Sashe 158
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Raba dare yayi yana kallon Umaimah dake baccinta hankali kwance saboda duniyar tana gara mata yanda take so, ta samu kan Mijinta bata da wata damuwa. Tunanin irin yanda zasu kwasota kawai yakeyi idan har maganar nan ta tabbata amma a wannan karon baya jin zeji bari, ko shi ko Umaimah.
HUMAIRAH
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 59
HUMAIRAH
Bayan da Khalil ya sauketa tana shiga gida ta ajiye ledar daya bata da saqon Mama ta faa bandaki saboda fitsarin daya matseta tunda suka fita take jinsa. Habibu ta tarar ya bude ledar data ajiye ya zaro kwalin Waya Iphone bata dai san ko wacce ce ba dan ita ba sanin waya tayi ba.
"Ke waya siya miki IPhone?" Ya fada ganin ta fito daga bandakin, Mama dake juya kwalin ta kalle ta tace
"Humaira wadannan fa daga ina haka?"
"Yaya Khalil ne ya bani, mun taho a hanya ya tambayeni inada waya nace masa Aa ta hannuna takice shine ya tsaya a wani shago ya siyo wannan ga kudi nan kuma yace na kawo miki ya wuce yana sauri" ta bawa Maman Amsa cikin nutsuwa, kafin ma Mama tayi magana Habibu ya amshe yana cewa
"Kan bala'i kuma shine ze siya miki IPhone? Lallai Yah Khalil qaiqayi kudi suke masa besan ko Keypad baki gama sanin yanda ake dannata ba ballantana wata IPhone ai kawai ni ya siya wallahi, alfarma daya zan miki na jefeki da Infinix dita ki qarasata" ya fada yana zaro wayarsa data sha jiki daga Aljihu. Bata fuska tayi kamar zatayi kuka Mama tace
"Sha kuruminki, kai kuma me son abin duniya baka isa ba. In kai na roqa ka rakata kaqi gara da baka je ba gashi nan rabo ne ya kirata. Maza karbi wayarki an gode masa Allah ya saka da Alkhairi daman yaushe muke zancen da Yayanku yace ze turo miki da wayar to ga dan uwansa ya hutashshe sa ya siya miki"
"Mama kinsan kudin wayar nan kuwa, Humairan za'a barwa ita lallai ma" Habibu ya sake fada Mama ta fizge kwalin wayar daga hannunsa tana cewa
"Ko Miliyan dubu ake saida ita haka zaka barta da abarta shi wanda ya siya beyi kyashi ba se kai dan hana ruwa gudu ko to ka canza hali. Maza ki kaita daki ki boye, Sumayya tace zata zo anjima naga hoton kamar irin tata da tazo seta saita miki ita kema ki samu ta daddannawa kinji Uwata Allah dai ya sakawa Khalil da Alkhairi" ta tattara mata wayar da ledar ta bata ta shige cikin daki Abinta. Tsalle ta ringa bugawa na murna tana kallon kwalin wayar.
Wai yau ita ma tayi wayar kanta kuma IPhone babba duk cikin yan qaryar Ajinsu masu zuwa da waya babu me irinta dole ranar Graduation kuwa ta wanke su sedai su ganta da waya tana daukar hotuna itama. Saboda zumudi bata iya jira Sumayyan tazo ba ta bude wayar ta jona chaji, Kati ta gani na dubu daya a ciki MTN, ta duba bataga Layi a ciki ba dan haka tana idar da Sallar Magriba tacewa Maman zata shagon Lawi ta siyo layi yayi mata Register Mama ta bata Dari biyar ta tafi, bata jima ba kuwa ta siyo ta dawo dan babu nisa daga gidansu tana dawowa ta tarar da Sumayyan tazo har Mama ta dakko mata wayar ta kunna Hotspot tana saita mata ita. Dakyar ta iya haqura ta bar Layin ya kai awannin da aka ce mata kafinta dora ta shiga WhatsApp da an rigada an mata downloading, number Noor data haddace tsaf ta loda tayi masa magana. Be yarda ita bace seda tayi masa voice yaji muryarta babu bata lokaci ya tura mata da hotunansa da tacs tana so, ya tafi Training din aikin Soja wanda shine karo na uku da yake zuwa biyun baya duk be samu ba amma haka ya sake nema ya tafi a karo na ukun dan ya dage shi idan ba Soja ba baya tunanin akwai aikin da ze iya yi.
A wayar Mama ta kwafi number Khalil layin na hawa kuwa ta rangada masa text na godiya kafin taci gaba da sabgoginta ta loda numbers din qawayenta da daman a wayar Mama take saving dinsu kafin ta shiga dora status din Haskenta kamar yanda take fata a kullum itama tayi waya ta ringa saka hotonsa a status kamar yanda yake saka nata.
KHALIL
Tun bayan maganar da sukayi da Anwar yake ta qoqarin ganin ya yakice Humaira da tunaninta daga zuciyarsa amma abun ya gagara. Tamkar yana jiran ayi masa fashin baqi akan abinda yake ji din akanta, maimakon ya cireta daga ransa kamar yanda yake niyya se abun ya faskara kullum qara samun guri takeyi tana narkewa a zuciyarsa idan kuwa ya ga tayi status na soyayya ji yakeyi kamar yayi bindiga amma a hakan kullum qaryata zuciyarsa yakeyi akan baya sonta.
A gari yaji za'a fara rubuta Jamb kwana biyu masu zuwa dan haka ranar ya shirya da Yamma tareda Mu'ayyad haka kawai suka tafi gidan Mama. Kewar Humairan yakeyi amma ya rasa ta inda ze jr gidan dan baya son Maman ta zargi wani abu yanzu daya samu zancen Jamb din seya fake dashi, kwalliya yasha da wata Danyar Shadda Cream color ya kafa hula. Yana cikin fesa turare Umaimah ta shiga dakin. Kallo daya ta masa ta dauke kai ba tace masa qala ba tabi lafiyar gado ta kwanta dan kwana biyun wani Mood swings take ji dashi kowa na gidan ma haushinsa take ji ko bangaren Hajiyan se a kwana a wuni bata leqa ba.
Turare ya dauka yana qara fesawa a jikinsa dukda ya saka amma ji yayi be ishe shi ba. Ya gama fesa turare ya sake daukar comb yana taje Gemu daga nan ya koma gyaran hula. Umaimah dake kwance abin ya isheta, yanda yake ta wani faman qalqale qalqale kamar sabon Ango yasa ta miqe zaune murya a cukule tace
"Wai ina zakaje kake ta wani faman kwalliya kana gyara fuska?"
Waigawa yayi ya kalleta fuskarsa babu yabo babu fallasa yace
"Inda kika aikeni" dan shima yanzu gasa mata magana yake a tsaye yanda take masa. Aiko ta harareshi ta koma tayi kwanciyarta yana jinta cikin qunquni tana cewa
"Duk abinda mutum yakeyi dan kansa ni dai idan anci Amanata ba yafewa zanyi ba".
Murmushi kawai yayi be tankata ba ya fice daga dakin, a bangaren Hajiya ya dauki Mu'ayyad bayan ya gaya mata zasu fita tayi masa a dawo lafiya kafin suka kama hanya.
Seda ya tsaya a hanya yauma yayi wa Maman cefanen kayan miya masu kyau daya gani ya biya gurin da ake siyar da Kaji ya siya Frozen kafin suka kama hanya. Seda sukaje qofar gidan zuciyarsa ta raya masa cewar ya kamata ace ya zowa da Humaira da tsaraba, wa yaga azarbabi.
A cikin Get din gidan yayi mugun gani, Humaira na tsaye ta saka dogon Hijabi kamar kullum har qasa tajawoshi ta refe fuska ta kamar mejin kunya. Ya maida kallonsa kan Dogo siririn Saurayin dake tsaye kusa da ita yana mata magana dukda be jiyo abinda yake fada ba da alama shi ya bata kunyar.
Wani abu me daci yaji ya taso masa, kamar ya juya amma Mu'ayyad daya dakko ledar Tumatir ya rigada ya shige ciki dan shi ya tsaya hado kan ragowar Ledojin, haka ya ratsa su ya wuce. Yana jin tana masa sannu da zuwa harda shima saurayin nata amma yayi kamar beji su ba ya shige ciki.
Mama nata yiwa Mu'ayyad sannu da zuwa ya shiga, ta juyo kansa tana cewa
"Gaskiya ka kyauta, yau zuwan naka yafi na kullum tunda ka taho mun da Megida harda Cefanensa"
Seda yayi da gaske kafin ya iya danne abinda ke taso masa ya shiga gaisheta, ta amsa tana tambayarsa gida tareda godiyar Wayar daya bawa Humairan.
Shiru yayi kawai ya zubawa qofa ido yana jiran yaga sanda zata shigo Mama data tafi kawo musu ruwa ta dawo da babban Try data doro ruwan da Lemo. Ta ajiye wani kwano gaban Mu'ayyad tana cewa
"Wannan na megida ne".
Alkaki ne a ciki nan take kuwa ya hau ci ta shiga tsokanarsa da cewa Shazumamu shidai Khalil ya gaza shan koda muqurwar ruwa daya dan ya tabbatar bazasu iya wucewa ta maqoshinsa ba. Hira Mama take masa ganin ya maida hankali yana ta danna waya yasa tayi shiru ta mayarda hirar tata kan Mu'ayyad.
Seda suka ahafe kusan minti Ashirin a zaune kafin ta shigo da sallama cikin siririyar muryarta.
"Oh ni Hauwa'u, wallahi na manta shaf da batun bakya gidan nan Humaira se kace wadda ta tafi rubuta jarabawar gaba daya kusan awa nawa keda kika ce ba zaki dade ba" Mama ta fada tana riqe baki dan da gaske ta manta da Humairan ta fita.
Baki ta tura cikin shagwaba tace
"Kai Mama ko fa awqa biyu banyi da fita ba kuma ni na dade da dawowa muna tsaye da Noor a Get, sanda su Yah Khalil ma suka zo muna nan fa" kallonta yayi, yanda ta ambaci Khalil din ka rantse ita ta saka masa sunan yanda ta fada yayi mugun masa dadi amma haushin maimaita cewar tana tsaye da koma waye yazo yasa ya galla mata wata harara.
HUMAIRAH
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 59
HUMAIRAH
Bayan da Khalil ya sauketa tana shiga gida ta ajiye ledar daya bata da saqon Mama ta faa bandaki saboda fitsarin daya matseta tunda suka fita take jinsa. Habibu ta tarar ya bude ledar data ajiye ya zaro kwalin Waya Iphone bata dai san ko wacce ce ba dan ita ba sanin waya tayi ba.
"Ke waya siya miki IPhone?" Ya fada ganin ta fito daga bandakin, Mama dake juya kwalin ta kalle ta tace
"Humaira wadannan fa daga ina haka?"
"Yaya Khalil ne ya bani, mun taho a hanya ya tambayeni inada waya nace masa Aa ta hannuna takice shine ya tsaya a wani shago ya siyo wannan ga kudi nan kuma yace na kawo miki ya wuce yana sauri" ta bawa Maman Amsa cikin nutsuwa, kafin ma Mama tayi magana Habibu ya amshe yana cewa
"Kan bala'i kuma shine ze siya miki IPhone? Lallai Yah Khalil qaiqayi kudi suke masa besan ko Keypad baki gama sanin yanda ake dannata ba ballantana wata IPhone ai kawai ni ya siya wallahi, alfarma daya zan miki na jefeki da Infinix dita ki qarasata" ya fada yana zaro wayarsa data sha jiki daga Aljihu. Bata fuska tayi kamar zatayi kuka Mama tace
"Sha kuruminki, kai kuma me son abin duniya baka isa ba. In kai na roqa ka rakata kaqi gara da baka je ba gashi nan rabo ne ya kirata. Maza karbi wayarki an gode masa Allah ya saka da Alkhairi daman yaushe muke zancen da Yayanku yace ze turo miki da wayar to ga dan uwansa ya hutashshe sa ya siya miki"
"Mama kinsan kudin wayar nan kuwa, Humairan za'a barwa ita lallai ma" Habibu ya sake fada Mama ta fizge kwalin wayar daga hannunsa tana cewa
"Ko Miliyan dubu ake saida ita haka zaka barta da abarta shi wanda ya siya beyi kyashi ba se kai dan hana ruwa gudu ko to ka canza hali. Maza ki kaita daki ki boye, Sumayya tace zata zo anjima naga hoton kamar irin tata da tazo seta saita miki ita kema ki samu ta daddannawa kinji Uwata Allah dai ya sakawa Khalil da Alkhairi" ta tattara mata wayar da ledar ta bata ta shige cikin daki Abinta. Tsalle ta ringa bugawa na murna tana kallon kwalin wayar.
Wai yau ita ma tayi wayar kanta kuma IPhone babba duk cikin yan qaryar Ajinsu masu zuwa da waya babu me irinta dole ranar Graduation kuwa ta wanke su sedai su ganta da waya tana daukar hotuna itama. Saboda zumudi bata iya jira Sumayyan tazo ba ta bude wayar ta jona chaji, Kati ta gani na dubu daya a ciki MTN, ta duba bataga Layi a ciki ba dan haka tana idar da Sallar Magriba tacewa Maman zata shagon Lawi ta siyo layi yayi mata Register Mama ta bata Dari biyar ta tafi, bata jima ba kuwa ta siyo ta dawo dan babu nisa daga gidansu tana dawowa ta tarar da Sumayyan tazo har Mama ta dakko mata wayar ta kunna Hotspot tana saita mata ita. Dakyar ta iya haqura ta bar Layin ya kai awannin da aka ce mata kafinta dora ta shiga WhatsApp da an rigada an mata downloading, number Noor data haddace tsaf ta loda tayi masa magana. Be yarda ita bace seda tayi masa voice yaji muryarta babu bata lokaci ya tura mata da hotunansa da tacs tana so, ya tafi Training din aikin Soja wanda shine karo na uku da yake zuwa biyun baya duk be samu ba amma haka ya sake nema ya tafi a karo na ukun dan ya dage shi idan ba Soja ba baya tunanin akwai aikin da ze iya yi.
A wayar Mama ta kwafi number Khalil layin na hawa kuwa ta rangada masa text na godiya kafin taci gaba da sabgoginta ta loda numbers din qawayenta da daman a wayar Mama take saving dinsu kafin ta shiga dora status din Haskenta kamar yanda take fata a kullum itama tayi waya ta ringa saka hotonsa a status kamar yanda yake saka nata.
KHALIL
Tun bayan maganar da sukayi da Anwar yake ta qoqarin ganin ya yakice Humaira da tunaninta daga zuciyarsa amma abun ya gagara. Tamkar yana jiran ayi masa fashin baqi akan abinda yake ji din akanta, maimakon ya cireta daga ransa kamar yanda yake niyya se abun ya faskara kullum qara samun guri takeyi tana narkewa a zuciyarsa idan kuwa ya ga tayi status na soyayya ji yakeyi kamar yayi bindiga amma a hakan kullum qaryata zuciyarsa yakeyi akan baya sonta.
A gari yaji za'a fara rubuta Jamb kwana biyu masu zuwa dan haka ranar ya shirya da Yamma tareda Mu'ayyad haka kawai suka tafi gidan Mama. Kewar Humairan yakeyi amma ya rasa ta inda ze jr gidan dan baya son Maman ta zargi wani abu yanzu daya samu zancen Jamb din seya fake dashi, kwalliya yasha da wata Danyar Shadda Cream color ya kafa hula. Yana cikin fesa turare Umaimah ta shiga dakin. Kallo daya ta masa ta dauke kai ba tace masa qala ba tabi lafiyar gado ta kwanta dan kwana biyun wani Mood swings take ji dashi kowa na gidan ma haushinsa take ji ko bangaren Hajiyan se a kwana a wuni bata leqa ba.
Turare ya dauka yana qara fesawa a jikinsa dukda ya saka amma ji yayi be ishe shi ba. Ya gama fesa turare ya sake daukar comb yana taje Gemu daga nan ya koma gyaran hula. Umaimah dake kwance abin ya isheta, yanda yake ta wani faman qalqale qalqale kamar sabon Ango yasa ta miqe zaune murya a cukule tace
"Wai ina zakaje kake ta wani faman kwalliya kana gyara fuska?"
Waigawa yayi ya kalleta fuskarsa babu yabo babu fallasa yace
"Inda kika aikeni" dan shima yanzu gasa mata magana yake a tsaye yanda take masa. Aiko ta harareshi ta koma tayi kwanciyarta yana jinta cikin qunquni tana cewa
"Duk abinda mutum yakeyi dan kansa ni dai idan anci Amanata ba yafewa zanyi ba".
Murmushi kawai yayi be tankata ba ya fice daga dakin, a bangaren Hajiya ya dauki Mu'ayyad bayan ya gaya mata zasu fita tayi masa a dawo lafiya kafin suka kama hanya.
Seda ya tsaya a hanya yauma yayi wa Maman cefanen kayan miya masu kyau daya gani ya biya gurin da ake siyar da Kaji ya siya Frozen kafin suka kama hanya. Seda sukaje qofar gidan zuciyarsa ta raya masa cewar ya kamata ace ya zowa da Humaira da tsaraba, wa yaga azarbabi.
A cikin Get din gidan yayi mugun gani, Humaira na tsaye ta saka dogon Hijabi kamar kullum har qasa tajawoshi ta refe fuska ta kamar mejin kunya. Ya maida kallonsa kan Dogo siririn Saurayin dake tsaye kusa da ita yana mata magana dukda be jiyo abinda yake fada ba da alama shi ya bata kunyar.
Wani abu me daci yaji ya taso masa, kamar ya juya amma Mu'ayyad daya dakko ledar Tumatir ya rigada ya shige ciki dan shi ya tsaya hado kan ragowar Ledojin, haka ya ratsa su ya wuce. Yana jin tana masa sannu da zuwa harda shima saurayin nata amma yayi kamar beji su ba ya shige ciki.
Mama nata yiwa Mu'ayyad sannu da zuwa ya shiga, ta juyo kansa tana cewa
"Gaskiya ka kyauta, yau zuwan naka yafi na kullum tunda ka taho mun da Megida harda Cefanensa"
Seda yayi da gaske kafin ya iya danne abinda ke taso masa ya shiga gaisheta, ta amsa tana tambayarsa gida tareda godiyar Wayar daya bawa Humairan.
Shiru yayi kawai ya zubawa qofa ido yana jiran yaga sanda zata shigo Mama data tafi kawo musu ruwa ta dawo da babban Try data doro ruwan da Lemo. Ta ajiye wani kwano gaban Mu'ayyad tana cewa
"Wannan na megida ne".
Alkaki ne a ciki nan take kuwa ya hau ci ta shiga tsokanarsa da cewa Shazumamu shidai Khalil ya gaza shan koda muqurwar ruwa daya dan ya tabbatar bazasu iya wucewa ta maqoshinsa ba. Hira Mama take masa ganin ya maida hankali yana ta danna waya yasa tayi shiru ta mayarda hirar tata kan Mu'ayyad.
Seda suka ahafe kusan minti Ashirin a zaune kafin ta shigo da sallama cikin siririyar muryarta.
"Oh ni Hauwa'u, wallahi na manta shaf da batun bakya gidan nan Humaira se kace wadda ta tafi rubuta jarabawar gaba daya kusan awa nawa keda kika ce ba zaki dade ba" Mama ta fada tana riqe baki dan da gaske ta manta da Humairan ta fita.
Baki ta tura cikin shagwaba tace
"Kai Mama ko fa awqa biyu banyi da fita ba kuma ni na dade da dawowa muna tsaye da Noor a Get, sanda su Yah Khalil ma suka zo muna nan fa" kallonta yayi, yanda ta ambaci Khalil din ka rantse ita ta saka masa sunan yanda ta fada yayi mugun masa dadi amma haushin maimaita cewar tana tsaye da koma waye yazo yasa ya galla mata wata harara.