar ubanki idan na riqeki" ta fada cikin tsananin fushi tana tashi zaune muryar Abba ta jiyo daga waje yana cewa
"Gani a kusa fito kici uban nata kuma karki fito kiyi abinda tace kinji".
Kuka daya riga ya zema mata jiki ta fasa amma bame qara irin na jiya ba, jikinta kamar ana sarata haka take ji bata warke daga jinyar dukan data ci jiyan ba ga Azabar aiki an tasota a gaba. Harta sauke tuwon tana kuka, Miyar dai yanzu ta saka musu maggi dukda bata dan dana taji yanda yayi ba gurin kadin ne daman ita hannunta baya yauqi dan haka kubewar ta tsinke kamar Romo, ta Jibge Tuwon a Kula gaba daya ba tareda ta Malmala ba danma na Semovita ne amma dukda haka jikinta ya gaya mata gurin tuqin tana gamawa ta tsallake komai a inda yake ta wuce daki harda kwanukan data wanke tun dazun bata kau dasu ba. Seda ta shiga dakin Mama dake lura da duk abinda takeyi ta fito.
Ta bude tukunyar Miyar ta dandana, kai kawai ta girgiza ta maidata kan wuta ta qara abinda ya kamata ta kuma daureta sannan ta sauke ta shiga rabon tuwon dan Goma ake nema a lokacin daman badan Abba daya ce setayi girkin ba batayi niyar sake jira ta kwashi takaicin Umaimah ba da tuni ta gama girkinta.
Guraren sha daya tuni tayi nisa a bacci dan tana shiga dakin ta kife tana kukan takaici a haka baccin ya kwasheta kiran sunanta taji anayi tareda bubbuga qafarta ta bude ido dakyar dan bata da Nauyin bacci taga Ummu-Salma tsaye, seda ta tashi zaune da kyar kafin Ummu-Salman tace
"Anty Umaimah kije inji Abba"
"Inje kuma Me zanyi masa?" Umaiman ta fada tamkar zata fasa kuka wannan wane kalar bala'ine?
Ita dai Ummu-Salma na tsaye a gefe, bata dade da shigowa gidan ba ta taho daga makaranta Dutse take FUD tana Final Semester dinta Motarsu ta lalace se goma ta iso tana shirin kwanciya Abban ya ce ta kirawo masa Umaiman.
Seda ta gama qunquninta da qananun hawaye kafin ta miqe tana layi ta fita, tsoronta karya sake mata irin dukan jiya da babu inda zata wlh haka ta isa falon Abban suna zaune tareda Mama da Anty ga Kular abincin ranar da tayi a gabansa tana kallon fuskarsa gabanta ya fadi saboda fushin data gani akanta wai shi da Bashi da lafiya dan Allah baze sararawa zuciyarsa haka ya dena fushi ba? Qasa ta samu ta rabe idonta har sannan yana yajin bacci Abban ya fara magana cikin fada yana cewa
"Wato saboda ki nuna ke bakya ji duk kuma abinda aka ce kiyi sekin bata wa mutane rai shiyasa kikayi haka ko? To bari kiji daga yau kamar yanda na fada miki zan sake jaddadawa aikin gidan nan kaf ya rataya a wuyanki kuma Tilas kiyishi akan lokaci sannan a mutunce yanda kikaga iyayenki sunayi.
Karki kuskura qarfe bakwai tayi baki gama abin karyawa ba a ranakun makaranta sannan duk rintse karki wuce biyu ba tareda kin sauke na rana ba haka na dare kin sani kafin na dawo daga Sallar Isha'i an ajiye mun abinci. Sannan maganar wanke wanke da shara bana so na sake maimaita miki daga yanzu kinsan yanda akeyinsu Kwanukan da kika ajiye tun Yamma kuma suna nan suna jiranki ki gyara su yau kin samu yan uwanki sun rage miki aiki gobe basa nan ke zakiyi komai kuma ki yarda kiyi wani abu da ba haka ya kamata ba zamu gauraya a cikin gidan nan maganar wannan abincin kuma( ya nuna kular gabansa yace) daga yau har zuwa sanda ze qare shine abincinki a cikin gidan nan Umaimah koda ace zeyi tsutsa Wallahi se ya qare zan ci gaba da baki abinci a cikin gidan nan idan kuma kika ci wani abu nawa ba tareda umarnina ba Allah ya isa"
A firgice suka kalleshi gaba dayansu Anty tayi saurin cewa
"Haba Alhaji me yayi zafi zakayi mata Allah ya isa akan Abinci?"
"Sharadi na bata idan kuma idan har ta qi bi na maimaita Ban yafe ba" ya sake fada cikin tabbatarwa se aka rasa wadda zata sake magana a cikinsu se Umaimah data rushe da sabon kukan tashin hankali dan lamarin kam ya girmama ya zarce tunaninsu, Abba kuwa ko a jikinsa yaci gaba da cewa
"Sannan komai ruwa komai Iska da Itace zakiyi girki ban yarda ki sake kunna mun Gas a gida ba tunda bada kudinki na siya ba wanda kikayi amfani dashi yauma se kin biyani".
Anty da Mama dai sun rasa ta cewa Umaimah ko kallonsu takeyi a qoqarinta nason su roqa mata sassauci akan wannan lamari ina zata kai wannan shinkafa da ta ranar ma dakyar ta iyaci muguntarta ta qare akanta kenan ai wlh gara yace ta biyashi kudin shinkafar kawai da wannan tsatstsauran hukunci ita zancen karta kuma ci masa abinci ma be dameta ba tana da yan kudadenta zata iya ciyar da kanta na tsahon lokacin da yace amma zancen tayi ta cin shinkafa ai bema taso ba. Ganin Abban ya miqe Alamar zeje ya kwanta kuma har sannan Anty da Mama basu roqa mata sassauci ba yasa ta zabura cikin kuka me tsanani tace
"Dan girman Allah Abba kayi haquri wlh bazan iya ci ba na yarda ayi lissafi zan biyq duk kudin amma ka barni na fita dashi na bawa Almajirai" s Abban ya dakata ya juya ya kalleta fuskarsa babu yabo babu fallasa yace
"Wato saboda su basu da uwa da uba a kusa shine zaki basu abinda kika kasa ci ko? To ban yarda ba kuma ban janye maganata ba" daga haka ya shige cikin dakinsa ya barsu. Anty tayi tsaki qasa qasa ta miqe ta fice daga falon Mama ta bita da kallo a ranta tana ayyana idan ba'ayi wasa ba Umaimah na shirin rusa zaman lafiyar da sukeyi a cikin gidan dab tun a daren jiya ta lura da Anty ta kai maqura da Al'amuran Umaiman dan a daren jiya da Abban ya yanke jiki ya fadi bayan ya fito daga wanka Allah ya rufa Asiri Antyn na tsaye ta kai masa ruwan shayi ita ta tareshi tana kuka take cewa Maman
"Gaskiya kija mata kunne ta dena dagawa Alhaji hankali haka dan idan ya mutu bata da Asara ke kanki kukanki kadan ne dan duka yayanki kin aurar kuma suna da Madafa nice me qananan yara" tun a daren Jiyan maganar take nuqurqusarta amma ta shanye ko su Nuratu bata gayawa ba ta kuma tabbatar dalilin da ya saka dazu har Sharifa take sake maimaitawa Umaiman cewar karta kashe musu uba kenan qila ita Antyn tayi zancen da yayanta.
Gajiya da kukan da Umaiman takeyi ya saka Maman miqewa ita ma se ta zabura ta bita har suka je bakin qofar Maman bata dena gunjin kukan ba ganin tana shirin shigewa daki ta barta yasa cikin kuka tace
"Dan Allah Mama dan darajar Manzon Allah kisa baki Abba ya haqura na bawa Almajirai abincin wlh bazan iya ci ba ni na yarda kar a bani abinci har tsahon lokacin daya kamata na cinye wannan din".
Yanda take kukan da magiya abin Da da Mahaifi se zuciyar Maman ta kamu da tausayinta dan haka cikin sanyi tace mata
"Ki samu Robobi ki juye ki saka a Freezer idan ta kitchen din bata dauke ba ki kawo nan ki saka a Fridge dare yayi yanzu da Safe maga yanda za'ayi" daga haka ta shige daki ta barta babu yanda ta iya ta koma ta dakko Kular abincin tayi yanda Maman tace dan tasan idan ma ta barshi ya lalace qarin laifi ne a gurinta. Seda ta gama Adana abincin tas ta kwashe kwanukan wanke wanken data bari bakin famfo ta shigar dasu kitchen kafin ta koma daki tana ci gaba da kuka, daren bata iya runtsawa ba tunanin yanda zata cinye shinkafar nan safe rana dare harta qare takeyi idan Abban be haqura ba seda Asuba ta gabato bacci ya fara fizgarta, motsin shigowar Abba dasu Salman daga Masallaci ya farkar da ita kamar wadda aka koro fit ta fice daga dakin ta tsaya gaban Abban tana muzurai so takeyi ta sake kafa masa magiya amma yanda taga fuskarsa a daure ya hanata iya bude baki tace masa komai se hawaye suka fara mata tsere Abba kuwa yayi wucewarsa ciki ba tareda yabi ta kanta ba indai juninta rashin ji yana da hanyoyin dafata cikin ruwan sanyi har tayi laushi kuwa.
Ciki ta koma tana sharar kwalla tayi Alwala tayi sallah, harta kishingida tana ci gaba da share Hawayen ta tuna da zancen girke seta fashe da kuka me sauti harda sheshsheqa musamman data tuna itace zata hura kai wannan bala'i da me yayi kama? Sanda tana gidanta iyanzu tana kan Royal Bed cikin Turkish Duvet ga sanyin Ac da qamshin freshner suna ratsata, tana kwance Ruqayya zata shigo mata da abin kari har kan gado ta shiga Jacuzzi tayo wanka taci a yangance ta sake kwanciya amma yanzu Murhune yake jiranta da Itace kai Allah ka kawo mata dauki. Kuka tasha bana wasa ba kafin ta lallabi kanta ta fita dan zaman ba amfani ze mata ba bandama ta sake ja wa kanta wata shiga ukun.
A qofar falon Mama ta durqusa ta gaisheta ta daga mata kai kawai a hakan ma taji dadi dan tunda ta dawo Maman bata taba amsa gaisuwarta ba, murya na rawa tace
"Me za'a dafa Mama?"
"Kunun tsamiya da Alala, wake yana nan an jiqa seki wanki ki bawa Yasir ya kai markade shima qullin kunun yana nan a Kitchen idan kinga dama ki bata ke zakiyi taci harsu qare" Maman ta bata amsa ba tareda ta kalleta ba harta miqe kuma ta koma murya na rawa tace
"Mama kinsan idan na dama kunu tsinkewa yakeyi, sedai na dafa Abba kuma baya so a dafa".