Sashe 234
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mama kanta tayi mamakin ganin Ruman dukda tasan tayi aure kuma bata ga laifinta na qin sanar dasu na saboda ta dade da sanin Umaiman ta watsar da ita kamar yanda ta watsar da duk sauran qawayenta na kirki ta cicciba ta fita, Mijinta Barr na tsaye jikin motarsa yana jiranta dan ta sanar masa ba zama zatayi ba tun kafin suzo Kano dan a Sokoto take aure take nanata masa idan sunje zataje gidansu Umaiman da ya haddace sunanta saboda yanda take yawanyin hirarta, ta rasa number ta kuma tambayo duk qawayensu bata samu ba dan haka jiya suka zo yau tayiwa gidan tsinke danta gaida Mamanta kuma karbi number Umaimah se gashi taci karo da sabon Al'amari.
"Har kin fito?" Barr ya fada yana qoqarin bude mata mota seta yi qasa da kai saboda kar yaga idonta da sauran hawayen dake ciki tace
"Kaje kawai Barr zuwa bayan Magriba se ka dawo la daukeni na ma tarar da Umaiman tana ciki".
"Are you ok? Yanaga kamar ma kuka kikayi?" Ya fada yana matsawa kusa da ita tareda nazarin fuskarta setayi saurin juyawa dan tasan yanzu inya fara jera mata tambayoyi ba sauqi tace
"Kaje kawai idan mun koma gidan zan gaya maka koma menene" ta shige gidanta barshi yana binta da kallo tareda hasashen meya samu qawar tata tunda tace tana ciki ko duk kewar ta ce ta sakata kuka haka yaja motarsa ya tafi kafin Magribar tayi ya dawo ya dauketa.
Ruma kuwa dakin Umaimah ta sake komawa, tana nan inda ta barta ta zubawa bango ido alamar tayi nisa cikin tunanin da takeyi hawaye suka sake kawowa a idon Ruman data qarewa Umaimah kallo, ko a hasashe bata taba tunanin akwai taskun da ze sameta ta dawo haka ba, ta tabbata akwai wani babban Al'amari daya faru wanda bata da masaniya seta zauna a hankali ta dafa kafadar Umaiman tayi firgigit ta kalleta a tare kowacce ta sake fashewa da kukan da take riqewa suka rungume junansu kuka Umaimah takeyi me nuna raunin ta da irin halin da zuciyarta take ciki wanda tafe yake da tarin nadama da dana sani tareda neman mafita. Tun Ruma na kukan itama har tayi shiru ta shiga rarrashin Umaiman da dakyar ta iya hadiye kukanta badan ta gama gaba daya ba sedai kawai ta samu sauqin nauyin abinda ya danne mata qirji.
"Umaimah ki fada mun meya sameki, ki fitar dani daga rudanin da ganin yanayinki ya jefani meya faru?" Ruman ta fada cikin qoqarin son hana kanta sake fashewa da kuka dan yanayin Umaimah ya raunata mata zuciya da yawa. Seda Umaiman taja numfashi tana riqe da hannayen Ruma biyu kafin ta bude baki cikin muryar kuka tace
"Komai ma ya faru Ruma ni yanzu abinda kadai ya ragemun ganin ranar da zan koma ga Allah dan a duniya na rigada na rasa kowa da komai nawa"
"Kiyi mun magana a bude Umaimah kiyi mun bayani yanda zan fahimta, kamar yaya kin rasa kowa? Ga Mama da Abba na gani da Ransu basu mutu ba Yanayin dana ganki na san cewa akwai wani al'amari mara dadi a tareda ke Umaimah kin ganki kuwa kinga yanda kika koma?" Ruma ta fada tana kallon Umaiman tareda dauke kwallar dake qoqarin sake dawo mata. Umaimah ta dauke kanta gefe tana goge nata hawayen nauyi da kunyar Ruman ya rufeta idan ta tuna wukaqancin data mata a baya se taji bata cancanci ta sake hada ido da ita ba, Ta banzatar da ita a matsayinta na Aminiyarta tunta yarinta da take saita ta a hanyar kwarai take kuma gaya mata gaskiya.
Rabonta da Ruman tun Haihuwar Bibi, qarfi da yaji ta yakiceta daga rayuwarta saboda tana gaya mata gaskiya itama kuma tayi zuciya ta fita daga sabgoginta kamar yanda ta fada Umaiman bata da Aljanna ballantana taci gaba da binta tana wulaqantata tun daga nan suka yanke alaqa bata sake ganinta ba se yau da kwatsam ta fado gidansu kamar jifa a yanayin da tayi mamaki kwarai.
Matsa hannunta Ruman tayi cikinsigar lallashi tace
"Ki tuna a baya babu abinda muke boyewa juna, Rumanki ce fa idan baki sanar dani damuwarki ba wa zaki gayawa?" A hankali Umaiman ta bude baki muryarta na rawa tace
"Ruma rayuwata ta gamu da qalubale kala kala a halin yanzu ina cike da Nadamar abubuwan dana aikata a rayuwata na godewa Allah daya kawo mun ke a daidai lokacin danake buqatar taimako wlh Ruma a yanda nake ji na tabbata wata rana za'a iya wayar gari a tarar da gawata zuciyata ta buga na mutu saboda irin baqin cikin da nake kwana dashi nake tashi"
Ki dena fadar haka Umaimah duk abinda kikaga ya samu bawa a rayuwarsa da sanin Ubangiji"
"Haka Ruma kuma duk abinda ya sameni ni na hawa kaiba, halina ya jefani a yanayin danake ciki kuma nasan da cewar haqqin Khalil ne ya fara bibiyata tun yanzu, Ruma banida nutsuwa bana iya bacci har na rasa me nake tunani kaina da qirjina tamkar zasu fashe haka nake jinsu gashi a cikin gidan nan babu me saurarata kowa haushina yakeji basa kulani sun gazayi mun uzuri su karbi cewar tawa kalar qaddarar ce a haka" Umaimah ta sake fada tana fashewa da kukan daya fi nada rauni ita dai Rumana riqe da hannu ta tana matsawa alamar rarrashi tana kuma qoqarin gano inda bakin zaren maganar Umaiman yake a hankali ta Sake ce mata
"Qawata me yayi zafi har haka, me kika aikata da har su Mama sukayi fushi dake? Yanzu yan uwanki da har kwatance akeyi daku saboda yanda kowa ya shaida qaunar dake a tsakaninku suka banzatar dake me kika aikata Umaimah?"
Shiru Umaiman tayi kafin ta nisa a nutse ta shiga warware mata iya abinda take ganin ya kamata ta sani. Ruma ta ringa kiran sunayen Allah saboda rudanin da labarin Umaimah ya jefata, a sanyaye tace
"Umaimah kinyi kuskure kin kuma shafawa kanki baqin fentin da gogeshi zeyi wuya domin kin taba martabar da ba kowa zaka keta masa ya dauke kai ba, na tabbata yau da ace rigimarki ta tsaya iya kan Khalil da tuni kowa dade da mantawa saboda tsakanin Mata da Miji daman ana sabawa kuma a koma a zauna kamar ba'ayi ba amma Uwa fa Umaimah kin keta alfarmar Mahaifiyar sa koda ace Allah ya qaddara da sauran zama a tsakaninku a duk sanda ya kalleki se wannan abun ya dawo masa sannan mafi muni shi a karan kansa kin bar masa tabon da har abada baze manta dake ba a kullum ina gaya miki ki dena biyewa zuciyarki ki ringa amfani da kwakwalwarki yanzu kin gane abinda nake nufi? Ita zuciya a koda yaushe tana qawata mana son ranmu duk kyau ko munin abu yayinda kwakwalwa takanyi lissafi ta tantance abinda ya kamata da wanda be kamata ba. Na tabbata a lokacin da kin yi amfani da Tunaninki ba son zuciya ba da yanzu haka bata faru ba amma duk da haka lokaci ne qure miki ba kina da damar ko tubarwa Allah ki kuma nemi gafarar duk wadanda kika batawa amma a farko se ke a karan kanki kin yarda da cewar kinyi ba daidai ba"
"Na nawa kuma Ruma na rigada na yarda da cewar na aikata kuskure nayi dana sanin komai daya faru rashin mafitar yanda zanyi na gyara shine abinda ya dameni yake cin zuciyata duk dare da wannan baqin cikin nake kwana nake tashi. Iyayena muna zaune gida daya dasu Ruma na rasa alfarmar da zasu amsa koda gaisuwata yan uwana kaf babu meyi mun magana na zama kamar wata mujiya a cikinsu yau tsayin shekara uku da watanni kenan Ruma ban sake saka qafata a qofar gidan nan ba tunda aka sallamoni daga Asibiti Abba ya kafa mun dokar babu fita kullum ina zaune nike aikin komai a cikin gidan nan amma dukda haka be sa sun rangwanta mun ba a kullum qara kyarata da hantarata akeyi a cikin gidannan a ganina ko Mutum na kashe ai iyakar abinda zasuyi mun kenan" Umaimah ta fada muryarta na rawa se Ruma tayi qaramin murmushi tace
"Umaimah kenan iyayenki da yan uwanki suna yi miki haka ne saboda ki gane kuskurenki kuma koda ace kinyi nadama ke a karan kanki bana zaton kin nuna musu hakan kinga kuwa dole zasu ci gaba da nuna miki halin ko in kula tunda baki nuna musu kema kin gane kuskurenki kuma kin shirya gyarawa ba".
"Toh ya zanyi, ta yaya zan nuna musu na karbi kuskurena Ruma?" Umaiman ta katseta se Ruma tace
"Tun da al'amarin nan ya faru wa kika taba samu a cikin su ke dashi kika bashi haquri kika nuna musu cewar kinyi nadama kuma kin karbi kuskurenki?" Ruma ta fada tana tsareta da ido a sanyaye tace
"Babu"
"Dama na tabbatar da amsar Babu ce danna sanki farin sani tun ba yanzu ba baki san kiyi laifi ki bada haquri ba nayi tsammanin aure yasa kin canza ashe har yanzu kina nan da baqar kafiyarki da da babu abinda take ja miki kullum se wahala. Har ki iya zama tsayin shekara uku Mahaifanki suna fushi dake ku kwana gida daya ku tashi bama kya tsoron ki mutu a wannan halin me zaki gayawa Allah meye hujjarki ta kasa neman yardarsu?"
"Wlh Ruma nayi, Abba cewa yayi karna qara gaisheshi Mama ta hanani shiga dakinta itama idan na gaidata ba amsawa takeyi ba ya zanyi?"
"Har kin fito?" Barr ya fada yana qoqarin bude mata mota seta yi qasa da kai saboda kar yaga idonta da sauran hawayen dake ciki tace
"Kaje kawai Barr zuwa bayan Magriba se ka dawo la daukeni na ma tarar da Umaiman tana ciki".
"Are you ok? Yanaga kamar ma kuka kikayi?" Ya fada yana matsawa kusa da ita tareda nazarin fuskarta setayi saurin juyawa dan tasan yanzu inya fara jera mata tambayoyi ba sauqi tace
"Kaje kawai idan mun koma gidan zan gaya maka koma menene" ta shige gidanta barshi yana binta da kallo tareda hasashen meya samu qawar tata tunda tace tana ciki ko duk kewar ta ce ta sakata kuka haka yaja motarsa ya tafi kafin Magribar tayi ya dawo ya dauketa.
Ruma kuwa dakin Umaimah ta sake komawa, tana nan inda ta barta ta zubawa bango ido alamar tayi nisa cikin tunanin da takeyi hawaye suka sake kawowa a idon Ruman data qarewa Umaimah kallo, ko a hasashe bata taba tunanin akwai taskun da ze sameta ta dawo haka ba, ta tabbata akwai wani babban Al'amari daya faru wanda bata da masaniya seta zauna a hankali ta dafa kafadar Umaiman tayi firgigit ta kalleta a tare kowacce ta sake fashewa da kukan da take riqewa suka rungume junansu kuka Umaimah takeyi me nuna raunin ta da irin halin da zuciyarta take ciki wanda tafe yake da tarin nadama da dana sani tareda neman mafita. Tun Ruma na kukan itama har tayi shiru ta shiga rarrashin Umaiman da dakyar ta iya hadiye kukanta badan ta gama gaba daya ba sedai kawai ta samu sauqin nauyin abinda ya danne mata qirji.
"Umaimah ki fada mun meya sameki, ki fitar dani daga rudanin da ganin yanayinki ya jefani meya faru?" Ruman ta fada cikin qoqarin son hana kanta sake fashewa da kuka dan yanayin Umaimah ya raunata mata zuciya da yawa. Seda Umaiman taja numfashi tana riqe da hannayen Ruma biyu kafin ta bude baki cikin muryar kuka tace
"Komai ma ya faru Ruma ni yanzu abinda kadai ya ragemun ganin ranar da zan koma ga Allah dan a duniya na rigada na rasa kowa da komai nawa"
"Kiyi mun magana a bude Umaimah kiyi mun bayani yanda zan fahimta, kamar yaya kin rasa kowa? Ga Mama da Abba na gani da Ransu basu mutu ba Yanayin dana ganki na san cewa akwai wani al'amari mara dadi a tareda ke Umaimah kin ganki kuwa kinga yanda kika koma?" Ruma ta fada tana kallon Umaiman tareda dauke kwallar dake qoqarin sake dawo mata. Umaimah ta dauke kanta gefe tana goge nata hawayen nauyi da kunyar Ruman ya rufeta idan ta tuna wukaqancin data mata a baya se taji bata cancanci ta sake hada ido da ita ba, Ta banzatar da ita a matsayinta na Aminiyarta tunta yarinta da take saita ta a hanyar kwarai take kuma gaya mata gaskiya.
Rabonta da Ruman tun Haihuwar Bibi, qarfi da yaji ta yakiceta daga rayuwarta saboda tana gaya mata gaskiya itama kuma tayi zuciya ta fita daga sabgoginta kamar yanda ta fada Umaiman bata da Aljanna ballantana taci gaba da binta tana wulaqantata tun daga nan suka yanke alaqa bata sake ganinta ba se yau da kwatsam ta fado gidansu kamar jifa a yanayin da tayi mamaki kwarai.
Matsa hannunta Ruman tayi cikinsigar lallashi tace
"Ki tuna a baya babu abinda muke boyewa juna, Rumanki ce fa idan baki sanar dani damuwarki ba wa zaki gayawa?" A hankali Umaiman ta bude baki muryarta na rawa tace
"Ruma rayuwata ta gamu da qalubale kala kala a halin yanzu ina cike da Nadamar abubuwan dana aikata a rayuwata na godewa Allah daya kawo mun ke a daidai lokacin danake buqatar taimako wlh Ruma a yanda nake ji na tabbata wata rana za'a iya wayar gari a tarar da gawata zuciyata ta buga na mutu saboda irin baqin cikin da nake kwana dashi nake tashi"
Ki dena fadar haka Umaimah duk abinda kikaga ya samu bawa a rayuwarsa da sanin Ubangiji"
"Haka Ruma kuma duk abinda ya sameni ni na hawa kaiba, halina ya jefani a yanayin danake ciki kuma nasan da cewar haqqin Khalil ne ya fara bibiyata tun yanzu, Ruma banida nutsuwa bana iya bacci har na rasa me nake tunani kaina da qirjina tamkar zasu fashe haka nake jinsu gashi a cikin gidan nan babu me saurarata kowa haushina yakeji basa kulani sun gazayi mun uzuri su karbi cewar tawa kalar qaddarar ce a haka" Umaimah ta sake fada tana fashewa da kukan daya fi nada rauni ita dai Rumana riqe da hannu ta tana matsawa alamar rarrashi tana kuma qoqarin gano inda bakin zaren maganar Umaiman yake a hankali ta Sake ce mata
"Qawata me yayi zafi har haka, me kika aikata da har su Mama sukayi fushi dake? Yanzu yan uwanki da har kwatance akeyi daku saboda yanda kowa ya shaida qaunar dake a tsakaninku suka banzatar dake me kika aikata Umaimah?"
Shiru Umaiman tayi kafin ta nisa a nutse ta shiga warware mata iya abinda take ganin ya kamata ta sani. Ruma ta ringa kiran sunayen Allah saboda rudanin da labarin Umaimah ya jefata, a sanyaye tace
"Umaimah kinyi kuskure kin kuma shafawa kanki baqin fentin da gogeshi zeyi wuya domin kin taba martabar da ba kowa zaka keta masa ya dauke kai ba, na tabbata yau da ace rigimarki ta tsaya iya kan Khalil da tuni kowa dade da mantawa saboda tsakanin Mata da Miji daman ana sabawa kuma a koma a zauna kamar ba'ayi ba amma Uwa fa Umaimah kin keta alfarmar Mahaifiyar sa koda ace Allah ya qaddara da sauran zama a tsakaninku a duk sanda ya kalleki se wannan abun ya dawo masa sannan mafi muni shi a karan kansa kin bar masa tabon da har abada baze manta dake ba a kullum ina gaya miki ki dena biyewa zuciyarki ki ringa amfani da kwakwalwarki yanzu kin gane abinda nake nufi? Ita zuciya a koda yaushe tana qawata mana son ranmu duk kyau ko munin abu yayinda kwakwalwa takanyi lissafi ta tantance abinda ya kamata da wanda be kamata ba. Na tabbata a lokacin da kin yi amfani da Tunaninki ba son zuciya ba da yanzu haka bata faru ba amma duk da haka lokaci ne qure miki ba kina da damar ko tubarwa Allah ki kuma nemi gafarar duk wadanda kika batawa amma a farko se ke a karan kanki kin yarda da cewar kinyi ba daidai ba"
"Na nawa kuma Ruma na rigada na yarda da cewar na aikata kuskure nayi dana sanin komai daya faru rashin mafitar yanda zanyi na gyara shine abinda ya dameni yake cin zuciyata duk dare da wannan baqin cikin nake kwana nake tashi. Iyayena muna zaune gida daya dasu Ruma na rasa alfarmar da zasu amsa koda gaisuwata yan uwana kaf babu meyi mun magana na zama kamar wata mujiya a cikinsu yau tsayin shekara uku da watanni kenan Ruma ban sake saka qafata a qofar gidan nan ba tunda aka sallamoni daga Asibiti Abba ya kafa mun dokar babu fita kullum ina zaune nike aikin komai a cikin gidan nan amma dukda haka be sa sun rangwanta mun ba a kullum qara kyarata da hantarata akeyi a cikin gidannan a ganina ko Mutum na kashe ai iyakar abinda zasuyi mun kenan" Umaimah ta fada muryarta na rawa se Ruma tayi qaramin murmushi tace
"Umaimah kenan iyayenki da yan uwanki suna yi miki haka ne saboda ki gane kuskurenki kuma koda ace kinyi nadama ke a karan kanki bana zaton kin nuna musu hakan kinga kuwa dole zasu ci gaba da nuna miki halin ko in kula tunda baki nuna musu kema kin gane kuskurenki kuma kin shirya gyarawa ba".
"Toh ya zanyi, ta yaya zan nuna musu na karbi kuskurena Ruma?" Umaiman ta katseta se Ruma tace
"Tun da al'amarin nan ya faru wa kika taba samu a cikin su ke dashi kika bashi haquri kika nuna musu cewar kinyi nadama kuma kin karbi kuskurenki?" Ruma ta fada tana tsareta da ido a sanyaye tace
"Babu"
"Dama na tabbatar da amsar Babu ce danna sanki farin sani tun ba yanzu ba baki san kiyi laifi ki bada haquri ba nayi tsammanin aure yasa kin canza ashe har yanzu kina nan da baqar kafiyarki da da babu abinda take ja miki kullum se wahala. Har ki iya zama tsayin shekara uku Mahaifanki suna fushi dake ku kwana gida daya ku tashi bama kya tsoron ki mutu a wannan halin me zaki gayawa Allah meye hujjarki ta kasa neman yardarsu?"
"Wlh Ruma nayi, Abba cewa yayi karna qara gaisheshi Mama ta hanani shiga dakinta itama idan na gaidata ba amsawa takeyi ba ya zanyi?"