Sashe 123
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Numfashi yaja ya fitar kansa na kallon qofar palour da aka liqa wata sticker me qyalqyali an rubuta
'WELCOME HOME HABIBI" A jiki. Waiwayawa yayi ya kalli qaramin compound din da yayi qal Interlocks se daukar ido suke alamar sunsha shara da wanki ga wani daddadan qamshi turaren wuta da yake tashi kamar anyi barinsa a gurin. Da sallama ya tura qofar palour ya shiga, wani qamshi, sanyi, nutsuwa da ya rasa ta mecece suka bige shi lokaci daya, cikin seconds goma ya qarewa palour da babu kowa a ciki kallo. Gyaranda akayi masa is morethan perfect, yanda kasan babu wanda yake rayuwa a ciki saboda yanda komai ya zauna daidai a muhallindaya dace dashi haka ya fara jefa qafafunsa yana tafiya duk taku daya yana jin wata kewar gidanna kama shi, gaskiya masu magana sunyi gaskiya da suka ce no place like home.
Qofar dakinsa ya tura kai tsaye ya shiga da sallama a bakinsa, wani sabon qamshi na daban yayi masa maraba tareda fuskar kyakykyawar Diyarsa dake kwance akan gadon daya sha shimfida ta alfarma itama cikin irin shigar da yake so ya gani jikin yara kamar ta sanshi suna hada ido ta bangale masa bakinta da babu haqori ta qara qarfin gwalantoyin da takeyi daga kwancen. Be san sanda ya dire jakar hannunsa ya isa kan gadon ya dagata ba ya hadeta da qirjinsa yana kissing fuskarta ita kuwa se dariya take abinta.
Umaimah ta bude qofar bandakin da ta shiga tana hada masa ruwan wanka saboda Habiba ta kira ta gaya masa gashi nan a hanya ya baro gidan Hajiya. Daskarewa tayi daga bakin qofar, So, shauqi tareda kewarsa suka shiga shawagi da ita a sararin samaniyar qauna bata san yanda akayi ba se ganin kanta tayi a bayansa ba kuwa ta tsaya tunanin komai ba ta saka hannuwa biyu ta zagaye cikinsa dasu kafin ta dora kanta a bayansa se ji tayi hawaye suna bin kuncinta da ita kanta bata san na menene ba.
A bazata abun yazo masa dan sam beji fitowarta daga bandakin ba gaba daya hankalinsa nakan Yar Babyn tasa da yake jin qaunarta har qololuwa, da yanzu Umaimah ta salwantar masa da ita tab da kuwa ta cuce shi. Saukar hannun mutum kawai yaji a cikinsa se saukar abi me dumi da yatabbatar hawayene ya shiga ratsa jini da jijiyarsa har zuwa cikin bargonsa, sosai yayi ta maza ya dake ya kuma hana kansa juyowa dan yasan tarko ne, idan har ya bari tayi tasiri akansa shikenan duk wani shiri daya dawo dashi ya wargatse.
Hannu daya ya saka dayan na rungume da Bibi ya janye hannayen Umaimah data zagaye shi dasu ya fara takawa zuwa gana kujerar dake cikin dakin ya ajiye yarinyar ya shiga zame rigar coat din daya dora, hannunta ya sake ji a kafadarsa tana taya shi, kafin muryarta da tayi wani irin laushi da sanyi ta ratsa dodon kunnensa tana cewa
"Barka da zuwa Habibin Umaimah, banji shigowarka ba ina ciki ina hada maka ruwan wanka, u are highly welcome" ta qarasa cikin wani sauti daya sakashi saurin sakar mata rigar ta qarasa cireta kafin ta juyo ta shiga balle masa maballin farar yar cikin jikinsa suka shiga kallon juna ido cikin ido kowanne yana karantar tsantsar kewar sa cikin idon Dan uwansa, tana gama balle masa rigar be zata ba yajita cikin jikinsa gaba daya suka yi baya ya samu ya dafe kujerar gabansu tareda qanqameta yana qarewa fuskarta kallo data sha simple kwalliyar nan tata wato pawder da man lebe ta gyara kyawawan idanunta da kwalli da Mascara gashin idon sun qara tsaho da baqi.
Lumshe idonta tayi ta sake bude su akan sa kafin ta raba labbanta data pente da jan lipstick ta sake shafe su Lipbalm me maiqo se daukar ido sukeyi tayi kamar zatayi magana amma ba tace komai ba, Idan yace yace beji wani abu na yayi qary, wani sanyi yaji ya taso masa tun daga tafin qafa ya dire a kwakwalwarsa, wani irin kallo take masa na cikin ido dashi kadai yasan ma'anarsa kuma ji yakeyi tamkar ta saka muqulli tana bude duk wasu qofofin jikinsa da suka jima a rufe, numfashinta da yaji cikin nasa kafin ta kai ga aikata abinda ta niyyata zumbur ya tashi tareda ita a jikinsa, sauketa yayi a qasa kan qafafunta kafin ya juya ya shige bandaki yanajin yanda jikinsa yake harbawa ba tareda ya qarasa cire kayan jikinsa ba ya sakarwa kansa ruwan sanyi yana gangarowa daga gashin kansa har zuwa qafafunsa.
Bazece ga iya adadadin mintinan daya kwashe a qasan ruwan ba, gajiya yayi dan a maimakon ya samu sauqin abinda yake ji se ya zamana tamkar ma yana qara iza wutar ne. Cikin ruwan data hada masa a bahon wankaya shiga bayan da ya cire jiqaqqun kayan jikinsa ya kwanta a ciki tareda rufe idonsa so yake ya tunano duk tarin laifukan da tayi masa ko zasu dishashe abinda yake bijiro masa akanta amma abin takaici ko daya yaqi zuwa, idan ma sunzo sam sun gagara bata masa rai ballantana har su gushe kaifin abinda yake ji qarshe dai yayi wanka ya dauro towel din data rataye masa ya fito.
UMAIMAH
Da kallo ta rakashi harya shiga ya kullo qofar kafin ta sauke ajiyar zuciya ta zauna kusada Bibi dake ta wulga idanu tana kallon fitilar dakin. Gaba daya jiki ta yayi mugun sanyin da batajin zata ko iya tafiya, abinda ta hango cikin idonsa ya sake sare mata guiwoyi, dagaske ne Khalil ya tsaneta ya zatayi da ranta?
Tana nan zaune cikin duniyar Lissafi har ya kwashe mintocinsa ya fito daure da towel a qugunsa, Kallo ta bishi dashi kamar wata tsohuwar mayya, ya wuceta ya dauki wayarsa dake kan gado kafin ya koma gaban mudubi yaja kura ya zauna bayan dayayi yan danne danne a wayar ya saka a speaker
"Kaje Ten to Ten ka karbo mun usually meal dina yanzu" ya fada kafin ya latse wayar ya janyo Mansa ya fara shafawa.
Hadiye abinda ya tsaya mata a wuya tayi ta tashi dakyar ta isa kusa dashi, ta cikin mudubin yake qare mata kallo, doguwar fitted gown din data saka ta Dark Orange din Lace tayi bala'in yi mata kyau ta fito da duk wani tudu da komadar jikinta daya qara cika dam kamar zata fashe, saurin dauke kansa yayi sanda ta iso ta karbi Man daya diba ta shiga shafa masa a banyansa, daga shi har itan ba zasu misalta yanda sukeji ba, Ta gaka shafa masa a bayan ya juyo tana fuskantarsa, hannu biyu ta saka taja shafa masa man A fuskarsa da tasa gyara saboda jiya yayi Aski cikin muryarta da tayi rauni kamar zatayi Kuka tace
"Nayi maka abinci, kuma naji kana cewa a kawo maka"
"Oh, thanks" ya fada yana miqewa saboda ya tabbata idan ta sake bude baki tayi magana cutarsa kawia zatayi. Wardrobe ya bude ya dauko Jallabiyya da boxer ya saka ya sake dawoa inda take tsaye ya dauki turare ya fesa kafin ya juya ya dauki Bibi data bingire da bacci ya fice daga dakin.
A kan Dan gadonta da ya gani a gefen kijera ya kwantar da ita tareda pecking goshinta. Kai tsaye kan Dining din ya wuce ya kalli wasu Luxury warmer data zuzuzuba abincin a ciki su kadai kyan su ya isa ya saka ka cin abinda yake ciki ko bakayi niyya ba. Zama yayi ya bude babbar ciki, Tuwon shinkafa ne fari so a ciki, ya waiwaya ya kalli Umaimah data biyo bayansa kamar mara gaskiya, da yar mutunchi suke tashi zeyi ya dagata yayi juyi da ita dan kamar ta shiga zuciyarsa, abinda yake muradi kenan yaci har mafarki yake ya samu tuwo dan tunda ya tafi ko a ido be ganshi ba, zuwan da yayi kwanaki ma zaman hotel ya qare harya tafi be ci ba.
Qaramin murmushi ya sakar mata, Umaimah ta sauke ajiyar zuciya har yana ganin yanda maqogaronta yayi sama da qasa kafin ta taho kamar wahainiya ta shiga bude masa sauran warmers din. Miya kala biyu tayi masa, Miyar Egusi dataji duk wani kalar Wasali da ake sakawa miya ga hadaddiyar Kuka wadda tayi digiri a London tasha zabi da suka dagargaje saboda yanda ta bata lokaci ta dafu.
Dayan kwanon Jellop din shinkafa ce itama dai se wanda ya gani ga wani Musulmin peppe meat tsabar qyallin da yake kamar zaka ga fuskarka a jiki. Se casserole data zuba hadin potatoe Salad dayan kuma ganyan lattece yasha garnishing se wani bowl me kyau data zuba Samosa da spring roll ga kuma Jug din Coconut drink dana Zobo se Jarkokin ruwa me sanyi har diga yakeyi
Duk yanda yaso ya daure seda ya kama hannunta na dama ya sumbata, qarshen abincin sa kenan ta hada masa su, ga Tuwo ga shinkafa ga nama.ga kayan fulawa. Kadan ta zuba masa kowanne a plate yayi bismilla ya shiga ci yana kallon fuskarta data marairaice kamar marainiyar Mage, tuwo ya gutsira ya nufi bakinta dashi, Allah sarki yanda take abu se yaji kamar zata bashi tausayi amma ya kanne haka suka shiga cin abincin yana ci yana bata har suka gama ba tareda wani yace qala ba.
Ita ta kwashe kayan ta kai kitchen ta dawo ta goge gurin harda fesa freshner, a ransa yace
"Ikon Allah, su Umaimah course din tsafta aka yo kenan yana kallo ta ta shige daki babu dadewa ta fito ta zauna akan kujerar gefensa.
"Na same ku lafiya?" Ya fada yana chanza channel, da sauri ta amsa masa ya daga kai ya kalleta, yanda take muimui da baki alamar tana son yin magana se juya yatsunta take kamar me jin tsoron yayi bala'in sake kunna shi.
"Kaak...kayi haquri dan Allah" ta fada dakyar hawaye na kawowa idonta, banza ya mata yaci gaba da chanza channel din da yakeyi
"Dan Allah Khalil ka yafe mun, wallahi sharrin shaidan ne bazan sake ba" ta sake fada cikin muryar kuka"
juyowa yayi ya kalleta, a cikin idonta ya karanci laushin da tayi na gaske ne ya kuma tabbatar da wannan ladabin bana qarya bane da gaske takeyi amma dukda haka baze saki da sauri ba, haka nan baze fasa qudurinsa akanta ba.
'WELCOME HOME HABIBI" A jiki. Waiwayawa yayi ya kalli qaramin compound din da yayi qal Interlocks se daukar ido suke alamar sunsha shara da wanki ga wani daddadan qamshi turaren wuta da yake tashi kamar anyi barinsa a gurin. Da sallama ya tura qofar palour ya shiga, wani qamshi, sanyi, nutsuwa da ya rasa ta mecece suka bige shi lokaci daya, cikin seconds goma ya qarewa palour da babu kowa a ciki kallo. Gyaranda akayi masa is morethan perfect, yanda kasan babu wanda yake rayuwa a ciki saboda yanda komai ya zauna daidai a muhallindaya dace dashi haka ya fara jefa qafafunsa yana tafiya duk taku daya yana jin wata kewar gidanna kama shi, gaskiya masu magana sunyi gaskiya da suka ce no place like home.
Qofar dakinsa ya tura kai tsaye ya shiga da sallama a bakinsa, wani sabon qamshi na daban yayi masa maraba tareda fuskar kyakykyawar Diyarsa dake kwance akan gadon daya sha shimfida ta alfarma itama cikin irin shigar da yake so ya gani jikin yara kamar ta sanshi suna hada ido ta bangale masa bakinta da babu haqori ta qara qarfin gwalantoyin da takeyi daga kwancen. Be san sanda ya dire jakar hannunsa ya isa kan gadon ya dagata ba ya hadeta da qirjinsa yana kissing fuskarta ita kuwa se dariya take abinta.
Umaimah ta bude qofar bandakin da ta shiga tana hada masa ruwan wanka saboda Habiba ta kira ta gaya masa gashi nan a hanya ya baro gidan Hajiya. Daskarewa tayi daga bakin qofar, So, shauqi tareda kewarsa suka shiga shawagi da ita a sararin samaniyar qauna bata san yanda akayi ba se ganin kanta tayi a bayansa ba kuwa ta tsaya tunanin komai ba ta saka hannuwa biyu ta zagaye cikinsa dasu kafin ta dora kanta a bayansa se ji tayi hawaye suna bin kuncinta da ita kanta bata san na menene ba.
A bazata abun yazo masa dan sam beji fitowarta daga bandakin ba gaba daya hankalinsa nakan Yar Babyn tasa da yake jin qaunarta har qololuwa, da yanzu Umaimah ta salwantar masa da ita tab da kuwa ta cuce shi. Saukar hannun mutum kawai yaji a cikinsa se saukar abi me dumi da yatabbatar hawayene ya shiga ratsa jini da jijiyarsa har zuwa cikin bargonsa, sosai yayi ta maza ya dake ya kuma hana kansa juyowa dan yasan tarko ne, idan har ya bari tayi tasiri akansa shikenan duk wani shiri daya dawo dashi ya wargatse.
Hannu daya ya saka dayan na rungume da Bibi ya janye hannayen Umaimah data zagaye shi dasu ya fara takawa zuwa gana kujerar dake cikin dakin ya ajiye yarinyar ya shiga zame rigar coat din daya dora, hannunta ya sake ji a kafadarsa tana taya shi, kafin muryarta da tayi wani irin laushi da sanyi ta ratsa dodon kunnensa tana cewa
"Barka da zuwa Habibin Umaimah, banji shigowarka ba ina ciki ina hada maka ruwan wanka, u are highly welcome" ta qarasa cikin wani sauti daya sakashi saurin sakar mata rigar ta qarasa cireta kafin ta juyo ta shiga balle masa maballin farar yar cikin jikinsa suka shiga kallon juna ido cikin ido kowanne yana karantar tsantsar kewar sa cikin idon Dan uwansa, tana gama balle masa rigar be zata ba yajita cikin jikinsa gaba daya suka yi baya ya samu ya dafe kujerar gabansu tareda qanqameta yana qarewa fuskarta kallo data sha simple kwalliyar nan tata wato pawder da man lebe ta gyara kyawawan idanunta da kwalli da Mascara gashin idon sun qara tsaho da baqi.
Lumshe idonta tayi ta sake bude su akan sa kafin ta raba labbanta data pente da jan lipstick ta sake shafe su Lipbalm me maiqo se daukar ido sukeyi tayi kamar zatayi magana amma ba tace komai ba, Idan yace yace beji wani abu na yayi qary, wani sanyi yaji ya taso masa tun daga tafin qafa ya dire a kwakwalwarsa, wani irin kallo take masa na cikin ido dashi kadai yasan ma'anarsa kuma ji yakeyi tamkar ta saka muqulli tana bude duk wasu qofofin jikinsa da suka jima a rufe, numfashinta da yaji cikin nasa kafin ta kai ga aikata abinda ta niyyata zumbur ya tashi tareda ita a jikinsa, sauketa yayi a qasa kan qafafunta kafin ya juya ya shige bandaki yanajin yanda jikinsa yake harbawa ba tareda ya qarasa cire kayan jikinsa ba ya sakarwa kansa ruwan sanyi yana gangarowa daga gashin kansa har zuwa qafafunsa.
Bazece ga iya adadadin mintinan daya kwashe a qasan ruwan ba, gajiya yayi dan a maimakon ya samu sauqin abinda yake ji se ya zamana tamkar ma yana qara iza wutar ne. Cikin ruwan data hada masa a bahon wankaya shiga bayan da ya cire jiqaqqun kayan jikinsa ya kwanta a ciki tareda rufe idonsa so yake ya tunano duk tarin laifukan da tayi masa ko zasu dishashe abinda yake bijiro masa akanta amma abin takaici ko daya yaqi zuwa, idan ma sunzo sam sun gagara bata masa rai ballantana har su gushe kaifin abinda yake ji qarshe dai yayi wanka ya dauro towel din data rataye masa ya fito.
UMAIMAH
Da kallo ta rakashi harya shiga ya kullo qofar kafin ta sauke ajiyar zuciya ta zauna kusada Bibi dake ta wulga idanu tana kallon fitilar dakin. Gaba daya jiki ta yayi mugun sanyin da batajin zata ko iya tafiya, abinda ta hango cikin idonsa ya sake sare mata guiwoyi, dagaske ne Khalil ya tsaneta ya zatayi da ranta?
Tana nan zaune cikin duniyar Lissafi har ya kwashe mintocinsa ya fito daure da towel a qugunsa, Kallo ta bishi dashi kamar wata tsohuwar mayya, ya wuceta ya dauki wayarsa dake kan gado kafin ya koma gaban mudubi yaja kura ya zauna bayan dayayi yan danne danne a wayar ya saka a speaker
"Kaje Ten to Ten ka karbo mun usually meal dina yanzu" ya fada kafin ya latse wayar ya janyo Mansa ya fara shafawa.
Hadiye abinda ya tsaya mata a wuya tayi ta tashi dakyar ta isa kusa dashi, ta cikin mudubin yake qare mata kallo, doguwar fitted gown din data saka ta Dark Orange din Lace tayi bala'in yi mata kyau ta fito da duk wani tudu da komadar jikinta daya qara cika dam kamar zata fashe, saurin dauke kansa yayi sanda ta iso ta karbi Man daya diba ta shiga shafa masa a banyansa, daga shi har itan ba zasu misalta yanda sukeji ba, Ta gaka shafa masa a bayan ya juyo tana fuskantarsa, hannu biyu ta saka taja shafa masa man A fuskarsa da tasa gyara saboda jiya yayi Aski cikin muryarta da tayi rauni kamar zatayi Kuka tace
"Nayi maka abinci, kuma naji kana cewa a kawo maka"
"Oh, thanks" ya fada yana miqewa saboda ya tabbata idan ta sake bude baki tayi magana cutarsa kawia zatayi. Wardrobe ya bude ya dauko Jallabiyya da boxer ya saka ya sake dawoa inda take tsaye ya dauki turare ya fesa kafin ya juya ya dauki Bibi data bingire da bacci ya fice daga dakin.
A kan Dan gadonta da ya gani a gefen kijera ya kwantar da ita tareda pecking goshinta. Kai tsaye kan Dining din ya wuce ya kalli wasu Luxury warmer data zuzuzuba abincin a ciki su kadai kyan su ya isa ya saka ka cin abinda yake ciki ko bakayi niyya ba. Zama yayi ya bude babbar ciki, Tuwon shinkafa ne fari so a ciki, ya waiwaya ya kalli Umaimah data biyo bayansa kamar mara gaskiya, da yar mutunchi suke tashi zeyi ya dagata yayi juyi da ita dan kamar ta shiga zuciyarsa, abinda yake muradi kenan yaci har mafarki yake ya samu tuwo dan tunda ya tafi ko a ido be ganshi ba, zuwan da yayi kwanaki ma zaman hotel ya qare harya tafi be ci ba.
Qaramin murmushi ya sakar mata, Umaimah ta sauke ajiyar zuciya har yana ganin yanda maqogaronta yayi sama da qasa kafin ta taho kamar wahainiya ta shiga bude masa sauran warmers din. Miya kala biyu tayi masa, Miyar Egusi dataji duk wani kalar Wasali da ake sakawa miya ga hadaddiyar Kuka wadda tayi digiri a London tasha zabi da suka dagargaje saboda yanda ta bata lokaci ta dafu.
Dayan kwanon Jellop din shinkafa ce itama dai se wanda ya gani ga wani Musulmin peppe meat tsabar qyallin da yake kamar zaka ga fuskarka a jiki. Se casserole data zuba hadin potatoe Salad dayan kuma ganyan lattece yasha garnishing se wani bowl me kyau data zuba Samosa da spring roll ga kuma Jug din Coconut drink dana Zobo se Jarkokin ruwa me sanyi har diga yakeyi
Duk yanda yaso ya daure seda ya kama hannunta na dama ya sumbata, qarshen abincin sa kenan ta hada masa su, ga Tuwo ga shinkafa ga nama.ga kayan fulawa. Kadan ta zuba masa kowanne a plate yayi bismilla ya shiga ci yana kallon fuskarta data marairaice kamar marainiyar Mage, tuwo ya gutsira ya nufi bakinta dashi, Allah sarki yanda take abu se yaji kamar zata bashi tausayi amma ya kanne haka suka shiga cin abincin yana ci yana bata har suka gama ba tareda wani yace qala ba.
Ita ta kwashe kayan ta kai kitchen ta dawo ta goge gurin harda fesa freshner, a ransa yace
"Ikon Allah, su Umaimah course din tsafta aka yo kenan yana kallo ta ta shige daki babu dadewa ta fito ta zauna akan kujerar gefensa.
"Na same ku lafiya?" Ya fada yana chanza channel, da sauri ta amsa masa ya daga kai ya kalleta, yanda take muimui da baki alamar tana son yin magana se juya yatsunta take kamar me jin tsoron yayi bala'in sake kunna shi.
"Kaak...kayi haquri dan Allah" ta fada dakyar hawaye na kawowa idonta, banza ya mata yaci gaba da chanza channel din da yakeyi
"Dan Allah Khalil ka yafe mun, wallahi sharrin shaidan ne bazan sake ba" ta sake fada cikin muryar kuka"
juyowa yayi ya kalleta, a cikin idonta ya karanci laushin da tayi na gaske ne ya kuma tabbatar da wannan ladabin bana qarya bane da gaske takeyi amma dukda haka baze saki da sauri ba, haka nan baze fasa qudurinsa akanta ba.