← Book details Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 140 OF 267

Sashe 140

Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ko gamo tayi? Amma haka kawai ace yarinya ta fito da gudu ai abin dubawa ne" Anty Laure ta fada tana hararar Hajiya qasa qasa dan tunda sukazo ta tarar da Umaiman ita kadai ranta ya baci. Ya za'ayi su kawo yarinya Asibiti subarta ita kadai tun jiyan ai se suyi waya gidansu a zo idan su bazasu iya zama da ita ba.
"Uhm" kawai Nuratu tace dan Maman Asad ta gaya mata yanda sukayi da Umaiman ta kuma tabbatar baze wuce akan zancen bane take tashin hankali, ai shikenan, idan ta kashe kanta a banza kowa ya huta.
Se bayan Azahar ta sake farkawa, kuka ta ringayi saboda radadin da hannayenta data yanke da kwalabe suke mata saboda Allurar da akayi mata ta saketa ta kuma ida dawowa hayyacinta gaba daya. Seda ta kwana biyu a Asibiti Anty Laure ce tareda ita take jinyarta kafin aka sallameta ta koma gida da gargadin karta kuskura ta ringa abinda ze jigata jikinta.

Da farko ma gida Anty Laurentace ko zasu wuce da ita Mama tace Aa ta barta ta koma dakinta idan yaso ta bita ta qara mata kwana biyu kafin a samo mata me aiki tunda iya hidimar aikin gida ce yara dabdalarsu duk a gurin Hajiya sukeyi bata da matsala dasu. haka kuwa akayi suka wuce gidan da Anty Laure washe gari se ga me aiki Nuratu ta kai mata yar uwar me aikintace tana jin dadin zama da ita sosai shiyasa tayi mata magana idan da wata tace akwai yar uwarta babbace a qalla zatayi shekara Arba'in Mininta ne ya rasu amma bata taba haihuwa ba daman tun tana Asibiti sukayi maganar ba'a yi shawara da ita ba dan sun san ma ba zata yarda ba se ganinta kawai tayi.

A cikin Bedrooms din qasa Umaiman ta koma daya ita da Anty Lauren saboda hawa da saukan baze yuwu ba saboda yanayin jikinta ga dakinta data rigada ta sauyawa Kamanni Khalil yasa an fitar da Furnitures din dukka dan ta lalata su, rabi Glass ne kuma ta rusa shi dole sedai a chanza wasu. Sanda Anty laure ta shiga dakin debo mata kayayyakinta riqe baki kawai tayi cikin mamaki ganin se Gado kawai ba komai a dakin kayan sawarwa ma an juye su akan gadon haka ta tsinto abinda zata iya ta sauka qasa tana wassafa abinda ya faru a gidan. Daman tun tana Asibiti ta lura sam da wata a qasa tsakaninta da Mijin nata.

Idan yazo baya wani dadewa yake tafiya kuma ko magana bata hadasu sedai su ya musu yame jiki ya qara gaba haka tunda suka dawo yau kwana hudu safe da yamma ze shiga ya gaidata ya duba Umaiman amma ko kallon arziqi taga baya hadasu. Ta qyaleta ne batayi mata magana ba taga iya gudun ruwansu amma har sukayi sati babu abinda ya canza Khalil dinma baya nan ya tafi Zamfara daze tafi ma ita yayiwa sallama ya bata kudi ya kuma gaya mata idan buqatar komawa Asibiti ta tashi Khalifa yana nan.
Hajiya ma kullum safe da yamma aeta shiga ta dubata su dan taba hira da Anty Lauren.

Kwana uku tafiyar da yayi ta dauke shi ya dawo cike da farin ciki saboda samun kiran da yayi daga Dr Sabitu akan gobe yaje da sauran takaddun kwangila ya saka masa hannu za'a tura masa da kudi ya fara aiki. Dawowar safe yayi, cikinfara'a ya shiga gidan, suka gaisa da sabuwar me aikin me suna Ruqayya ya tambayeta Anty Laure tace taje gida wai surukarta ce bata lafiya Maman Mijinta marigayi kuma jikin yayi tsanani shine taje dubata a Asibiti amma bazata jima ba.

Dakin da Umaimah ta koma ya tura a hankali ya shiga da sallama. Tana zaune ta jingina bayanta da Gado da waya a kunnenta tana magana ta dago tayi masa kallo daya ta mayar dakai taci gana da maganarta. Fuskarsa har sannan dauke da murmushi ya zauna a gefenta saboda tsokana harda kai hannu ya shafi gefen fuskarta. Yayi missing dinta sosai amma nisantar ta da yayi shine maslaha hat zuwa sanda ze kammala abinda yake gabansa gashi kiwa komai yazo qarshe.

Yafi minti goma a zaune yana jiranta amma taqi kashe wayar, yi tayi tamkar ma bata san da wanzuwarsa a dakin ba seda ya gaji ya saka hannu ya zare wayar daga kunnenta ta juyo a fusace tace
"Malam meye haka? Kana da matsala dani ne da zaka shiga rayuwata ko yaya?"

"Yi haquri maida wuqar naga kamar baki san da zamana bane shiyasa ki bari mu gaisa se kici gaba da wayar taki ko" ya fada yana murmushi se kuwa ta galla masa harara ta miqe tana jan qwafa, miqewar yayi shima yana kama kafadunta ta baya ya rungumeta yana cewa
"Wai fushin ne har yanzu baki dena ba?"
"Wallahi Khalil ka fita a sabgata kafin nayi maka rashin mutunchi, badai aure kace zakayi ba? To mu zuba nidakai a gidan nan shege ka fasa" Umaimah ta fada a fusace tana fuzge jikinta se yayi saurin sakinta yana cewa
"Easy Ma, duk da kin kwantar da hankalinki zancen auran nan fa wasa ne. Da kin haqura dakaina zanyi miki bayanin komai amma kima shiga tashin hankali yanzu kalli abinda kika jawa kanki"

Kallonsa tayi da son jin qarin bayanin wasan da yace maganar auran. Khalil ya daga mata gira kafin yace
"Yes, wasa ne, idan kina so kiji komai kizo muje dakina nayi wanka na huta zan warware miki yanda abun yake". Numfashi ta sauke har sannan tana kallonsa, idan kuma wasa yake so ya qarayi da hankalinta fa? Zuciyarta ta raya mata.

"Muje" ya katse mata tunanin, se kuwa ta bishi kamar wata sokuwa seda sukaje gaban matakalar ta tsaya tana kallonsa tace
"Likita yace karna hau bene"
"Ohk" ya sakw fada kafin ya shiga nade hannun rigar jikinsa. Cak ya dagata cikin takatsantsan ya fara hawa saman da ita be direta ko ina ba se kan gadon dakinsa ya ajiyeta tareda saka mata pillow a bayanta yana mata murmushi ya wuce bandaki.

Tana jiyo qarar saukar ruwa alamar wanka yake ta dannawa Safina kira.
"Ki tsaya kiji abinda zw fada amma dukda haka bazamu fasa wannan plan dinba dan kin ganni ma na kusa layin nasu amma bari na shiga gidan Hadiza Sani na jira muji abinda zece miki" Safinan ta fada bayan data gaya mata yanda sukayi da Khalil. Sun gama tsarawa daman Safina zataje gidansu Zahran tayi tijara ta yanda da kansu zasu fasa bashi auran yar tasu tunda ita jikinta baze bari ta fita ba amma zata dakata taji rainin wayom da ze mata yanzu kafin su aiwatar da nufinsu.

Da kansa ya sauka qasa ya soyo kwai ya hada shayi kafin ya dawo dakin Umaimah data qagu da jira se tsaki takeyi. Dole ta sakata zama inuwa daya dashi dan bala'in haushinsa take ji. Da yayi mata tayin shayin ma harara ta maka masa yayi dariya ya shanye abinsa seda ya gama tas kafin ya dauko Laptop dinsa ya hawo kan gadon da take yana murmushi ya bude.

Wasu hotuna ya shiga bude mata, Taswirar gini ce kamar Kasuwa kamar kuma gidaje ita dai bata wani gane ba saboda yanayin ginin anyi shi rututu gasu nan in ma gidajene sunfi dari seta dago tana cewa
"Nifa ba wannan tasa na zauna jiranka ba tam" ta qarasa tana zumbura baki. Dariya yayi ya koma ta bayanta ya raba qafarsa ya zamana tana tsakiyarsa. Kwantar da fuskarsa yayi a gadon bayanta yace
"My troublesome lover" kafin ya kama hannunta biyu cikin nashi ya shiga labarta mata yanda ya hadu da Zahra har zuwa yarjejeniyar da sukayi da Mahaifinta zuwa kiran da yayi masa na yau ya qarashe da cewa
"Kinga daya saka mun hannu kudi sun shigo shikenan babu ni babu yarsa, daman na yarda ne saboda na samu Kwangilar tunda bayayin abu dan Allah kinga ai idanna yaudare shi nima banyi laifi ba dan Yarsa ba type dina bace kuma ko aure zanyi babu abinda zanyi da sangartacviyar yarinya irinta. Sam bata da Class taya ya ma Mace daga ganin Namiji kawai kice kina sonsa sanna kinga irin rawar jiki da nacin da take mun kuwa? Nooo na raina ajinta bazan iya auranta ba".

Gaba daya surutun da yakewa Umaimah tamkar suna shiga ta kunnen dama ne suna bullewa ta hagu, banda ma ya raina mata wayo wato saboda yana neman abu a gurin Mahaifinta yasa ya yarda ze aureta yanzu so yake ta yarda cewar daya samu biyan buqata ze gujeta kenan shi Mahaifin nata sakaran inane da ze yarda haka ta faru? Ko kuwa ita yake so ya mayar sakarya ta yarda da qaryarsa sedai kawai taji ana matsa zata shigo da Amarya ko? To zatayi maganinsu daga shi har Uban Zahran, Kwangila ce ta hada kuna zata raba kowa ya kama gabansa yaje can ya nemawa yarsa data qi auruwa yake neman kai da ita wani Mijin badai Khalil ba.

Janye jikinta tayi daga ruqon da yayi mata Khalil ya kallonta yace
"Are you now happy? Kin yarda ba cin Amanarki nayi ba ko?"
Murmushin da ita kadai tasan ma'anarsa tayi kafin tace
"Hajiya tace zatayi mun Danwake yu wa nakeji ko zaka duba idan an gama"
"Sure, kinsan kuwa ban shiga gurinta ba gaba daya hankalina yana kan nazo na wanke kaina a gurin Babbar Hajiyata, bari nayi maza na karbo miki kici nima kizo ki bani nawa danwaken kar ma kice mun Dr ya hana" ya qarasa yana miqewa tareda kashe mata ido daya ya fice daga dakin. Ta balcony dake saman taga fitarsa daga part dinsu kafin ta koma dakinsa tana tafiya a hankali dan idan tayi motsi da yawa har sannan Marar ta na mata ciwo.

Wayarsa daya manta akan Mirror ta dauka. Bata bata lokaci ba gurin nemo number Dr Sabitu ba tareda tunanin komai ba ta danna masa kira ta wayar Khalil din.
"Aa, My son badai har ka iso ba? Kasan itama mutuniyar ina gaya mata zaka zo gata can se fushi take ashe baka sanar mata yau zaka dawo ba" Dr Sabitu ya fada cikin maganarsa me sauri, Umaimah taja iska ta jiqa hunhunta kafintace
Chapter 140 · 0% Book details