Sashe 249
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh yanzu nace kaje ka dawo da itan sedai kuma in ban isa ba seka gaya mun, meta maka? Duk abinda zata maka dai nasan baze kai na wacce ta tsaya a gabanka ta zageni ba toh tunda muka yafe mata banga laifin da za'a mana ya gagara yafuwa ba dan haka ka tashi kaje ka dawo da matarka banda tsabar rashin tunani Yarinyar data rufa maka Asiri ta zauna dakai a halin lalura yanzu daka samu lafiya shine zaka fara gwada mata halinku na Maza ko kuda baku san abin arziqi ba daman"
"Toh saboda ina da lalura shine zata ringa kula wasu Mazan a waje?" Maganar ta subuto daga bakinsa ba tareda ya shirya ba take kuwa Hajiya tayi tsit saga bambamin da takeyi qirjinta ya shiga dokawa ta kalli Khalil da shima yayi tsilli tsilli saboda subul da bakan da yayi, a sanyaye tace
"Babana me kace? Wane mqza take kulawa a waje?"
"Am ni ba haka nace ba, kawai dai ki bar maganar dan Allah Hajiya ta kwana gobe da safe ta dawo shikenan" ya fada yana qoqarin miqewa seta daka masa tsawa tana cewa
"Bana son rashin arziqi, ka dakko magana irin wannan sannan ka tashi kana neman bagarar da ita kasan me kake cewa kuwa? Maza fa naji kayi zancen tana kulawa a waje, koma ka Zauna Khalil ka gaya mun gaskiya ka samu lafiya da gaske kuwa? kuma wane irin zama kukeyi? tun yaushe hakan take faruwa?"
Zaman yayi gaba daya ya rasa me zece mata ganin ta rikice ya tabbata fassarar datayi wa maganar daban da abinda Yakima nufi dole ya tattaro nutsuwarsa jin tana cewa
"Cikin jikinta kuma fa a ina aka sameshi" se yayi saurin cewa
"Haba Hajiya abin be kai nan ba, bafa irin kula Mazan da kike tunani bane nine ban daka miki maganar a yanda zaki fahimta ba daman wannan yaron saurayinta ne yake aiki a Asibitin Al'amin, tun randa muka fara ganinsa naja mata kashedi akan sa amma bataji ba shine yau.." Tiryan tiryan ya labarta mata komai ya qara da cewa
"Ni daman nasan ba wata rashin lafiya kawai ta shirya zuwa ta ganshi ne, na gaya mata ta zaba koni koshi, idanta zabeshi wlh data haihu zan sawwaqe mata taje suyi aure bazan tauyeta ba dan nasan zaman haquri takeyi dani bawai samun yanda take so takeyi ba" yayi maganar kansa a qasa saboda nauyinta.
Hajiya ta sauke numfashi saboda jin abin beyi girman data zata ba amma dukda haka hankalinta be kwanta ba dan ita fitina tana qarama idan ba'a maganceta ba girma takeyi. A hankali tace
"Bata kyauta ba amma kaima kayi saurin yanke hukunci wannan ai abinda za'azo gida a sasantane ba wai seka turata gidansu ba. Sannan shedan ne kawai yake tunzuraka yana qara rura maka wutar kishi amma babu wani abu, aikinsa yakeyi ita kuma kace likita ta turata yin test kaga baze yuwu ai tace ba ze dauki Jininta ba tunda shine a gurin"
"Amma ai bashi kadai bane a gurin Hajiya, data san tsakaninsu akan me zata bashi jikinta har ya wani riqeta yana shafata yana murmushi? Daman ai ya fada mun se ya zama fitina a rayiwarmu to gara kafin muga fitina taje can ta aureshi su qarata ni na haqura" ya sake fada idonsa nayin Jaa dan abin ya bala'in qona masa rai se Hajiya tayi saurin cewa
"Ashsha ka dena cewa haka Mana Babana shaidan ne kawai ya haska maka haka babu tabbacin ma murmushin yakeyi sannan waccen magana daya fada na tabbata a lokacin cikin fushi ne shima bazamuga fitina ba da yardar Allah amma koma yayane kayi haquri tayi kuskure kuma ba za'a sake ba ka daure dan ni badan halin taba ka daukota ta dawo gida karka ja mana abin fada, kana ji har yar uwarka ta fara jifan tsohuwar matarka da cewar Asiri tayi muku to lallaba ka dawo da matarka kafin kasa can itama a fara jefa mata wani zargin, Mace da tsohon ciki haihuwa kowanne lokaci a turata gida ai abin a tambayi ba'asine, zan gayawa Hauwa na tabbata zatayiwa tufkar hanci ba za'a sake yin hakan ba kaji" Hajiya ta shiga lallabashi dole badan yaso na ya tafi ya daukota, harta kwanta Mama ta tasheta akan Khalil yazo ta zare ido tana shirin yin kuka ita dai data barta ta kwana gobe koma me za'ayi ayi amma ya ta iya haka suka kama hanya har sukaje gida be kulata ba. Sum sum ta shige bangarenta shima yayi nasa, yara duk sunyi bacci dan haka itama ta kwanta washe gari kuwa qarfe tara Mama ta dira a gidan dan Hajiya kasa bacci tayi saboda zullumi seda ta kirata ta gaya mata komai.
Irin labaran da take yawan ji akan Tsohon saurayi da budurwa yasa ta kasa samun nutsuwa, bata zargin Humairan da wani banzan hali amma shaidan abin tsoro ne musamman su da suke da baraka yana iya amfani da wannan damar ya kaisu ga abinda ba za'a so ba ga kuma maganar shi yaron da Khalil yace mata ya taba gaya masa tuna shekarun baya na cewar ya jira ya gani, seya zama fitina a rayuwarsu idan har qullin na nan a ransa har yanzu gara ayiwa tufkar hanci da wuri kafin azo ana kukan da an sani.
Tana shiga kafin takai qasa Mama Hauwa ta dauketa da Marin daya gigitata, Khalil dake bayabta ya tareta dan tafiya tayi zata fadi ta kuwa fashe da kuka dan hannun Mama badai zafi ba kamar na maza haka yake. Ta shiga surfa mata bala'i tana zaginta, duk yanda Hajiya taso ta tausheta taqiyin shiru seda tayi mata tatas tana cewa
"Saboda bakida hankali baki saninda yake miki ciwo ba, ke ko a hanya kika ga Nura ya kamata kibi inda yabi yaron daya sha Alwashin lalata rayuwarki shine kike bibiya wato ki bashi damar aiwatar da shirinsa a sauqaqe kenan to ki jini da kyau idan kika kashe auranki sedai ki san inda zaki nufa badai gidana ba tunda ke baki san abin arziqi ba".
"Haba Hajiya abinfa bekai haka ba, na sanar dake ne kawai saboda ya kamata ace kin sani amma badan ki dau abinda zafi ki ringa maganganu haka ba, naga kinada alaqa da uwar yaron zaki iya mata magana taja masa kunne ya fita a sabgarta shikenan ba se anje ga wannan tone tonen ba" Hajiya ta fada, Khalil dai yana riqe da Humaira dake gunsheqar kuka idonsa ya kada yayi jaa shima kamar yayi kukan daya sani be sanarwa da Hajiya ba, beyi tsammanin zata fadawa Mama maganar ba gashi yanzun abin nema yake ya qara girmama.
"Ki barni da mutuniyar banza Hajiya wannan yarinyar da kike gani kunnen qashi ne da ita ai, banda ma abu irin na yaran zamani ina ke ina kula wani tsohon saurayi da auranki duk ba daga nan fitinu suke bullowa ba wai se suce mutunchi mutunchin yaci uwarsa da ubansa ai tunda soyayya ta gifta Shaidan na iya shiga ya taka rawa son ransa yayi abinda yaga dama dan haka kowa ya zauna a iyakarsa babu wani mutunchi da tsohon masoyi ai da ka sani tun jiyan ka fada mun da bazata dawo ba seta zauna a gidan idan yaso ka saketa ta gani idan Nuran ze aureta in ma abind akije saqawa a ranki kenan to sedai ya lalata miki rayuwar kamar yanda yace ya kashe miki aure kuma shi ba auranki zeyi ba dan daman kafin su bar unguwar ya dade yana fadar maganganu akan seya fito dake kuma na auranki zeyi ba sakarya shine har zaki taka kije inda yake. Daga nan shima gidansu zani na samu Hajiya Asaben" Mama ta fada tana miqewa tsaye ta kalli Khalil tace
"Kar kaji komai Khalil in kaga ba zaka iya ba ka sakota duk inada labarin diban Albarkar da take maka ai ta dawo gidan taga idan zawarcin da take sha'awa wasane, abinda take rainawar se naga a gidan ubanda zata same shi".
Kamar qasa ta tsage su shige shida Hunairan, wannan tonon silili da yawa yake dai Mama ta fice Hajiya ta bita rai babu dadi datasan haka zata dauki abin da bata gaya mata ba. Seda ta rakata ta dawo ta sake hadasu su biyun tayi musu fada da Nasiha kafin suka koma bangarensu, fita yayi niyyar yi amma ya haqura ya zauna ta ringa kuka tana bashi haquri da rantsuwar ba abinda yake tsammani bane.
"Wlh bansan a Lab yake ba, kuma danaje duk Matan sunyi sun kasa dubo jijiyar ne" ta miqa masa hannu ta se sannan yaga kumburin da yayi taci gaba da cewa
"Sun kasa ganin jijiyar se caka mun Allura sukeyi shiyasa ya karba yace zeyi amma wlh dana shiga koda na gaishe shima dauke kai yayi be amsa ba"
"To murmushin da yakeyi yana shafa hannunki fa?" Khalil ya sake tambaya dan abin nan ya tsaya masa a rai seta cigaba da kuka tana cewa
"Wlh badani yake ba kuma ba shafawa yakeyi ba jijiya yake dannanwa hirar su sukeyi suna labarin wani abokin aikinsu aida ka kalle su duka dariya sukeyi ba shi kadai bane" se kuma yaji wani iri dan da gaske take dukkansu dariyar sukeyi amma a lokacin dauka yayi su sukewa Dariyar ganin yanda tayi da fuska shi kuma yana mata murmushi, be nuna mata nadamar zaton daya qulla ba ya miqe yana cewa
"To se ki dena kukan haka kuma Test dinna menene gashi ba'ayi ba?"
"Toh saboda ina da lalura shine zata ringa kula wasu Mazan a waje?" Maganar ta subuto daga bakinsa ba tareda ya shirya ba take kuwa Hajiya tayi tsit saga bambamin da takeyi qirjinta ya shiga dokawa ta kalli Khalil da shima yayi tsilli tsilli saboda subul da bakan da yayi, a sanyaye tace
"Babana me kace? Wane mqza take kulawa a waje?"
"Am ni ba haka nace ba, kawai dai ki bar maganar dan Allah Hajiya ta kwana gobe da safe ta dawo shikenan" ya fada yana qoqarin miqewa seta daka masa tsawa tana cewa
"Bana son rashin arziqi, ka dakko magana irin wannan sannan ka tashi kana neman bagarar da ita kasan me kake cewa kuwa? Maza fa naji kayi zancen tana kulawa a waje, koma ka Zauna Khalil ka gaya mun gaskiya ka samu lafiya da gaske kuwa? kuma wane irin zama kukeyi? tun yaushe hakan take faruwa?"
Zaman yayi gaba daya ya rasa me zece mata ganin ta rikice ya tabbata fassarar datayi wa maganar daban da abinda Yakima nufi dole ya tattaro nutsuwarsa jin tana cewa
"Cikin jikinta kuma fa a ina aka sameshi" se yayi saurin cewa
"Haba Hajiya abin be kai nan ba, bafa irin kula Mazan da kike tunani bane nine ban daka miki maganar a yanda zaki fahimta ba daman wannan yaron saurayinta ne yake aiki a Asibitin Al'amin, tun randa muka fara ganinsa naja mata kashedi akan sa amma bataji ba shine yau.." Tiryan tiryan ya labarta mata komai ya qara da cewa
"Ni daman nasan ba wata rashin lafiya kawai ta shirya zuwa ta ganshi ne, na gaya mata ta zaba koni koshi, idanta zabeshi wlh data haihu zan sawwaqe mata taje suyi aure bazan tauyeta ba dan nasan zaman haquri takeyi dani bawai samun yanda take so takeyi ba" yayi maganar kansa a qasa saboda nauyinta.
Hajiya ta sauke numfashi saboda jin abin beyi girman data zata ba amma dukda haka hankalinta be kwanta ba dan ita fitina tana qarama idan ba'a maganceta ba girma takeyi. A hankali tace
"Bata kyauta ba amma kaima kayi saurin yanke hukunci wannan ai abinda za'azo gida a sasantane ba wai seka turata gidansu ba. Sannan shedan ne kawai yake tunzuraka yana qara rura maka wutar kishi amma babu wani abu, aikinsa yakeyi ita kuma kace likita ta turata yin test kaga baze yuwu ai tace ba ze dauki Jininta ba tunda shine a gurin"
"Amma ai bashi kadai bane a gurin Hajiya, data san tsakaninsu akan me zata bashi jikinta har ya wani riqeta yana shafata yana murmushi? Daman ai ya fada mun se ya zama fitina a rayiwarmu to gara kafin muga fitina taje can ta aureshi su qarata ni na haqura" ya sake fada idonsa nayin Jaa dan abin ya bala'in qona masa rai se Hajiya tayi saurin cewa
"Ashsha ka dena cewa haka Mana Babana shaidan ne kawai ya haska maka haka babu tabbacin ma murmushin yakeyi sannan waccen magana daya fada na tabbata a lokacin cikin fushi ne shima bazamuga fitina ba da yardar Allah amma koma yayane kayi haquri tayi kuskure kuma ba za'a sake ba ka daure dan ni badan halin taba ka daukota ta dawo gida karka ja mana abin fada, kana ji har yar uwarka ta fara jifan tsohuwar matarka da cewar Asiri tayi muku to lallaba ka dawo da matarka kafin kasa can itama a fara jefa mata wani zargin, Mace da tsohon ciki haihuwa kowanne lokaci a turata gida ai abin a tambayi ba'asine, zan gayawa Hauwa na tabbata zatayiwa tufkar hanci ba za'a sake yin hakan ba kaji" Hajiya ta shiga lallabashi dole badan yaso na ya tafi ya daukota, harta kwanta Mama ta tasheta akan Khalil yazo ta zare ido tana shirin yin kuka ita dai data barta ta kwana gobe koma me za'ayi ayi amma ya ta iya haka suka kama hanya har sukaje gida be kulata ba. Sum sum ta shige bangarenta shima yayi nasa, yara duk sunyi bacci dan haka itama ta kwanta washe gari kuwa qarfe tara Mama ta dira a gidan dan Hajiya kasa bacci tayi saboda zullumi seda ta kirata ta gaya mata komai.
Irin labaran da take yawan ji akan Tsohon saurayi da budurwa yasa ta kasa samun nutsuwa, bata zargin Humairan da wani banzan hali amma shaidan abin tsoro ne musamman su da suke da baraka yana iya amfani da wannan damar ya kaisu ga abinda ba za'a so ba ga kuma maganar shi yaron da Khalil yace mata ya taba gaya masa tuna shekarun baya na cewar ya jira ya gani, seya zama fitina a rayuwarsu idan har qullin na nan a ransa har yanzu gara ayiwa tufkar hanci da wuri kafin azo ana kukan da an sani.
Tana shiga kafin takai qasa Mama Hauwa ta dauketa da Marin daya gigitata, Khalil dake bayabta ya tareta dan tafiya tayi zata fadi ta kuwa fashe da kuka dan hannun Mama badai zafi ba kamar na maza haka yake. Ta shiga surfa mata bala'i tana zaginta, duk yanda Hajiya taso ta tausheta taqiyin shiru seda tayi mata tatas tana cewa
"Saboda bakida hankali baki saninda yake miki ciwo ba, ke ko a hanya kika ga Nura ya kamata kibi inda yabi yaron daya sha Alwashin lalata rayuwarki shine kike bibiya wato ki bashi damar aiwatar da shirinsa a sauqaqe kenan to ki jini da kyau idan kika kashe auranki sedai ki san inda zaki nufa badai gidana ba tunda ke baki san abin arziqi ba".
"Haba Hajiya abinfa bekai haka ba, na sanar dake ne kawai saboda ya kamata ace kin sani amma badan ki dau abinda zafi ki ringa maganganu haka ba, naga kinada alaqa da uwar yaron zaki iya mata magana taja masa kunne ya fita a sabgarta shikenan ba se anje ga wannan tone tonen ba" Hajiya ta fada, Khalil dai yana riqe da Humaira dake gunsheqar kuka idonsa ya kada yayi jaa shima kamar yayi kukan daya sani be sanarwa da Hajiya ba, beyi tsammanin zata fadawa Mama maganar ba gashi yanzun abin nema yake ya qara girmama.
"Ki barni da mutuniyar banza Hajiya wannan yarinyar da kike gani kunnen qashi ne da ita ai, banda ma abu irin na yaran zamani ina ke ina kula wani tsohon saurayi da auranki duk ba daga nan fitinu suke bullowa ba wai se suce mutunchi mutunchin yaci uwarsa da ubansa ai tunda soyayya ta gifta Shaidan na iya shiga ya taka rawa son ransa yayi abinda yaga dama dan haka kowa ya zauna a iyakarsa babu wani mutunchi da tsohon masoyi ai da ka sani tun jiyan ka fada mun da bazata dawo ba seta zauna a gidan idan yaso ka saketa ta gani idan Nuran ze aureta in ma abind akije saqawa a ranki kenan to sedai ya lalata miki rayuwar kamar yanda yace ya kashe miki aure kuma shi ba auranki zeyi ba dan daman kafin su bar unguwar ya dade yana fadar maganganu akan seya fito dake kuma na auranki zeyi ba sakarya shine har zaki taka kije inda yake. Daga nan shima gidansu zani na samu Hajiya Asaben" Mama ta fada tana miqewa tsaye ta kalli Khalil tace
"Kar kaji komai Khalil in kaga ba zaka iya ba ka sakota duk inada labarin diban Albarkar da take maka ai ta dawo gidan taga idan zawarcin da take sha'awa wasane, abinda take rainawar se naga a gidan ubanda zata same shi".
Kamar qasa ta tsage su shige shida Hunairan, wannan tonon silili da yawa yake dai Mama ta fice Hajiya ta bita rai babu dadi datasan haka zata dauki abin da bata gaya mata ba. Seda ta rakata ta dawo ta sake hadasu su biyun tayi musu fada da Nasiha kafin suka koma bangarensu, fita yayi niyyar yi amma ya haqura ya zauna ta ringa kuka tana bashi haquri da rantsuwar ba abinda yake tsammani bane.
"Wlh bansan a Lab yake ba, kuma danaje duk Matan sunyi sun kasa dubo jijiyar ne" ta miqa masa hannu ta se sannan yaga kumburin da yayi taci gaba da cewa
"Sun kasa ganin jijiyar se caka mun Allura sukeyi shiyasa ya karba yace zeyi amma wlh dana shiga koda na gaishe shima dauke kai yayi be amsa ba"
"To murmushin da yakeyi yana shafa hannunki fa?" Khalil ya sake tambaya dan abin nan ya tsaya masa a rai seta cigaba da kuka tana cewa
"Wlh badani yake ba kuma ba shafawa yakeyi ba jijiya yake dannanwa hirar su sukeyi suna labarin wani abokin aikinsu aida ka kalle su duka dariya sukeyi ba shi kadai bane" se kuma yaji wani iri dan da gaske take dukkansu dariyar sukeyi amma a lokacin dauka yayi su sukewa Dariyar ganin yanda tayi da fuska shi kuma yana mata murmushi, be nuna mata nadamar zaton daya qulla ba ya miqe yana cewa
"To se ki dena kukan haka kuma Test dinna menene gashi ba'ayi ba?"