Sashe 7
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai rabu da motar nan, kasan 306 da matsalar belt, haka kawai ina tafiya se ya cire kai na gaji dai kawai na siyar da ita na siyi wannan yafi mun na shiga ko ina hankalina a kwance".
"Tab, gaye iya gaye ashe gurgune" Nabila Sani ta fada tana kallon Khalil dake buga machine, tunda suka fito ta saka su zama a kujerun da suke kusa da Office din saboda harga Allah Khalil din ya tafi da imaninta, jira take ya fito tasan ta yanda zata yi masa magana se ga wannan big turn off din, ashe ma wankan ne kawai aljihu babu ko sisi.
"Arziqi nufin Allah ne, kuma dan kin ganshi da lifan shine aka ce miki matsiyaci ne wallahi Nabila ki dena abinda kike shiyasa har yau kika rasa ko wanda ze kiraki a waya ki rage dare" Umaimah data kalli Khalil din itama ta juya tana gayawa Nabila.
"Allahu akbar, Allah ka nuna mana Annabi, yau Umaimah ce takewa wani fadan yayi ba daidai ba lallai inda ranka kasha kallo" Halima ta fada cikin sigar tsokana dan daman ita gwanace.
"Se ku tashi mu tafi ai" Nabilan ta fada a fusace fuu tayi gaba suka rufa mata baya suna sake caccakarta.
Murmushi Khalil da duk abinda suka fada yaji yayi dan da dan qarfi suke maganar bayan haka yana da kunne sosai, Kallon Nasir yayi dake danna waya yace
"Nas kodai na shiga gurin nan ne, dagaske fa yarinyar nan tamun over taking"
"Abokina ka shiga kawai mana tsoron me kake ji, babu komai in sha Allahu tsamu tsaya maka kawai dai ka shirya ina qara gaya maka akwai daru" Nasir ya fada yana bashi hannu,
"Shikenan zanyi tunani akai" daga nan sukayi sallama ya buga mashin dinsa yayi gaba. A bakin get ya sake haduwa dasu suna jiran abin hawa, sukayi ido hudu da Umaimah ta kuwa murguda masa baki da harara yayi mata murmushi ya wuce abinsa.
Cikin taimakon Allah suka qare jarabawarsu tsaf saura jiran sakamako, ranar ansha hotuna anyi celebration, akwai Dinner da suka shirya yi an dade ana hada kudi daman dan harda anko suka fita Umaimah ta biya kudin komai amma bata jin zataje, tasan ma baza'a barta ba yanzu kuwa da take gudun laifi bazata fita babu izini ba. tunda suka fara jarabawa daman a faduwar gaban abinda yake gaba take, furucin Abba na idan bata fitar da Miji ba ze bada ita sadaka na bala'in damunta ta kuma rasa yanda zatayi.
Ta nemi shawarar Rumasa'u akan maganar tace mata tayita Addu'a kawao Allah ya yi mata zabi na gari, ta kuma ce mata ta gwada neman wanda taga hankalinta yafi kwantawa dashi cikin samarinta na baya ko Allah zesa a dace amma babu nasara.
Duk wanda tayi qoqarin bugun cikinsa akan batun aure zillewa suke, qiriqiri suke nuna mata suna sonta da gaske amma bazasu iya da halinta ba wannan abin na bala'in qona mata rai, ita wane hali ne da ita?
Shin laifi ne dan kayi kishin abinda kake so su ba abin alfaharin su bane ma ace ana kishin su?
Kusan sati da gama makarantar su babu wanda yace mata qala akan batun aure, ba kamar baya ba yanzu komai ya dawo daidai a gidan itace ma take dararewa wani lokacin saboda gudun kar a diro mata da maganar fito da Miji katsahan. Fita ce dai aka hanata, dan ko Islamiyyar da take zuwa Asabar da Lahadi ma Abban ya soke yace yawo ne kawai, daidai gwargwado ta samu ilimi ta zauba agida tayita tilaqar abinda ta sani amma fita indai bada dalili me qarfi ba be yarda ba.
Ana haka Yayarsu Anty Hajiyayye ta haihu, dayake CS akayi mata da farko akace a dawo da ita gida ta zauna idan jikinta ya warware seta koma tunda a can babu mataimaki ga yara kuma amma Abban su yaqi, daga qarshe dai dakyar Mama ta lallabashi akan tunda Umaimah bata komai taje ta zauna mata tareda wata mata da aka samu har zuwa sanda zata warware.
Seda ya kafa mata warning sosai ya kuma jawa Hajiyayyae kunne akan duk in yaji ba daidai ba se ranta yafi na kowa baci haka ta tattara ta tafi gidan Yaya Hajiyayyen.
Washe garin suna da yake ba taro sukayi ba bayan an gama suyar nama an kasa Yaya Hajiyayye ta bata tace ta shiga gidan da yake kallon nasu takai.
Dogon Hijabi har qasa ta dora akan Doguwar rigar material din jikinta fuskar nan kamar ko yaushe babu ko digon kwalli akan ta amma da yake kyanta daga Allah ne se gata ta fito shar abin ta.
Tun daga wajen gidan ta tabbatar da gidan masu arziqi ne, idan ma a yanzu babu to tabbas da an samu ta tura qofar get din da take a bude ta shiga qaton compound din gidan da sallama. Babu kowa a tsakar gidan, taja ta tsaya ganin qofofi biyu ne manya bata san wanne ne ta shiga ba, gashi ma ta manta ta tambayeta wa zaa kaiwa dan qila mata biyu ne a gidan.
Daga bayanta taji ance
"Ya kika tsaya? Bismillah ki shiga suna ciki" seta juya a firgice dan bataji takun takalma ba se magana kawai, ido hudu sukayi da Khalil dake tsaye a bayanta yasha wanka da wata danyar Shadda Fara gurin gaba daya ya karade da Qamshin turarensa.
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 4
Ya ganeta, amma da alama it bata gane shi ba tace,qasa qasa ta harareshi tace
"Ka tsorata ni wallahi, kuma bansan qofar shigan ba. Daga gidan Maman Asad nake ta bada naman suna a kawowa Hajiya" ta qarasa tana miqa masa ledar Naman. Se yayi gaba yana cewa
"Muje na nuna miki"
Tsabar neman magana irin nata bibsa take a baya tana kwaikwayon tafiyar sa da yake yi cikin nutsuwa kamar me qirga takunsa. Gulmarsa take a zuciya tana cewa
"Ji yanda yake wani yanga dan Allah kamar mace ya ware qafa yayi sauri Aa se batamun lokaci yake" a haka ya tura babbar qofar dake part din farko ya shiga da sallama ta rufa masa baya.
"Zauna, bari nayi mata magana inaga tana sama" ya fada yana wucewa matakalar bene, seta nemi daya daga kujerun palour ta zauna tana bin ko ina da kallon.
Kayan cikin palour sun dan tsufa amma da yake masu kyau ne da asalin tsada ga kuma ingantacciyar tsafta da suke samu seya boye tsufan nasu. Ko ina qalqal se daukar ido yake ga qamshin turaren wuta daya hadu da sanyin Ac suka qarawa gurin nutsuwa ta musamman.
Babban Enlargement photo dake kafe a bangon palor ta ringa kallo, Wanda take kyautata zaton shine megidan tareda matar gidan se yaransu guda bakwai maza biyu mata biyar.
Kallon su take tanaso ta tuna inda tasan fuskar dan kusan duk kamar su daya sedai wasu sunfi wasu haske a ciki amma ta kasa tunawa.
Bataji sakkowarsu ba se maganar babbar mace da take cewa "Sannu da zuwa yammata"
Zamowa tayi daga kujerar tayi ta shiga gaisheta ta amsa mata cikin sakin fuska.
Kanta a qasa saboda kwarjinin da matar tayi mata ta miqa mata ledar tana cewa "gashi inji Maman Asad tace a kawo"
"Toh naman suna ne aka biyo mu dashi dukda bamu shiga ba? An gode Allah ya raya Ummu-salma, kice mata tayi haquri wallahi qafata ce ta motsa abinda ya hanani fitowa kenan amma in sha Allahu zanzo naga baby" Hajiyan ta fada kafin ta cigaba da cewa
"Qanwarta ce ko qanwar Habibu?"
"Qanwar tace ni" Umaimah ta bata amsa cikin qaguwa, to tambayar kuma ta mecece haka.
Ita kuwa Hajiya cikin son janta da hira ta ci gaba da cewa "Allah sarki ban taba ganinki ba, na dan san qannen nata kuma musamman Nuratu indai tazo takan shigo mu gaisa"
"Gwana uwar an cusai kenan, wato taga qaton gida har wani shiga take su gaisa Allah ya sawwaqawa Yaya Nuratu dai" Umaimah ta fada a ranta a fili kuwa tace
"Allah sarki ai Nuratun nake bi, nice autar su a Mata" se ta miqe tsaye
"Aa badai tafiya ba kuma muna cikin yar hirar mu, gashi ma ko ruwa baa kawo miki ba 'Habiba kina ina ne? Ki kawo mata ruwa" Hajiyan ta fada.
Se ta fara tafiya tana cewa "Aa wallahi babu komai Hajiya bari naje aiki mukeyi ne se an jima"
"Toh shikenan ki gaida gida na gode, se kin sake shigo mana ko, yaya sunan yar tawa?"
"Umaimah" ta bata amsa tana dan murmushi
"Toh Umaimah ki gaishe da Hajiyayyen nagode kinji" daga nan sukayi sallama ta fice kamar wadda take akan qaya.
Tana fita Khalil ya fito daga wata qaramar qofa ya canza kayan jikinsa zuwa dogon wadon jeans da T-shirt yanata zuba qamshi.
"Sannu Babana mutanen zazzau kunsha hanya amma kunyi sauri kamar wanda kuka taho a iska"
Seda yasha ruwan da aka kawowa Umaimah bata sha ba kafin yace "aikinsan yanzu hanya ta gyaru sunci qarfin aikin titin sosai shiyasa tafiyar take sauri kuma bamu zauna ba ana daura auran muka taho harda Amaryar dan a shirye suke suma"
"Masha Allahu Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana na yan baya lafiya, kana kallo dai daga sa'anninka gashi nan layi ya fara zuwa kan qannenka sun fara aje iyali kai ko kunya baka ji sedai kasa shadda ka tafi daurin aure ka kasa yunquri kai azo naka" Hajiya ta fara qorafin nata na kullum indai aka yi zancen aure.
Murmushi yayi ba tareda ya bata amsar maganar tata ba ya waiwaya yana duban palour yace "ta tafi kenan"
"Wacece?" Hajiyan ta tambaye shi, seda ya sake kurbar ruwa kafin yace
"Umaimah" shikansa se da yaji wani iri, yama akayi ya riqe sunanta?/yanda ya kira sunan seka rantse shiya rada mata shi.
"Tab, gaye iya gaye ashe gurgune" Nabila Sani ta fada tana kallon Khalil dake buga machine, tunda suka fito ta saka su zama a kujerun da suke kusa da Office din saboda harga Allah Khalil din ya tafi da imaninta, jira take ya fito tasan ta yanda zata yi masa magana se ga wannan big turn off din, ashe ma wankan ne kawai aljihu babu ko sisi.
"Arziqi nufin Allah ne, kuma dan kin ganshi da lifan shine aka ce miki matsiyaci ne wallahi Nabila ki dena abinda kike shiyasa har yau kika rasa ko wanda ze kiraki a waya ki rage dare" Umaimah data kalli Khalil din itama ta juya tana gayawa Nabila.
"Allahu akbar, Allah ka nuna mana Annabi, yau Umaimah ce takewa wani fadan yayi ba daidai ba lallai inda ranka kasha kallo" Halima ta fada cikin sigar tsokana dan daman ita gwanace.
"Se ku tashi mu tafi ai" Nabilan ta fada a fusace fuu tayi gaba suka rufa mata baya suna sake caccakarta.
Murmushi Khalil da duk abinda suka fada yaji yayi dan da dan qarfi suke maganar bayan haka yana da kunne sosai, Kallon Nasir yayi dake danna waya yace
"Nas kodai na shiga gurin nan ne, dagaske fa yarinyar nan tamun over taking"
"Abokina ka shiga kawai mana tsoron me kake ji, babu komai in sha Allahu tsamu tsaya maka kawai dai ka shirya ina qara gaya maka akwai daru" Nasir ya fada yana bashi hannu,
"Shikenan zanyi tunani akai" daga nan sukayi sallama ya buga mashin dinsa yayi gaba. A bakin get ya sake haduwa dasu suna jiran abin hawa, sukayi ido hudu da Umaimah ta kuwa murguda masa baki da harara yayi mata murmushi ya wuce abinsa.
Cikin taimakon Allah suka qare jarabawarsu tsaf saura jiran sakamako, ranar ansha hotuna anyi celebration, akwai Dinner da suka shirya yi an dade ana hada kudi daman dan harda anko suka fita Umaimah ta biya kudin komai amma bata jin zataje, tasan ma baza'a barta ba yanzu kuwa da take gudun laifi bazata fita babu izini ba. tunda suka fara jarabawa daman a faduwar gaban abinda yake gaba take, furucin Abba na idan bata fitar da Miji ba ze bada ita sadaka na bala'in damunta ta kuma rasa yanda zatayi.
Ta nemi shawarar Rumasa'u akan maganar tace mata tayita Addu'a kawao Allah ya yi mata zabi na gari, ta kuma ce mata ta gwada neman wanda taga hankalinta yafi kwantawa dashi cikin samarinta na baya ko Allah zesa a dace amma babu nasara.
Duk wanda tayi qoqarin bugun cikinsa akan batun aure zillewa suke, qiriqiri suke nuna mata suna sonta da gaske amma bazasu iya da halinta ba wannan abin na bala'in qona mata rai, ita wane hali ne da ita?
Shin laifi ne dan kayi kishin abinda kake so su ba abin alfaharin su bane ma ace ana kishin su?
Kusan sati da gama makarantar su babu wanda yace mata qala akan batun aure, ba kamar baya ba yanzu komai ya dawo daidai a gidan itace ma take dararewa wani lokacin saboda gudun kar a diro mata da maganar fito da Miji katsahan. Fita ce dai aka hanata, dan ko Islamiyyar da take zuwa Asabar da Lahadi ma Abban ya soke yace yawo ne kawai, daidai gwargwado ta samu ilimi ta zauba agida tayita tilaqar abinda ta sani amma fita indai bada dalili me qarfi ba be yarda ba.
Ana haka Yayarsu Anty Hajiyayye ta haihu, dayake CS akayi mata da farko akace a dawo da ita gida ta zauna idan jikinta ya warware seta koma tunda a can babu mataimaki ga yara kuma amma Abban su yaqi, daga qarshe dai dakyar Mama ta lallabashi akan tunda Umaimah bata komai taje ta zauna mata tareda wata mata da aka samu har zuwa sanda zata warware.
Seda ya kafa mata warning sosai ya kuma jawa Hajiyayyae kunne akan duk in yaji ba daidai ba se ranta yafi na kowa baci haka ta tattara ta tafi gidan Yaya Hajiyayyen.
Washe garin suna da yake ba taro sukayi ba bayan an gama suyar nama an kasa Yaya Hajiyayye ta bata tace ta shiga gidan da yake kallon nasu takai.
Dogon Hijabi har qasa ta dora akan Doguwar rigar material din jikinta fuskar nan kamar ko yaushe babu ko digon kwalli akan ta amma da yake kyanta daga Allah ne se gata ta fito shar abin ta.
Tun daga wajen gidan ta tabbatar da gidan masu arziqi ne, idan ma a yanzu babu to tabbas da an samu ta tura qofar get din da take a bude ta shiga qaton compound din gidan da sallama. Babu kowa a tsakar gidan, taja ta tsaya ganin qofofi biyu ne manya bata san wanne ne ta shiga ba, gashi ma ta manta ta tambayeta wa zaa kaiwa dan qila mata biyu ne a gidan.
Daga bayanta taji ance
"Ya kika tsaya? Bismillah ki shiga suna ciki" seta juya a firgice dan bataji takun takalma ba se magana kawai, ido hudu sukayi da Khalil dake tsaye a bayanta yasha wanka da wata danyar Shadda Fara gurin gaba daya ya karade da Qamshin turarensa.
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR🥰👹 (ALKHAIRI CE KO SHARRI)*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH AND NOW*
*HALIN KISHI*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE NAIRA 500*
*GA DUK ME SO ZE TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHEDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
Free page 4
Ya ganeta, amma da alama it bata gane shi ba tace,qasa qasa ta harareshi tace
"Ka tsorata ni wallahi, kuma bansan qofar shigan ba. Daga gidan Maman Asad nake ta bada naman suna a kawowa Hajiya" ta qarasa tana miqa masa ledar Naman. Se yayi gaba yana cewa
"Muje na nuna miki"
Tsabar neman magana irin nata bibsa take a baya tana kwaikwayon tafiyar sa da yake yi cikin nutsuwa kamar me qirga takunsa. Gulmarsa take a zuciya tana cewa
"Ji yanda yake wani yanga dan Allah kamar mace ya ware qafa yayi sauri Aa se batamun lokaci yake" a haka ya tura babbar qofar dake part din farko ya shiga da sallama ta rufa masa baya.
"Zauna, bari nayi mata magana inaga tana sama" ya fada yana wucewa matakalar bene, seta nemi daya daga kujerun palour ta zauna tana bin ko ina da kallon.
Kayan cikin palour sun dan tsufa amma da yake masu kyau ne da asalin tsada ga kuma ingantacciyar tsafta da suke samu seya boye tsufan nasu. Ko ina qalqal se daukar ido yake ga qamshin turaren wuta daya hadu da sanyin Ac suka qarawa gurin nutsuwa ta musamman.
Babban Enlargement photo dake kafe a bangon palor ta ringa kallo, Wanda take kyautata zaton shine megidan tareda matar gidan se yaransu guda bakwai maza biyu mata biyar.
Kallon su take tanaso ta tuna inda tasan fuskar dan kusan duk kamar su daya sedai wasu sunfi wasu haske a ciki amma ta kasa tunawa.
Bataji sakkowarsu ba se maganar babbar mace da take cewa "Sannu da zuwa yammata"
Zamowa tayi daga kujerar tayi ta shiga gaisheta ta amsa mata cikin sakin fuska.
Kanta a qasa saboda kwarjinin da matar tayi mata ta miqa mata ledar tana cewa "gashi inji Maman Asad tace a kawo"
"Toh naman suna ne aka biyo mu dashi dukda bamu shiga ba? An gode Allah ya raya Ummu-salma, kice mata tayi haquri wallahi qafata ce ta motsa abinda ya hanani fitowa kenan amma in sha Allahu zanzo naga baby" Hajiyan ta fada kafin ta cigaba da cewa
"Qanwarta ce ko qanwar Habibu?"
"Qanwar tace ni" Umaimah ta bata amsa cikin qaguwa, to tambayar kuma ta mecece haka.
Ita kuwa Hajiya cikin son janta da hira ta ci gaba da cewa "Allah sarki ban taba ganinki ba, na dan san qannen nata kuma musamman Nuratu indai tazo takan shigo mu gaisa"
"Gwana uwar an cusai kenan, wato taga qaton gida har wani shiga take su gaisa Allah ya sawwaqawa Yaya Nuratu dai" Umaimah ta fada a ranta a fili kuwa tace
"Allah sarki ai Nuratun nake bi, nice autar su a Mata" se ta miqe tsaye
"Aa badai tafiya ba kuma muna cikin yar hirar mu, gashi ma ko ruwa baa kawo miki ba 'Habiba kina ina ne? Ki kawo mata ruwa" Hajiyan ta fada.
Se ta fara tafiya tana cewa "Aa wallahi babu komai Hajiya bari naje aiki mukeyi ne se an jima"
"Toh shikenan ki gaida gida na gode, se kin sake shigo mana ko, yaya sunan yar tawa?"
"Umaimah" ta bata amsa tana dan murmushi
"Toh Umaimah ki gaishe da Hajiyayyen nagode kinji" daga nan sukayi sallama ta fice kamar wadda take akan qaya.
Tana fita Khalil ya fito daga wata qaramar qofa ya canza kayan jikinsa zuwa dogon wadon jeans da T-shirt yanata zuba qamshi.
"Sannu Babana mutanen zazzau kunsha hanya amma kunyi sauri kamar wanda kuka taho a iska"
Seda yasha ruwan da aka kawowa Umaimah bata sha ba kafin yace "aikinsan yanzu hanya ta gyaru sunci qarfin aikin titin sosai shiyasa tafiyar take sauri kuma bamu zauna ba ana daura auran muka taho harda Amaryar dan a shirye suke suma"
"Masha Allahu Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana na yan baya lafiya, kana kallo dai daga sa'anninka gashi nan layi ya fara zuwa kan qannenka sun fara aje iyali kai ko kunya baka ji sedai kasa shadda ka tafi daurin aure ka kasa yunquri kai azo naka" Hajiya ta fara qorafin nata na kullum indai aka yi zancen aure.
Murmushi yayi ba tareda ya bata amsar maganar tata ba ya waiwaya yana duban palour yace "ta tafi kenan"
"Wacece?" Hajiyan ta tambaye shi, seda ya sake kurbar ruwa kafin yace
"Umaimah" shikansa se da yaji wani iri, yama akayi ya riqe sunanta?/yanda ya kira sunan seka rantse shiya rada mata shi.