Sashe 126
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
KHALIL
Kiransa Hajiya tayi ta rufeshi da fada ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba taqi bashi ko damar ya gaisheta har seda ta kao aya kafin ta kashe wayarta, yasan baze wuce Umaimah taje ta gaya mata qarya da gaskiyar data saba bane shine zata hau kansa ba tareda shi taji ta bakinsa ba haka ya tashi shirin tahowa dan ce masa tayi ko ya dawo ko Umaiman ta bishi shi kuwa daman ba zaman wani abu yake ba aikin ma da suke gaba daya an kusa kammalashi kuma ya gama bangarensa tuntuni kawai wasu harkokin kasuwanci ya sake samu a can da taimakon wani Co-Architect da sukayi aiki tare shi ya nuna masa hanya ta irin abubuwan da suke tafiya a can wanda basu dashi se an shigar musu daga wasu qasashenda kuma namu na nan da suke da sauqi acan nan da nanya fantsama harkar shigowa da fitar da kayayyaki kuma da Allah ya saka albarka a abin yana ganin haske, ga harkar Gold da yake da sauqi sosai a can, sunq ulla Bashir, danye yake siya su kai Dubai a canza shi zuwa abubuwa da dama wannan hidimomin ne suka dauke masa hankali gaba daya har mamakin kansa yake ta yanda ya iya share tsahon lokacin ba tareda Mace ba kuma baya jin wata damuwa kodanbaya kawo abin a ransa ne yana fushi dame abun sabanin da da ko muryarta yaji yanzu jikinsa ze amsa?
Shidakansa yasan zazzafar soyayar da yakewa Umaimah ta dishashe ba kuma ya zaton zata sake samun matsayi irin wanda take dashi a da cikin zuciyarsa ta rigada ta barar da damarta.
Ranar Lahadi kamar yanda ya fada qarfe sha biyun Rana tayi masa a gidan Hajiya. Dakyar ta barshi yayi sallar Azahar banda ruwa ba abinda yasha ta korashi wanda be so haka ba, so yayi ko ze koma gidan se cikin dare amma haka ya tafi yana ta doka tsaki Mu'ayyad nata kukan ze bishi aka lallabashi da kyar akan se an kwana biyu za'a maida musu shi. A Mota Khalifa dai sedai ya juya ya kalle shi ya dauke kai, tunawa yakeyi lokuta baya idan yayi tafiya ya dawo yanda yake doki da zumudin komawa gidan ya ringa Azalzalarsa da yayi sauri kenan amma yau har fada yake masa wai yana gudu da motar. Har cikin gidan ya shigar masa da mota ya fita yayi masa sallama ba tareda ya tsaya sun gaisa da Umaimah ba.
Numfashi yaja ya fitar kansa na kallon qofar palour da aka liqa wata sticker me qyalqyali an rubuta
'WELCOME HOME HABIBI" A jiki. Waiwayawa yayi ya kalli qaramin compound din da yayi qal Interlocks se daukar ido suke alamar sunsha shara da wanki ga wani daddadan qamshi turaren wuta da yake tashi kamar anyi barinsa a gurin. Da sallama ya tura qofar palour ya shiga, wani qamshi, sanyi, nutsuwa da ya rasa ta mecece suka bige shi lokaci daya, cikin seconds goma ya qarewa palour da babu kowa a ciki kallo. Gyaranda akayi masa is morethan perfect, yanda kasan babu wanda yake rayuwa a ciki saboda yanda komai ya zauna daidai a muhallindaya dace dashi haka ya fara jefa qafafunsa yana tafiya duk taku daya yana jin wata kewar gidanna kama shi, gaskiya masu magana sunyi gaskiya da suka ce no place like home.
Qofar dakinsa ya tura kai tsaye ya shiga da sallama a bakinsa, wani sabon qamshi na daban yayi masa maraba tareda fuskar kyakykyawar Diyarsa dake kwance akan gadon daya sha shimfida ta alfarma itama cikin irin shigar da yake so ya gani jikin yara kamar ta sanshi suna hada ido ta bangale masa bakinta da babu haqori ta qara qarfin gwalantoyin da takeyi daga kwancen. Be san sanda ya dire jakar hannunsa ya isa kan gadon ya dagata ba ya hadeta da qirjinsa yana kissing fuskarta ita kuwa se dariya take abinta.
Umaimah ta bude qofar bandakin da ta shiga tana hada masa ruwan wanka saboda Habiba ta kira ta gaya masa gashi nan a hanya ya baro gidan Hajiya. Daskarewa tayi daga bakin qofar, So, shauqi tareda kewarsa suka shiga shawagi da ita a sararin samaniyar qauna bata san yanda akayi ba se ganin kanta tayi a bayansa ba kuwa ta tsaya tunanin komai ba ta saka hannuwa biyu ta zagaye cikinsa dasu kafin ta dora kanta a bayansa se ji tayi hawaye suna bin kuncinta da ita kanta bata san na menene ba.
A bazata abun yazo masa dan sam beji fitowarta daga bandakin ba gaba daya hankalinsa nakan Yar Babyn tasa da yake jin qaunarta har qololuwa, da yanzu Umaimah ta salwantar masa da ita tab da kuwa ta cuce shi. Saukar hannun mutum kawai yaji a cikinsa se saukar abi me dumi da yatabbatar hawayene ya shiga ratsa jini da jijiyarsa har zuwa cikin bargonsa, sosai yayi ta maza ya dake ya kuma hana kansa juyowa dan yasan tarko ne, idan har ya bari tayi tasiri akansa shikenan duk wani shiri daya dawo dashi ya wargatse.
Hannu daya ya saka dayan na rungume da Bibi ya janye hannayen Umaimah data zagaye shi dasu ya fara takawa zuwa gana kujerar dake cikin dakin ya ajiye yarinyar ya shiga zame rigar coat din daya dora, hannunta ya sake ji a kafadarsa tana taya shi, kafin muryarta da tayi wani irin laushi da sanyi ta ratsa dodon kunnensa tana cewa
"Barka da zuwa Habibin Umaimah, banji shigowarka ba ina ciki ina hada maka ruwan wanka, u are highly welcome" ta qarasa cikin wani sauti daya sakashi saurin sakar mata rigar ta qarasa cireta kafin ta juyo ta shiga balle masa maballin farar yar cikin jikinsa suka shiga kallon juna ido cikin ido kowanne yana karantar tsantsar kewar sa cikin idon Dan uwansa, tana gama balle masa rigar be zata ba yajita cikin jikinsa gaba daya suka yi baya ya samu ya dafe kujerar gabansu tareda qanqameta yana qarewa fuskarta kallo data sha simple kwalliyar nan tata wato pawder da man lebe ta gyara kyawawan idanunta da kwalli da Mascara gashin idon sun qara tsaho da baqi.
Lumshe idonta tayi ta sake bude su akan sa kafin ta raba labbanta data pente da jan lipstick ta sake shafe su Lipbalm me maiqo se daukar ido sukeyi tayi kamar zatayi magana amma ba tace komai ba, Idan yace yace beji wani abu na yayi qary, wani sanyi yaji ya taso masa tun daga tafin qafa ya dire a kwakwalwarsa, wani irin kallo take masa na cikin ido dashi kadai yasan ma'anarsa kuma ji yakeyi tamkar ta saka muqulli tana bude duk wasu qofofin jikinsa da suka jima a rufe, numfashinta da yaji cikin nasa kafin ta kai ga aikata abinda ta niyyata zumbur ya tashi tareda ita a jikinsa, sauketa yayi a qasa kan qafafunta kafin ya juya ya shige bandaki yanajin yanda jikinsa yake harbawa ba tareda ya qarasa cire kayan jikinsa ba ya sakarwa kansa ruwan sanyi yana gangarowa daga gashin kansa har zuwa qafafunsa.
Bazece ga iya adadadin mintinan daya kwashe a qasan ruwan ba, gajiya yayi dan a maimakon ya samu sauqin abinda yake ji se ya zamana tamkar ma yana qara iza wutar ne. Cikin ruwan data hada masa a bahon wankaya shiga bayan da ya cire jiqaqqun kayan jikinsa ya kwanta a ciki tareda rufe idonsa so yake ya tunano duk tarin laifukan da tayi masa ko zasu dishashe abinda yake bijiro masa akanta amma abin takaici ko daya yaqi zuwa, idan ma sunzo sam sun gagara bata masa rai ballantana har su gushe kaifin abinda yake ji qarshe dai yayi wanka ya dauro towel din data rataye masa ya fito.
UMAIMAH
Da kallo ta rakashi harya shiga ya kullo qofar kafin ta sauke ajiyar zuciya ta zauna kusada Bibi dake ta wulga idanu tana kallon fitilar dakin. Gaba daya jiki ta yayi mugun sanyin da batajin zata ko iya tafiya, abinda ta hango cikin idonsa ya sake sare mata guiwoyi, dagaske ne Khalil ya tsaneta ya zatayi da ranta?
Tana nan zaune cikin duniyar Lissafi har ya kwashe mintocinsa ya fito daure da towel a qugunsa, Kallo ta bishi dashi kamar wata tsohuwar mayya, ya wuceta ya dauki wayarsa dake kan gado kafin ya koma gaban mudubi yaja kura ya zauna bayan dayayi yan danne danne a wayar ya saka a speaker
"Kaje Ten to Ten ka karbo mun usually meal dina yanzu" ya fada kafin ya latse wayar ya janyo Mansa ya fara shafawa.
Hadiye abinda ya tsaya mata a wuya tayi ta tashi dakyar ta isa kusa dashi, ta cikin mudubin yake qare mata kallo, doguwar fitted gown din data saka ta Dark Orange din Lace tayi bala'in yi mata kyau ta fito da duk wani tudu da komadar jikinta daya qara cika dam kamar zata fashe, saurin dauke kansa yayi sanda ta iso ta karbi Man daya diba ta shiga shafa masa a banyansa, daga shi har itan ba zasu misalta yanda sukeji ba, Ta gaka shafa masa a bayan ya juyo tana fuskantarsa, hannu biyu ta saka taja shafa masa man A fuskarsa da tasa gyara saboda jiya yayi Aski cikin muryarta da tayi rauni kamar zatayi Kuka tace
"Nayi maka abinci, kuma naji kana cewa a kawo maka"
"Oh, thanks" ya fada yana miqewa saboda ya tabbata idan ta sake bude baki tayi magana cutarsa kawia zatayi. Wardrobe ya bude ya dauko Jallabiyya da boxer ya saka ya sake dawoa inda take tsaye ya dauki turare ya fesa kafin ya juya ya dauki Bibi data bingire da bacci ya fice daga dakin.
Kiransa Hajiya tayi ta rufeshi da fada ta inda ta shiga ba ta nan take fita ba taqi bashi ko damar ya gaisheta har seda ta kao aya kafin ta kashe wayarta, yasan baze wuce Umaimah taje ta gaya mata qarya da gaskiyar data saba bane shine zata hau kansa ba tareda shi taji ta bakinsa ba haka ya tashi shirin tahowa dan ce masa tayi ko ya dawo ko Umaiman ta bishi shi kuwa daman ba zaman wani abu yake ba aikin ma da suke gaba daya an kusa kammalashi kuma ya gama bangarensa tuntuni kawai wasu harkokin kasuwanci ya sake samu a can da taimakon wani Co-Architect da sukayi aiki tare shi ya nuna masa hanya ta irin abubuwan da suke tafiya a can wanda basu dashi se an shigar musu daga wasu qasashenda kuma namu na nan da suke da sauqi acan nan da nanya fantsama harkar shigowa da fitar da kayayyaki kuma da Allah ya saka albarka a abin yana ganin haske, ga harkar Gold da yake da sauqi sosai a can, sunq ulla Bashir, danye yake siya su kai Dubai a canza shi zuwa abubuwa da dama wannan hidimomin ne suka dauke masa hankali gaba daya har mamakin kansa yake ta yanda ya iya share tsahon lokacin ba tareda Mace ba kuma baya jin wata damuwa kodanbaya kawo abin a ransa ne yana fushi dame abun sabanin da da ko muryarta yaji yanzu jikinsa ze amsa?
Shidakansa yasan zazzafar soyayar da yakewa Umaimah ta dishashe ba kuma ya zaton zata sake samun matsayi irin wanda take dashi a da cikin zuciyarsa ta rigada ta barar da damarta.
Ranar Lahadi kamar yanda ya fada qarfe sha biyun Rana tayi masa a gidan Hajiya. Dakyar ta barshi yayi sallar Azahar banda ruwa ba abinda yasha ta korashi wanda be so haka ba, so yayi ko ze koma gidan se cikin dare amma haka ya tafi yana ta doka tsaki Mu'ayyad nata kukan ze bishi aka lallabashi da kyar akan se an kwana biyu za'a maida musu shi. A Mota Khalifa dai sedai ya juya ya kalle shi ya dauke kai, tunawa yakeyi lokuta baya idan yayi tafiya ya dawo yanda yake doki da zumudin komawa gidan ya ringa Azalzalarsa da yayi sauri kenan amma yau har fada yake masa wai yana gudu da motar. Har cikin gidan ya shigar masa da mota ya fita yayi masa sallama ba tareda ya tsaya sun gaisa da Umaimah ba.
Numfashi yaja ya fitar kansa na kallon qofar palour da aka liqa wata sticker me qyalqyali an rubuta
'WELCOME HOME HABIBI" A jiki. Waiwayawa yayi ya kalli qaramin compound din da yayi qal Interlocks se daukar ido suke alamar sunsha shara da wanki ga wani daddadan qamshi turaren wuta da yake tashi kamar anyi barinsa a gurin. Da sallama ya tura qofar palour ya shiga, wani qamshi, sanyi, nutsuwa da ya rasa ta mecece suka bige shi lokaci daya, cikin seconds goma ya qarewa palour da babu kowa a ciki kallo. Gyaranda akayi masa is morethan perfect, yanda kasan babu wanda yake rayuwa a ciki saboda yanda komai ya zauna daidai a muhallindaya dace dashi haka ya fara jefa qafafunsa yana tafiya duk taku daya yana jin wata kewar gidanna kama shi, gaskiya masu magana sunyi gaskiya da suka ce no place like home.
Qofar dakinsa ya tura kai tsaye ya shiga da sallama a bakinsa, wani sabon qamshi na daban yayi masa maraba tareda fuskar kyakykyawar Diyarsa dake kwance akan gadon daya sha shimfida ta alfarma itama cikin irin shigar da yake so ya gani jikin yara kamar ta sanshi suna hada ido ta bangale masa bakinta da babu haqori ta qara qarfin gwalantoyin da takeyi daga kwancen. Be san sanda ya dire jakar hannunsa ya isa kan gadon ya dagata ba ya hadeta da qirjinsa yana kissing fuskarta ita kuwa se dariya take abinta.
Umaimah ta bude qofar bandakin da ta shiga tana hada masa ruwan wanka saboda Habiba ta kira ta gaya masa gashi nan a hanya ya baro gidan Hajiya. Daskarewa tayi daga bakin qofar, So, shauqi tareda kewarsa suka shiga shawagi da ita a sararin samaniyar qauna bata san yanda akayi ba se ganin kanta tayi a bayansa ba kuwa ta tsaya tunanin komai ba ta saka hannuwa biyu ta zagaye cikinsa dasu kafin ta dora kanta a bayansa se ji tayi hawaye suna bin kuncinta da ita kanta bata san na menene ba.
A bazata abun yazo masa dan sam beji fitowarta daga bandakin ba gaba daya hankalinsa nakan Yar Babyn tasa da yake jin qaunarta har qololuwa, da yanzu Umaimah ta salwantar masa da ita tab da kuwa ta cuce shi. Saukar hannun mutum kawai yaji a cikinsa se saukar abi me dumi da yatabbatar hawayene ya shiga ratsa jini da jijiyarsa har zuwa cikin bargonsa, sosai yayi ta maza ya dake ya kuma hana kansa juyowa dan yasan tarko ne, idan har ya bari tayi tasiri akansa shikenan duk wani shiri daya dawo dashi ya wargatse.
Hannu daya ya saka dayan na rungume da Bibi ya janye hannayen Umaimah data zagaye shi dasu ya fara takawa zuwa gana kujerar dake cikin dakin ya ajiye yarinyar ya shiga zame rigar coat din daya dora, hannunta ya sake ji a kafadarsa tana taya shi, kafin muryarta da tayi wani irin laushi da sanyi ta ratsa dodon kunnensa tana cewa
"Barka da zuwa Habibin Umaimah, banji shigowarka ba ina ciki ina hada maka ruwan wanka, u are highly welcome" ta qarasa cikin wani sauti daya sakashi saurin sakar mata rigar ta qarasa cireta kafin ta juyo ta shiga balle masa maballin farar yar cikin jikinsa suka shiga kallon juna ido cikin ido kowanne yana karantar tsantsar kewar sa cikin idon Dan uwansa, tana gama balle masa rigar be zata ba yajita cikin jikinsa gaba daya suka yi baya ya samu ya dafe kujerar gabansu tareda qanqameta yana qarewa fuskarta kallo data sha simple kwalliyar nan tata wato pawder da man lebe ta gyara kyawawan idanunta da kwalli da Mascara gashin idon sun qara tsaho da baqi.
Lumshe idonta tayi ta sake bude su akan sa kafin ta raba labbanta data pente da jan lipstick ta sake shafe su Lipbalm me maiqo se daukar ido sukeyi tayi kamar zatayi magana amma ba tace komai ba, Idan yace yace beji wani abu na yayi qary, wani sanyi yaji ya taso masa tun daga tafin qafa ya dire a kwakwalwarsa, wani irin kallo take masa na cikin ido dashi kadai yasan ma'anarsa kuma ji yakeyi tamkar ta saka muqulli tana bude duk wasu qofofin jikinsa da suka jima a rufe, numfashinta da yaji cikin nasa kafin ta kai ga aikata abinda ta niyyata zumbur ya tashi tareda ita a jikinsa, sauketa yayi a qasa kan qafafunta kafin ya juya ya shige bandaki yanajin yanda jikinsa yake harbawa ba tareda ya qarasa cire kayan jikinsa ba ya sakarwa kansa ruwan sanyi yana gangarowa daga gashin kansa har zuwa qafafunsa.
Bazece ga iya adadadin mintinan daya kwashe a qasan ruwan ba, gajiya yayi dan a maimakon ya samu sauqin abinda yake ji se ya zamana tamkar ma yana qara iza wutar ne. Cikin ruwan data hada masa a bahon wankaya shiga bayan da ya cire jiqaqqun kayan jikinsa ya kwanta a ciki tareda rufe idonsa so yake ya tunano duk tarin laifukan da tayi masa ko zasu dishashe abinda yake bijiro masa akanta amma abin takaici ko daya yaqi zuwa, idan ma sunzo sam sun gagara bata masa rai ballantana har su gushe kaifin abinda yake ji qarshe dai yayi wanka ya dauro towel din data rataye masa ya fito.
UMAIMAH
Da kallo ta rakashi harya shiga ya kullo qofar kafin ta sauke ajiyar zuciya ta zauna kusada Bibi dake ta wulga idanu tana kallon fitilar dakin. Gaba daya jiki ta yayi mugun sanyin da batajin zata ko iya tafiya, abinda ta hango cikin idonsa ya sake sare mata guiwoyi, dagaske ne Khalil ya tsaneta ya zatayi da ranta?
Tana nan zaune cikin duniyar Lissafi har ya kwashe mintocinsa ya fito daure da towel a qugunsa, Kallo ta bishi dashi kamar wata tsohuwar mayya, ya wuceta ya dauki wayarsa dake kan gado kafin ya koma gaban mudubi yaja kura ya zauna bayan dayayi yan danne danne a wayar ya saka a speaker
"Kaje Ten to Ten ka karbo mun usually meal dina yanzu" ya fada kafin ya latse wayar ya janyo Mansa ya fara shafawa.
Hadiye abinda ya tsaya mata a wuya tayi ta tashi dakyar ta isa kusa dashi, ta cikin mudubin yake qare mata kallo, doguwar fitted gown din data saka ta Dark Orange din Lace tayi bala'in yi mata kyau ta fito da duk wani tudu da komadar jikinta daya qara cika dam kamar zata fashe, saurin dauke kansa yayi sanda ta iso ta karbi Man daya diba ta shiga shafa masa a banyansa, daga shi har itan ba zasu misalta yanda sukeji ba, Ta gaka shafa masa a bayan ya juyo tana fuskantarsa, hannu biyu ta saka taja shafa masa man A fuskarsa da tasa gyara saboda jiya yayi Aski cikin muryarta da tayi rauni kamar zatayi Kuka tace
"Nayi maka abinci, kuma naji kana cewa a kawo maka"
"Oh, thanks" ya fada yana miqewa saboda ya tabbata idan ta sake bude baki tayi magana cutarsa kawia zatayi. Wardrobe ya bude ya dauko Jallabiyya da boxer ya saka ya sake dawoa inda take tsaye ya dauki turare ya fesa kafin ya juya ya dauki Bibi data bingire da bacci ya fice daga dakin.