Sashe 215
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nima haka na gani kuma jiya munyi magana dashi a yanda na fahimta dai qila da akwai cikin dan be musa ba dana fada" Mama taja Kabbara tace
"Kin gani ko? Allah kadai yasan abinda ya boye cikin auran nan dan haka ayi haquri a bi komai a sannu shi kuma Allah ya bashi lafiya yasa kaffara ne zan saka Sumayya ko Unaizatu suje gidan suyi magana da ita idan ma akwai wata damuwa wadda nake fatan babu zasuji Allah ya shige mana gaba"
"Amin Hajiya mun gode Allah ya saka da Alkhairi na sani abubuwan da suka faru daga fara neman auran nan zuwa yanzu yanzu da a waje Khalil yaje da ba'ayi shi ba koda anyi da yanzu gari kaf ya gama jin abinda ake ciki Mungode" Hajiya ta sake fada Se Mama Hauwa tace
"Haba dai Hajiya mu daku ai daya ne dan ni yanda Mansur yake a gurina haka na dauki Khalil shi yasa banji ko dar ba na bashi auran Humaira domin nasan ze kula da ita kuma Alhamdulillahi bana nadamar hada auransu ba"
"Allah ya jishshemu Alkhairi Hajiya, bari naje se na sake zagayowa" daga haka sukayi sallama ta tafi. Hajiya na tafiya Mama Hauwa ta kira Unaizatu, sunfi fahimta da Humairan dan haka ita zata saka tayi mata wannan aikin. Washe garin ranar kuwa Unaizatu tayiwa gidan Humairan tsinke da sassafe dan ba qaramin kaduwa tayi da jin Al'amarin ba taya ma za'a yi yarinya qarama kamar Humaira da bata san komai a cikin rayuwa ba ace tayi irin wannan zaman? Gangan kenan. Bata nunawa Mama komai ba tace mata dai goben zata je a ranta ta qudure niyyar baiwa yar uwarta shawarar data kamata dan ba zata zuba ido a saka yarinya qara ma a tasku ba. Sanda taje ta tarar da Khalil a gidan be fita ba saboda Humaira data tashi bata jin dadi suka gaisa cikin mutuntawa shi ya kawo mata Ruwa da lemo da abin tabawa dan basu rigada sun dauki me aiki ba tunda Ruqayya ta tafi seda ya ajiye mata komai kafin ya shiga ya kirawo Humairan data dan kwanta ta huta.
Tana ganin Unaizatun ta fasa ihun murna ta fada jikinta Khalil ya bude ido yace
"Kiyi a hankali fa karki jima kanki ciwo, seya juya dakin yana cewa
"Tunda kin samu abokiyar hira bari naje Anwar yana jirana bazan jima ba zan dawo" be jima ba ya fito a shirye yayi musu sallama ya fita bayan ya cewa Unaizatun karta tafi ta jirashi jintana cewa ba dadewa zatayi ba ya fita ya barsu.
Humaira kuwa rasa inda zata saka ranta don murna tayi, Anty Unaizan bata taba zuwa gidan ba tayi nacin harta gaji se yau gata bagatatan tazo mata.
"Muje ku gaisa da Hajiya Anty se na girka miki duk abinda kike so" ta fada tana kama Hannunta Unaiza tayi dariya tace
"To yar Hajiya ai can na fara shiga kafin nazo nan ya jikin tace baki ji dadi ba"
"Ni ai na warke kawai bana so ya fita ne daman shiyasa na langwabe" Hunaira ta fada tana tura baki se Unaizatu ta kama haba tace
"Lallai yarinyar nan to idan be fita ba so kike ya zauna kuci soyayya kenan?"
"Eh mana Anty ni bana so yana fita yana barina ni kadai gara ya zauna inyiyi masa shagwaba yana lallashina"
"Ikon Allah" Unaizatu ta fada jin abin bana wasa bane, seta miqe tana cewa
"Muje dakinki to magana nazo muyi" Humaira ta miqe tayi gaba Unaizatun na biye da ita a baya suka shiga falonta. A Bedroom suka qule kan Gado Unaizatu se qare mata kallo take ganin yanda ta canza gaba daya ta cika kamar ba ita ba ga wani haske data qara masha Allah kamar seka wanke hannu ka taba. A nutse kuma cikin dabara take bugar cikinta dan taji koda wata matsala daga bakinta amma bataji komai ba hakan yasa ta gyara zamanta dakyau tana kallonta tace
"Kinsan abinda ya kawoni maganar rashin lafiyar Mijinki ce jiya Hajiya taje gurin Mama tayi mata bayanin komai akan abinda ya same shi dalili daya sa tace mu tambayeki kenan kar kiji kunya ko nauyi ki fadi tsakaninki da Allah idan kina son zama dashi"
"Bangane ba Anty wani abu ya samu Yaya Khalil ne daga baya ko daman be warke bane?" Humairan ta fada cikin rashin fahimta se Unaizatu ta gyara zama tana kallonta tace
"Yace miki ya warke ne ko ke kinga alamar hakan?"
"Toh Anty tunda aka sallaameshi daga Asibiti ya warke kenan shekaran jiya nema dai daya dawo naga kamar bashida lafiya kuma yace qalau yake gashi nan ma kin ganshi ai yanzu" Humairan ta sake fada innocently se Unaizatu taja tsaki tace
"Bana son sakarci ki nutsu ki gaya mun gaskiya tun bayan da kika tare wata Mu'amalar aure ta shiga tsakaninku ne?"
Kafin ma ta rufe baki Humairan ta juya baya ta rufe fuska wai kunya Unaizatu ta dana mata duka a baya ta gantsare tareda yin ihu dan dukanya shgeta bata barta ba a fusace tace
"Dan ubanki ki juyo ki bude baki kiyi mun magana kunyar uwar me zakiji ana neman yanda za'a kwatar miki yanci kin zauna kinawa mutane yarinta da shirme nace kun taba kwanciyar aure da Khalil bayan kin tare a gidan ko yaya?"
Baki ta tura kamar zatayi kuka tana soshe soshe ba tareda ta bari sunhada ido ba tace
"Sau daya ne ranar da aka kawoni da daddare"
"Bayan nan fa? Tunda aka sallamo shi daga Asibiti ya nemeki?" Ta sake jefa mata wata tambayar zuciyarta na bugawa da jin ya kwanta da Humairan, sam bata so haka ba, taso ko rabuwar zasuyi ta fita a yanda tazo amma aikin gama ya gama.
Baki Humairan ta sake tunzurawa tace
"No shike nan sau dayane to wai tambayar mecece ma haka bayan bake kikace karna ringa yin hira da kowa ba koda kece ko Anty Sumayya kuma yanzu kin zo kina ta tambayata"
A hasale Unaizatu tace
"Dole kimun rashin kunya mana tunda yanzu mun zama kai daya kema kin san Namiji, to bari kiji tunda naga har yanzu yarinya na damunki baki ma san abinda yake faruwa ba Rashin lafiyar da Mijinki yayi kayan aikin sa ne ya samu matsala, a taqaice dai ina nufin dake dashi yanzu marabar ku kadance dan baze iya miki abinda sauran Maza sukeyi ba. Daman zuwan da nayi Mama ce ta turo ni akan na tambayeki kina son Mijinki zaki ci gaba da zama dashi da lalurar sa ko kuwa ba haka ba? Sannan in miki dalla dalla zama dashi da lalura yana nufin babu haihuwa tunda ba harka yawwa dan nasan kanki ba ja yake da kyau ba".
Tayi fakare tana kallon Unaizatu danharga Allah kam bata gane me take nufi ba, maganar haihuwa kadai ta tsinta wannan kuma in ta fassara daidai tana nufin Khalil baya haihuwa to Mu'ayyad da Bibi yayan waye?
"Kin tsaya kina kallona kamar wawiya ko baki gane me nake nufi ba?" Unaizatu ta sake fada ganin irin kallon da take mata seta daga mata kai alamar haka ne bata gane ba, takaici ya qume Unaizatu, bayan yarintar Humaira harda rashin wayewa saboda gaba daya rayuwarta ta tashi ne tsakanin Makaranta se Mama, qawayenta kuma duk yara ne kamarta lissafinsu da tunaninsu be san wadannan abubuwanba a da suna jin dadin rashin wayewar kannata domin hakan ma wani mataki ne na kariya daga fitina amma yanzu titsiyen nanda tayi mata na seta fadi komai gatsal gatsal yasa taji haushin rashin iliminta ko yaya ne a wannan bangaren.
Cikin dakewa tace
"Ai kin san Manhood a biology ko?" Seta sake daga kai alamar ta sani ta zaburo mata tace
"Ki bude baki kika sake daga mun kai kamar qadangaruwa sena mareki kin sani ko baki sani ba?"
"Na sani" Humairan ta fada tana sunkuyar da kai a ranta tana hakaito na Khalil daya kusa kasheta dashi.
"Yawwa to shi wannan abin nake nufi tsohuwar kishiyarki data kwada masa abu akai hakan yasa ya samu matsala baze iya kwanciya da Mace ba kinga kenan baze iya baki ciki ba" Unaizatu ta fada tana basarwa saboda kar Humairanta kawo mata raini ita kuwa dafe qirji tayi ta gwalalo ido tana kallonta jin abinda tace kafin bakinta na rawa tace
"Daman a nan ta buga masa? Innalillahi shi yasa Yaya Khalil ya ringa ciwon ciki kamar ze mutu koda yake ai ance nan ne makasar Maza daman kenan kashi taso tayi?'
"Oho dai koma menene kinji abinda ake ciki, kuma dai kinsan shi aure badan aci abinci kawai ayi kashi ake yinsa ba akwai biyan buqata ta sha'awa, wannan abinda kike cewa kina ji a jikinki idan kin sha magunguna lokacin to shi ake nufi da Sha'awa koda yake ai kin ma san komai rainamun hankali kikeyi tunda kina zuwa Islamiyya an karanta muku komai" Inji Unaiza, Ita dai Humaira na cike da Jimamin abinda taji dan har idonta ya tara hawaye tausayin Khalil ya kamata ta tuna wani dan Ajinsu a makaranta suna Ball aka buga masa ita a gurin ya Suma dalilin cire shi kenan ita bata masan ya rayu ko ya mutu ba anan ne ma taji Mazan Ajinsu na fadar nan ne Makasar Maza yanzu ashe abinda ya samu Yaya Khalil kenan gaskiya Allah ya saka masa Maman Mu'ayyad muguwa ce.
"Toh yanzu dai seki zauna kiyiwa kanki tunani ki gani zaki iya zama dashi a haka ko kuwa saboda ke yarinya ce baki san komai ba a yanzu amma dukda haka babu me miki dole ke zaki zabarwa kanki abinda kike ganin shinr mafita a rayuwarki"
"Kin gani ko? Allah kadai yasan abinda ya boye cikin auran nan dan haka ayi haquri a bi komai a sannu shi kuma Allah ya bashi lafiya yasa kaffara ne zan saka Sumayya ko Unaizatu suje gidan suyi magana da ita idan ma akwai wata damuwa wadda nake fatan babu zasuji Allah ya shige mana gaba"
"Amin Hajiya mun gode Allah ya saka da Alkhairi na sani abubuwan da suka faru daga fara neman auran nan zuwa yanzu yanzu da a waje Khalil yaje da ba'ayi shi ba koda anyi da yanzu gari kaf ya gama jin abinda ake ciki Mungode" Hajiya ta sake fada Se Mama Hauwa tace
"Haba dai Hajiya mu daku ai daya ne dan ni yanda Mansur yake a gurina haka na dauki Khalil shi yasa banji ko dar ba na bashi auran Humaira domin nasan ze kula da ita kuma Alhamdulillahi bana nadamar hada auransu ba"
"Allah ya jishshemu Alkhairi Hajiya, bari naje se na sake zagayowa" daga haka sukayi sallama ta tafi. Hajiya na tafiya Mama Hauwa ta kira Unaizatu, sunfi fahimta da Humairan dan haka ita zata saka tayi mata wannan aikin. Washe garin ranar kuwa Unaizatu tayiwa gidan Humairan tsinke da sassafe dan ba qaramin kaduwa tayi da jin Al'amarin ba taya ma za'a yi yarinya qarama kamar Humaira da bata san komai a cikin rayuwa ba ace tayi irin wannan zaman? Gangan kenan. Bata nunawa Mama komai ba tace mata dai goben zata je a ranta ta qudure niyyar baiwa yar uwarta shawarar data kamata dan ba zata zuba ido a saka yarinya qara ma a tasku ba. Sanda taje ta tarar da Khalil a gidan be fita ba saboda Humaira data tashi bata jin dadi suka gaisa cikin mutuntawa shi ya kawo mata Ruwa da lemo da abin tabawa dan basu rigada sun dauki me aiki ba tunda Ruqayya ta tafi seda ya ajiye mata komai kafin ya shiga ya kirawo Humairan data dan kwanta ta huta.
Tana ganin Unaizatun ta fasa ihun murna ta fada jikinta Khalil ya bude ido yace
"Kiyi a hankali fa karki jima kanki ciwo, seya juya dakin yana cewa
"Tunda kin samu abokiyar hira bari naje Anwar yana jirana bazan jima ba zan dawo" be jima ba ya fito a shirye yayi musu sallama ya fita bayan ya cewa Unaizatun karta tafi ta jirashi jintana cewa ba dadewa zatayi ba ya fita ya barsu.
Humaira kuwa rasa inda zata saka ranta don murna tayi, Anty Unaizan bata taba zuwa gidan ba tayi nacin harta gaji se yau gata bagatatan tazo mata.
"Muje ku gaisa da Hajiya Anty se na girka miki duk abinda kike so" ta fada tana kama Hannunta Unaiza tayi dariya tace
"To yar Hajiya ai can na fara shiga kafin nazo nan ya jikin tace baki ji dadi ba"
"Ni ai na warke kawai bana so ya fita ne daman shiyasa na langwabe" Hunaira ta fada tana tura baki se Unaizatu ta kama haba tace
"Lallai yarinyar nan to idan be fita ba so kike ya zauna kuci soyayya kenan?"
"Eh mana Anty ni bana so yana fita yana barina ni kadai gara ya zauna inyiyi masa shagwaba yana lallashina"
"Ikon Allah" Unaizatu ta fada jin abin bana wasa bane, seta miqe tana cewa
"Muje dakinki to magana nazo muyi" Humaira ta miqe tayi gaba Unaizatun na biye da ita a baya suka shiga falonta. A Bedroom suka qule kan Gado Unaizatu se qare mata kallo take ganin yanda ta canza gaba daya ta cika kamar ba ita ba ga wani haske data qara masha Allah kamar seka wanke hannu ka taba. A nutse kuma cikin dabara take bugar cikinta dan taji koda wata matsala daga bakinta amma bataji komai ba hakan yasa ta gyara zamanta dakyau tana kallonta tace
"Kinsan abinda ya kawoni maganar rashin lafiyar Mijinki ce jiya Hajiya taje gurin Mama tayi mata bayanin komai akan abinda ya same shi dalili daya sa tace mu tambayeki kenan kar kiji kunya ko nauyi ki fadi tsakaninki da Allah idan kina son zama dashi"
"Bangane ba Anty wani abu ya samu Yaya Khalil ne daga baya ko daman be warke bane?" Humairan ta fada cikin rashin fahimta se Unaizatu ta gyara zama tana kallonta tace
"Yace miki ya warke ne ko ke kinga alamar hakan?"
"Toh Anty tunda aka sallaameshi daga Asibiti ya warke kenan shekaran jiya nema dai daya dawo naga kamar bashida lafiya kuma yace qalau yake gashi nan ma kin ganshi ai yanzu" Humairan ta sake fada innocently se Unaizatu taja tsaki tace
"Bana son sakarci ki nutsu ki gaya mun gaskiya tun bayan da kika tare wata Mu'amalar aure ta shiga tsakaninku ne?"
Kafin ma ta rufe baki Humairan ta juya baya ta rufe fuska wai kunya Unaizatu ta dana mata duka a baya ta gantsare tareda yin ihu dan dukanya shgeta bata barta ba a fusace tace
"Dan ubanki ki juyo ki bude baki kiyi mun magana kunyar uwar me zakiji ana neman yanda za'a kwatar miki yanci kin zauna kinawa mutane yarinta da shirme nace kun taba kwanciyar aure da Khalil bayan kin tare a gidan ko yaya?"
Baki ta tura kamar zatayi kuka tana soshe soshe ba tareda ta bari sunhada ido ba tace
"Sau daya ne ranar da aka kawoni da daddare"
"Bayan nan fa? Tunda aka sallamo shi daga Asibiti ya nemeki?" Ta sake jefa mata wata tambayar zuciyarta na bugawa da jin ya kwanta da Humairan, sam bata so haka ba, taso ko rabuwar zasuyi ta fita a yanda tazo amma aikin gama ya gama.
Baki Humairan ta sake tunzurawa tace
"No shike nan sau dayane to wai tambayar mecece ma haka bayan bake kikace karna ringa yin hira da kowa ba koda kece ko Anty Sumayya kuma yanzu kin zo kina ta tambayata"
A hasale Unaizatu tace
"Dole kimun rashin kunya mana tunda yanzu mun zama kai daya kema kin san Namiji, to bari kiji tunda naga har yanzu yarinya na damunki baki ma san abinda yake faruwa ba Rashin lafiyar da Mijinki yayi kayan aikin sa ne ya samu matsala, a taqaice dai ina nufin dake dashi yanzu marabar ku kadance dan baze iya miki abinda sauran Maza sukeyi ba. Daman zuwan da nayi Mama ce ta turo ni akan na tambayeki kina son Mijinki zaki ci gaba da zama dashi da lalurar sa ko kuwa ba haka ba? Sannan in miki dalla dalla zama dashi da lalura yana nufin babu haihuwa tunda ba harka yawwa dan nasan kanki ba ja yake da kyau ba".
Tayi fakare tana kallon Unaizatu danharga Allah kam bata gane me take nufi ba, maganar haihuwa kadai ta tsinta wannan kuma in ta fassara daidai tana nufin Khalil baya haihuwa to Mu'ayyad da Bibi yayan waye?
"Kin tsaya kina kallona kamar wawiya ko baki gane me nake nufi ba?" Unaizatu ta sake fada ganin irin kallon da take mata seta daga mata kai alamar haka ne bata gane ba, takaici ya qume Unaizatu, bayan yarintar Humaira harda rashin wayewa saboda gaba daya rayuwarta ta tashi ne tsakanin Makaranta se Mama, qawayenta kuma duk yara ne kamarta lissafinsu da tunaninsu be san wadannan abubuwanba a da suna jin dadin rashin wayewar kannata domin hakan ma wani mataki ne na kariya daga fitina amma yanzu titsiyen nanda tayi mata na seta fadi komai gatsal gatsal yasa taji haushin rashin iliminta ko yaya ne a wannan bangaren.
Cikin dakewa tace
"Ai kin san Manhood a biology ko?" Seta sake daga kai alamar ta sani ta zaburo mata tace
"Ki bude baki kika sake daga mun kai kamar qadangaruwa sena mareki kin sani ko baki sani ba?"
"Na sani" Humairan ta fada tana sunkuyar da kai a ranta tana hakaito na Khalil daya kusa kasheta dashi.
"Yawwa to shi wannan abin nake nufi tsohuwar kishiyarki data kwada masa abu akai hakan yasa ya samu matsala baze iya kwanciya da Mace ba kinga kenan baze iya baki ciki ba" Unaizatu ta fada tana basarwa saboda kar Humairanta kawo mata raini ita kuwa dafe qirji tayi ta gwalalo ido tana kallonta jin abinda tace kafin bakinta na rawa tace
"Daman a nan ta buga masa? Innalillahi shi yasa Yaya Khalil ya ringa ciwon ciki kamar ze mutu koda yake ai ance nan ne makasar Maza daman kenan kashi taso tayi?'
"Oho dai koma menene kinji abinda ake ciki, kuma dai kinsan shi aure badan aci abinci kawai ayi kashi ake yinsa ba akwai biyan buqata ta sha'awa, wannan abinda kike cewa kina ji a jikinki idan kin sha magunguna lokacin to shi ake nufi da Sha'awa koda yake ai kin ma san komai rainamun hankali kikeyi tunda kina zuwa Islamiyya an karanta muku komai" Inji Unaiza, Ita dai Humaira na cike da Jimamin abinda taji dan har idonta ya tara hawaye tausayin Khalil ya kamata ta tuna wani dan Ajinsu a makaranta suna Ball aka buga masa ita a gurin ya Suma dalilin cire shi kenan ita bata masan ya rayu ko ya mutu ba anan ne ma taji Mazan Ajinsu na fadar nan ne Makasar Maza yanzu ashe abinda ya samu Yaya Khalil kenan gaskiya Allah ya saka masa Maman Mu'ayyad muguwa ce.
"Toh yanzu dai seki zauna kiyiwa kanki tunani ki gani zaki iya zama dashi a haka ko kuwa saboda ke yarinya ce baki san komai ba a yanzu amma dukda haka babu me miki dole ke zaki zabarwa kanki abinda kike ganin shinr mafita a rayuwarki"