Sashe 240
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ai kasan shi da kafiya seda na hanshi baccin a daki ashe daya fito kwanciya yayi anan na tashe shi yanzun ma yaqi farkawa se nauyin bacci kamar wani babba" Humaira ta fada tana sake tada yaron amma ko gezau data dago shi ze janye ya koma da alama baccin ne a kansa sosai.
"Ai dashi da Bibi bansan inda sula samo kafiyar nan ba har gara itama, dazu fa a makaranta da Manniru yaje daukarsu" (nan ya bata labarin yanda sukayi) se ta kama baki tana cewa
"Gaskiya kafa dena abinda kakeyi ba yanzu ake ji ba gaba ce abin dubawa wai tayaya za'ayi ace komai Bibi take so shi za'ayi a gidan nan?"
"Baki san sunan Hajiya ne da ita ba kuma gata matata ai dole nayi abinda tace" ya fada da sigar tsokana seta hade fuska tana cewa
"Ba wasa nakeyi ba Yaya Khalil maganar Allah itace tun yana danye ake tankwarashi. Yanzu abinda kayi mun shekaran jiya shiru kawai nayi amma naji haushi sosai wlh ya za'ayi tayi laifi ina mata fada a gabanta ka nuna abinda tayi be kai nayi fada ba har kace mata ta tafi ta kwanta kuma ko a jikinka? Shekara takwas ai ba wata takwas bace da zata ringa yiwa mutane barna kuma baza'a tsawatar mata ba gaskiya karka sake yi mun haka ko a gaba idan yaro yayi ba daidai ba in ba zaka taya muyi musu fada ba karka sa mun baki kuma yanzu banda wulaqanci a makaranta zata je tana ihu da birgima akan abu kuma kayi mata gobe ma kace ta maimaita kenan".
Kallonta ya ringayi yanda take kumfar baki a kan abinda be kai ya kawo ha a ganinsa kenan amma duk tabi ta haqiqance seya kama hannunta yana cewa
"Yanzu meye abun fushi a maganar shekaran jiya da har kika riqe a ranki Bottle water ne fa ta dauka tayi Alwala shine abintada jiniyar wuya kika ringa fada kamar wadda tayi alwalar da Mangyada ko Madara sannan maganar yau ni na amsa mata jiya kan za'a kaisu kinga ai bazan saba mata alqawari ba"
"Ai shikenan" ta bashi amsa dan zuciyarta ta qulu da maganar tasa tunda bega rashin dacewar abinda yakeyi ba seya ci gaba ita dai ba zata fasa tsawatarwa duk wanda yayi ba daidai ba a cikinsu sedai yaji haushi tunda idan sun lalace qarshe ita za'a zaga ace ta musu mugunta tunda ba ita ta haifesu ba. Ganin da yayi ta hada rai yasa ya ringa rara gefe amma tayi masa shiru bata cewa komai suna nan zaune har aka kira Magriba ya tashi yayo alwala ita ma ta shiga daki da Aryaan daya farka daga bacci, yanda ya shigo a firgice bayan an idar da sallah ya bata tsoro. Ta kalle shi tace
"Lafiya?"
"Ina fa lafiya, har yanzu yaran nan basu dawo daga Islamiyyar ba, kuma na tambayi Sammani ina Manniru yake dan motarsu bata nan yace tunda ya tafi dakko su daga Boko be dawo ba which mean basu je islamiyyar ba kenan ma ashe gashi ina ta kiran wayarsa bata shiga" Khalil dinya fada a kidime take itama hankalinta ya tashi ta miqe tsaye tana cewa
"Number sa bata shiga kuma Sammanin bashi da wani layin nasa da za'a kira?"
"Number sa daya ce babu wata" ya bata amsa yana zagaye dakin, tunanin inda yaransa suka shiga yakeyi kar fa wani abu ya same su.
"Toh ba kace ya kaisu gurin Mamansu ba ka kira can mana kaji" Humairan ta fada cikin damuwa se yayi saurin zaro wayarsa dan ya manta da can din ma. Number Mama ya kira a kashe, baya tsammanin Abba na gida dan haka kai tsaye zuciyarsa ta bashi ya kira Umaiman. Da ka ya zuba numberta dake haddace, sunan da yayi saving ya fito 'WIFE' da Emojin Heart guda biyu daga shi har Humairan dake kallon wayar wani abu ya daki zukatansu sedai kowanne da kalar nasa, tabbacin da aka bashi na wayar a kashe take itama yasa shi jan tsaki ya juya yana cewa
"Bari naje gidan na gani" kafinta ce masa wani abu ya fice daga dakin da saurin gaske har yana hada hanya seta bishi da ido wani abu me daci yana taso mata, number wayarta da Sweetheart yayi saving amma shine ita da basa tare hau yau be canza mata suna a wayarsa ba.
Khalil kuwa cikin qanqanin lokaci ya isa gidansu Umaimah saboda gudun da ya ringa shararawa a hanya idan wani abu ya samu yaransa be san yanda zeyi ba. Layin babu kowa saboda an shiga sallar isha, ya kasa haqurin jira se kawai ta kutsa kansa gidan bakinsa dauke da Sallama tareda taraddadin samunsu ko akasin haka dan rashin ganin Motarsu a waje ya qara daga masa hankali seda yayi sallama uku kafin ya shiga ainihin tsakar gidan daidai nan Umaimah ta fito daga daki jin kamar ana sallama sukayi ido hudu dashi yana tsaye daga bakin qofa yana jiran ganin giftawar wani.
Cikin qasa da seconds biyar ya qare mata kallo kafin ya dauke kansa sama saboda yanda zuciyarsa ta shiga wani bugu kamar zata fito, Umaimah kuwa ido ta zuba masa kamar farin shigar Maita, ta kasa gasgata Khalil ne da gaske ko kuma Mafarkan data sabayi ne amma kuma qamshin turarensa dake busata yasa ta ke son gasgata shi din ne da gaske ba mafarki ba
"Naji kamar ana sallama ko ba a nan bane?" Mama data leqo ta fada ganin Khalil a tsaye yasa ta fadada murmushinta tana cewa
"Au kaine? Shigo ciki mana ka tsaya a qofa kamar wani baqo".
Cikin takunsa me cike da nutsuwa ya giftata tamkar bega mutum a gurin ba qamshinsa ya cika mata hunhu ji ta ringayi kamar tana shaqar sabon numfashi seta rufe idonta ta bude ta sake rakashi da kallo harya shige falon Mama jikintavna wani irin sanyi kamar wadda ake daskararwa. Yanda Khalil din ya debeta ya watsar bema nuna alamar yaga mutum a tsakar gidan ba lallai abin Azimun ne. A sanyaye taja qafafunta ta matsa jikin bango zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, takai kusan minti biyar a tsaye kafin ta jiyo qamshin turaren sa yana sake tun karota, tayi saurin bude idanunta jin takunsa kusa da ita muryarta na rawa ta kira sunansa ya tsaya cak a inda yake ba tareda ya juyo ba tamkar kuma wanda aka tsikara yaci gaba da tafi da sauri ba kamar yanda ya fito daga dakin Maman yana tafiya a hankali ba.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 82
Seda ya dauki kusan minti goma zaune a cikin motar kafin ya kunnata wayarsa dake ajiye kan kujera ta yi haske ya janyota ganin Sweetheart ke kiransa kafin ya daga ta katse se sannan ya lura da tarin missed calls din data yi masa da alama tun fitowarsa daga gidan take kira. Cikin mutuwar jikin da ganinta ya haifar masa ya sake kashe motar kafin yabi bayan kiran Humairan
"Habibi ina ka shiga tunda ka fita nake kira gasu sun dawo qila ma kun hadu a hanya dan motarka na fita tasu ta shigo" Humairanta fada cikin damuwa seya sauke ajiyar zuciya murya can qasa yace mata
"Sorry wayar a silent take bangani ba se yanzu gani nan zuwa gidan nima"
"Amma lafiya naji muryarka haka? Nagaya maka fa gasu sun dawo babu abinda ya samesu tun ranan suna gurin Mamansu shi kuma cajinsa ne wai ya qare shiyasa kaji wayar a kashe" ta sake fada saboda jin muryarsa da tayi wani iri seda yayi qoqarin saita kansa kafin yace
"Babu komai fa nazo gidan nima suka ce sun tafi gani nan ina hanyar dawowa" daga haka sukayi sallama. Yana tuqi amma gaba daya hankalinsa baya kan Titin, wani irin mix emotions ke damun sa. Ganin Umaiman ya haddasa masa abubuwa da yawa ta tuna masa da wancan daren daya zama baqin dare a rayuwarsu gaba daya abubuwan da suka faru suka ringa dawo masa kamar a sannan suke faruwa a bangare daya kuma daga can qasan zuciyarsa yana jin wani abu na motsa masa akanta. Allah shine shaidarsa yana son Umaimah irin son da be taba yiwa wata Halitta shi ba. Yana jinta har cikin jini da jijiyarsa amma ta barar da damarta tayi masa abinda idan harda gaske shi dan Halal ne kamar yanda take fada koda ace ita kadai ta rage mace a doron duniya ze zabi ya qare rayuwarsa babu aure domin ta keta alfarmar wadanda baya hada komai dasu. Tabbas idan da ace iyakar abinda tayi masa ne tabbas ze iya yafe mata ya rungumeta suci gaba da zama Albarkacin son da yake mata da zuri'ar dake tsakaninsu amma a yanzu baya zaton akwai wani uzuri da ze iya yi mata daze kankare tarin laifukanta a zuciyarta data sauran Ahalainsa.
Maganar da Mama tayi masa bayan shigarsa akan Bibi ta tsaya masa a rai, ya gagara ganin abinda yakeyi mata da kowa yake cewa yana lalata ta shin laifine dan ya samarwa da yarsa abinda take so Alhali yana da halin hakan? Shi haka kawai duk cikin yaran tafi shiga zuciyarsa hakan kuma ya samo Asali da suna da kuma kammanin Hajiyarsa data dauka kuma shi baya nuna banbanci tsakaninta da yan uwanta kamar yanda ake cewa yanayi kawai ita tafi sakewa dashi kuma tafi tambayarsa yayi mata abu shiyasa amma suma duk wanda ya nemi abu a gurinsa ai yanayi masa ba wai ita kadai ba yana wadannan tunane tunanen ya isa gida. Yaran har sunyi wanka suna cin abinci ya shiga falon sukayi masa sannu da zuqa gaba daya ya amsa ba tareda ya kalle su ba ya haye sama.
"Ai dashi da Bibi bansan inda sula samo kafiyar nan ba har gara itama, dazu fa a makaranta da Manniru yaje daukarsu" (nan ya bata labarin yanda sukayi) se ta kama baki tana cewa
"Gaskiya kafa dena abinda kakeyi ba yanzu ake ji ba gaba ce abin dubawa wai tayaya za'ayi ace komai Bibi take so shi za'ayi a gidan nan?"
"Baki san sunan Hajiya ne da ita ba kuma gata matata ai dole nayi abinda tace" ya fada da sigar tsokana seta hade fuska tana cewa
"Ba wasa nakeyi ba Yaya Khalil maganar Allah itace tun yana danye ake tankwarashi. Yanzu abinda kayi mun shekaran jiya shiru kawai nayi amma naji haushi sosai wlh ya za'ayi tayi laifi ina mata fada a gabanta ka nuna abinda tayi be kai nayi fada ba har kace mata ta tafi ta kwanta kuma ko a jikinka? Shekara takwas ai ba wata takwas bace da zata ringa yiwa mutane barna kuma baza'a tsawatar mata ba gaskiya karka sake yi mun haka ko a gaba idan yaro yayi ba daidai ba in ba zaka taya muyi musu fada ba karka sa mun baki kuma yanzu banda wulaqanci a makaranta zata je tana ihu da birgima akan abu kuma kayi mata gobe ma kace ta maimaita kenan".
Kallonta ya ringayi yanda take kumfar baki a kan abinda be kai ya kawo ha a ganinsa kenan amma duk tabi ta haqiqance seya kama hannunta yana cewa
"Yanzu meye abun fushi a maganar shekaran jiya da har kika riqe a ranki Bottle water ne fa ta dauka tayi Alwala shine abintada jiniyar wuya kika ringa fada kamar wadda tayi alwalar da Mangyada ko Madara sannan maganar yau ni na amsa mata jiya kan za'a kaisu kinga ai bazan saba mata alqawari ba"
"Ai shikenan" ta bashi amsa dan zuciyarta ta qulu da maganar tasa tunda bega rashin dacewar abinda yakeyi ba seya ci gaba ita dai ba zata fasa tsawatarwa duk wanda yayi ba daidai ba a cikinsu sedai yaji haushi tunda idan sun lalace qarshe ita za'a zaga ace ta musu mugunta tunda ba ita ta haifesu ba. Ganin da yayi ta hada rai yasa ya ringa rara gefe amma tayi masa shiru bata cewa komai suna nan zaune har aka kira Magriba ya tashi yayo alwala ita ma ta shiga daki da Aryaan daya farka daga bacci, yanda ya shigo a firgice bayan an idar da sallah ya bata tsoro. Ta kalle shi tace
"Lafiya?"
"Ina fa lafiya, har yanzu yaran nan basu dawo daga Islamiyyar ba, kuma na tambayi Sammani ina Manniru yake dan motarsu bata nan yace tunda ya tafi dakko su daga Boko be dawo ba which mean basu je islamiyyar ba kenan ma ashe gashi ina ta kiran wayarsa bata shiga" Khalil dinya fada a kidime take itama hankalinta ya tashi ta miqe tsaye tana cewa
"Number sa bata shiga kuma Sammanin bashi da wani layin nasa da za'a kira?"
"Number sa daya ce babu wata" ya bata amsa yana zagaye dakin, tunanin inda yaransa suka shiga yakeyi kar fa wani abu ya same su.
"Toh ba kace ya kaisu gurin Mamansu ba ka kira can mana kaji" Humairan ta fada cikin damuwa se yayi saurin zaro wayarsa dan ya manta da can din ma. Number Mama ya kira a kashe, baya tsammanin Abba na gida dan haka kai tsaye zuciyarsa ta bashi ya kira Umaiman. Da ka ya zuba numberta dake haddace, sunan da yayi saving ya fito 'WIFE' da Emojin Heart guda biyu daga shi har Humairan dake kallon wayar wani abu ya daki zukatansu sedai kowanne da kalar nasa, tabbacin da aka bashi na wayar a kashe take itama yasa shi jan tsaki ya juya yana cewa
"Bari naje gidan na gani" kafinta ce masa wani abu ya fice daga dakin da saurin gaske har yana hada hanya seta bishi da ido wani abu me daci yana taso mata, number wayarta da Sweetheart yayi saving amma shine ita da basa tare hau yau be canza mata suna a wayarsa ba.
Khalil kuwa cikin qanqanin lokaci ya isa gidansu Umaimah saboda gudun da ya ringa shararawa a hanya idan wani abu ya samu yaransa be san yanda zeyi ba. Layin babu kowa saboda an shiga sallar isha, ya kasa haqurin jira se kawai ta kutsa kansa gidan bakinsa dauke da Sallama tareda taraddadin samunsu ko akasin haka dan rashin ganin Motarsu a waje ya qara daga masa hankali seda yayi sallama uku kafin ya shiga ainihin tsakar gidan daidai nan Umaimah ta fito daga daki jin kamar ana sallama sukayi ido hudu dashi yana tsaye daga bakin qofa yana jiran ganin giftawar wani.
Cikin qasa da seconds biyar ya qare mata kallo kafin ya dauke kansa sama saboda yanda zuciyarsa ta shiga wani bugu kamar zata fito, Umaimah kuwa ido ta zuba masa kamar farin shigar Maita, ta kasa gasgata Khalil ne da gaske ko kuma Mafarkan data sabayi ne amma kuma qamshin turarensa dake busata yasa ta ke son gasgata shi din ne da gaske ba mafarki ba
"Naji kamar ana sallama ko ba a nan bane?" Mama data leqo ta fada ganin Khalil a tsaye yasa ta fadada murmushinta tana cewa
"Au kaine? Shigo ciki mana ka tsaya a qofa kamar wani baqo".
Cikin takunsa me cike da nutsuwa ya giftata tamkar bega mutum a gurin ba qamshinsa ya cika mata hunhu ji ta ringayi kamar tana shaqar sabon numfashi seta rufe idonta ta bude ta sake rakashi da kallo harya shige falon Mama jikintavna wani irin sanyi kamar wadda ake daskararwa. Yanda Khalil din ya debeta ya watsar bema nuna alamar yaga mutum a tsakar gidan ba lallai abin Azimun ne. A sanyaye taja qafafunta ta matsa jikin bango zuciyarta na bugawa da sauri da sauri, takai kusan minti biyar a tsaye kafin ta jiyo qamshin turaren sa yana sake tun karota, tayi saurin bude idanunta jin takunsa kusa da ita muryarta na rawa ta kira sunansa ya tsaya cak a inda yake ba tareda ya juyo ba tamkar kuma wanda aka tsikara yaci gaba da tafi da sauri ba kamar yanda ya fito daga dakin Maman yana tafiya a hankali ba.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 82
Seda ya dauki kusan minti goma zaune a cikin motar kafin ya kunnata wayarsa dake ajiye kan kujera ta yi haske ya janyota ganin Sweetheart ke kiransa kafin ya daga ta katse se sannan ya lura da tarin missed calls din data yi masa da alama tun fitowarsa daga gidan take kira. Cikin mutuwar jikin da ganinta ya haifar masa ya sake kashe motar kafin yabi bayan kiran Humairan
"Habibi ina ka shiga tunda ka fita nake kira gasu sun dawo qila ma kun hadu a hanya dan motarka na fita tasu ta shigo" Humairanta fada cikin damuwa seya sauke ajiyar zuciya murya can qasa yace mata
"Sorry wayar a silent take bangani ba se yanzu gani nan zuwa gidan nima"
"Amma lafiya naji muryarka haka? Nagaya maka fa gasu sun dawo babu abinda ya samesu tun ranan suna gurin Mamansu shi kuma cajinsa ne wai ya qare shiyasa kaji wayar a kashe" ta sake fada saboda jin muryarsa da tayi wani iri seda yayi qoqarin saita kansa kafin yace
"Babu komai fa nazo gidan nima suka ce sun tafi gani nan ina hanyar dawowa" daga haka sukayi sallama. Yana tuqi amma gaba daya hankalinsa baya kan Titin, wani irin mix emotions ke damun sa. Ganin Umaiman ya haddasa masa abubuwa da yawa ta tuna masa da wancan daren daya zama baqin dare a rayuwarsu gaba daya abubuwan da suka faru suka ringa dawo masa kamar a sannan suke faruwa a bangare daya kuma daga can qasan zuciyarsa yana jin wani abu na motsa masa akanta. Allah shine shaidarsa yana son Umaimah irin son da be taba yiwa wata Halitta shi ba. Yana jinta har cikin jini da jijiyarsa amma ta barar da damarta tayi masa abinda idan harda gaske shi dan Halal ne kamar yanda take fada koda ace ita kadai ta rage mace a doron duniya ze zabi ya qare rayuwarsa babu aure domin ta keta alfarmar wadanda baya hada komai dasu. Tabbas idan da ace iyakar abinda tayi masa ne tabbas ze iya yafe mata ya rungumeta suci gaba da zama Albarkacin son da yake mata da zuri'ar dake tsakaninsu amma a yanzu baya zaton akwai wani uzuri da ze iya yi mata daze kankare tarin laifukanta a zuciyarta data sauran Ahalainsa.
Maganar da Mama tayi masa bayan shigarsa akan Bibi ta tsaya masa a rai, ya gagara ganin abinda yakeyi mata da kowa yake cewa yana lalata ta shin laifine dan ya samarwa da yarsa abinda take so Alhali yana da halin hakan? Shi haka kawai duk cikin yaran tafi shiga zuciyarsa hakan kuma ya samo Asali da suna da kuma kammanin Hajiyarsa data dauka kuma shi baya nuna banbanci tsakaninta da yan uwanta kamar yanda ake cewa yanayi kawai ita tafi sakewa dashi kuma tafi tambayarsa yayi mata abu shiyasa amma suma duk wanda ya nemi abu a gurinsa ai yanayi masa ba wai ita kadai ba yana wadannan tunane tunanen ya isa gida. Yaran har sunyi wanka suna cin abinci ya shiga falon sukayi masa sannu da zuqa gaba daya ya amsa ba tareda ya kalle su ba ya haye sama.