Sashe 197
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wata dariya Umaimah tayi tana girgiza kai tace
"Toh inaga ba Mama kadai ta rikice ba harda ke Anty Laure shiyasa she na ganku wani iri kamar an muku mutuwa to gaskiya ya kamata ku nemi magani tunda wuri kar abin ya zarce haka. Idan ba rashin lafiya ba taya ma tunaninku ze fara baku wai Khalil yayi aure kuma ace ban sani ba? Ai wlh ko na mutu ina cikin kabari na tabbata idan Khalil zeyi aure se yaje kan kabarina ya fada mun saboda kar na tashi na ringa yi musu fatalwa ballantana ace da raina ina zaune cikin gidan nan yaje yayi aure hhhhhh" ta sake yin wata dariya duk se suka saki baki suna kallonta Anty Laure tace
"Eh lallai babu shakka Umaimah kai tsaye kice hauka mukeyi kawai meye wani sakayawa kice bamu da lafiya? Toh karma ki kidina kanki a banza kiyi kamar baki san me muke fada ba, Khalil dai yayi aure bakuma yanda kika iya" bata tsaya qarasa jin abinda Anty Lauren take fada ba ta shige dakinta da sauri ta kullo qofar dan karma su bita cikin. Wayarta ta dauka bayan data zauna gefen gado ko kusa taqi ta bawa kwakwalwarta damar daukar abinda suka fada ballan tana har tayi tunani akai.
Kwanciyarta tayi kusada Mu'ayyad tana jin ana buga qofar dakin tayi banza dasu har suka gaji suka bari daga wajen tana jiyo Anty Laure na qunduma mata zagi ko a jikinta sema ta rufe ido babu dadewa kuwa bacci ya kwasheta bata farka ba se bayan Azahar shima dalilin bugun qofarta da ake tayi babu qaqqautawa.
MAMA
Da ido tabi Umaimah harta shige daki ta bugo musu qofa. Anty Laure ta kwashi salati tana tafa hannu tace
"Yaya kina kallon abinda yar iskar yarinyar nan tayi mana? Mu ta kira da mahaukata sannan ta shige daki ta barmu a zaune kamar wasu gantalallu to dan kanta kuma ni wlh yanzu naji dadin kishiyar da akayi mata yar banza me baqin hali da bamu san a inda ta gado ba"
"Laure ni duk ba wannan ya dameni ba, yarinyar nan fa bata yarda da abunda muke fada ba. Ina tsoron abinda ze biyo baya idan ta farga"
"Toh ba ita ta sani ba Yaya ina cewa tayi bamu da lafiya ita da take lafiyayyar ai shikenan idan taji ana ta matsa za'a shigo da Amarya ai a sannan zata sha jinin jikinta wawiyar yarinya da babu abinda ta sani se hauka da rashin hankali nidai tafiya zanyi idan zaki tafi muje idan kuma se kin zauna kin fahimtar da ita Allah ya bamu Alkhairi ni nayi nan" Anty Laure ta fada tana figar jakarta zata fita se Mama ta miqe a sanyaye itama tabi bayanta.
Gidan Maman suka wuce a can suka tarar da Maman Asad tun kafin ma ta tambayi ba'asi akan ganin yanayin Maman Anty Laure ta kwaza mata zance, Anty na tsakar gida tana aikace aikace da yake cikin daga murya Anty Laure take maganar dan haka taji komai a kidime ta saki tsintsiyar hannunta ta dafe qirji babu shiri ta afka dakin. Maman Asad kuwa sunan zaune tayi, seda ta kwashi wasu mintoci kafin ta iya bude baki tace
"Tashin hankali da ba'a saka masa rana toh yanzu Anty Laure ya zamuyi?"
"Ya zamuyi Hajiyayye ko ya zatayi? Meye namu a ciki ya wuce mu koma gefe musha kallo ba cewa tayi bamu da lafiya ba se mu jira muga yanda tata rashin lafiyar zata bayyana aure dai an rigada an daura"
"Amma tsakani da Allah babu Adalci a cikin wannan abun, yama za'ayi ace Khalil yayi aure ba tareda Umaimah ta sani ba kawai saboda ya jazawa mutane da wanda yaji da wanda beji ba duk jidalinta ya shafe su gaskiya ba'a kyauta ba" Anty ta fada kamar zatayi kuka, ita dai Mama tayi shiru tana jinsu kawai kafin ta nisa ta kalli Maman Asad tace
"Hajiyayye ki kira Nuratu da Hafsa qila ku fimu dabarar da zaku fahimtar da ita ta gane bana son azo ana tashin hankali daga baya gara yanzu duk abinda zatayi ta gama kafin tarewar Amaryar. Bari na shiga ciki na kwanta kaina yana mun ciwo".
Ita dai Maman Asad ta rasa abin cewa se Anty Laure keta bala'i Anty Saratu kuma ta rafka tagumi tana wasiqar jaki. Hasashen abinda ze faru daga sanda Umaimah ta fahimci dagaske Khalil yayi aure.
UMAIMAH
Bacci tasha da gaske dan bata farka ba se kusan qarfe uku na rana dalilin buga mata qofa da akayi. Seda ta wanko fuskarta da bakinta tukunna ta bude qofar jin me bugun har sannan be haqura ba. Fuska a hade ta bude qofar tayi tozali da Lubna, rabonda su hadu ido da ido tun haihuwar Mu'ayyad da sukazo suna.
Wani kallon banza suka aikawa junansu Umaimah ta harde hannu a qirji tana qarewa Lubna Kallo kamar yanda itama take kallonta kafin Lubnan taja tsaki cike da mugun kishin da yake nuqurqusarta na rasa Khalil a karo na biyu tace
"An fito da kaya za'a tafi kaiwa nace be kamata ace uwar gida bata gani ba dan haka ki fito ki saka albarka amma se kin daure fa dan nasan lokacinki baki samu kamarsu ba"
Gajeran murmushi Umaiman tayi kafin ta turo qofar tana cewa
"Kece baquwar saka sutura da har Lefe zeyi intimidating naki, koda yake ba'a taba kawo miki ba shiyasa" tana gama fadar haka ta maido qofarta ta rufe, Lubna ta ciji yatsa cikeda takaici ta daga murya tace
"A banza dai wlh kuma ki shirya duk wano Alqadarinko Allah ya kawo mi karyashi sati i war haka kin zama bora a gidan nan kina ji kina gani Khalil ze ringa ririta yar babynsa sedai bakin ciki ya qumeki kiyi bunga".
Haka suka kwashi Akwatunan suka fita dasu daga gidan ba tareda Umaimah tasan me akeyi bama, da Magriba Bibi take mata surutun biki za'ayi taga Akwati da yawa kuma an ce na Dady ne ko kusa bata maida hankali na, bama wannan ba hatta da zuwan Mama ma ta manta da anyi seda Ruqayya take tambayarta me zata ci, ta gaya mata akwai abincin data hadawa su Hajiya dazu kuma suka tafi basuci ba se a sannan ma ta tuna da zuwan nasu da abinda Maman ta gaya mata.
"Uhm Mama da Mafarkanta mara sa kan gado wanna karon kumai kaina suka fada" ta fada qasa qasa tana taunar Chewing gum.
Kiran wayar Safina ya shigo mata, suka gaisa Safina na tambayarta yaya dazun kuwa ta saka
"To wama ya sani ne na dai saka ban sani ba ko Mama ta gani dan jin muryarta kawai akaina, zan dai sake turara ragowar gobe inma sun shaqa su qara" Umaimah ta fada se Safina ta kwashe da dariyar shaqiyanci tana cewa
"Ke matar nan gara dai ki jira ki gani karki qara guma musu su susuce gaba daya"
"To meya ruwana ciki in ma zaucewa zasuyi su ta shafa gonata suka shiga kuma dole na hukuntasu ko dan su kiyaye faruwar hakan a gaba. Ke ni ba wannan bama kinsan wai Mama zuwan da tayi wai gaya mun takeyi Khalil yayi aure ko zeyi aurene ma ni ban gane kan abin ba"
"Halan Mama nada hawan jini ko kin san idan yayi yawa yana saka mutum ya ringa tunanin abubuwa ba daidai ba, se su ringa tunanin abu suna gani kamar a gaske ya faru Illusion ake kiran abun ko to inaga shi Mama takeyi" Safina ta fada cike da shaqiyanci se Umaimah tace
"Kema kya fada, ni gudun kar abun ya bata mun rai ma daki na shige na barsu"
"Ke kuma ya haka gaskiya baki kyauta ba Maman zaki tashi ki bari a zaune tana miki magana matsala ta dake Qawata kanki akwai ruwa wani lokaci ai duk iskanci a dagawa Mama qafa dai" Safina ta fada se Umaimah ta yanutsa fuska tace
"Ai tashin nawa yafi zaman Alkhairi saboda kalar zancen data zo dashi badan ita bace bama da sena zagi uwar wanda ya fada wlh kafin in gurje masa baki"
"Toh Allah yayi mana tsari da mugun ji da mugun gani, yanzu dai ki turamun da ragowar kudadena dana ranta akayi miki aiki tunda dai aiki yaci ina da buqatar kudi gobe ma Qaraye zanje Sailuba ta hadani da wani sabon Teacher kinsan fa shi aikin Suleiman idan ba rubdugu akayi masa ba baci yake ba dan Uwarsa a tsaye take akansa imata in gaya miki sau da yawa ma da nata aikin nake basaja na cusa nawa idan ta kawo Masa Rubutu dasu hayaqi sena canza na ajiye masa nawa yayi tayi to yanzu ta dena bashi sedai kullum yaje gidanta yayi koma menene shiyasa nake so ayi mun kwaf daya kawai, farraqu nake so ayi masa da uwar ta yanda ko inda take baze ringa zuwa ba balle ta ringa lalata mun aiki"
"Toh Allah ya tsare ni kam bazan iya aikin shuka dusa ba" Umaimah ta fada mata cikin izgili se Safina tace
"Na nawa kuma ai kin shuka sedai kiyita aikin ban ruwa kuma qaryar banza da wofi kawai" Safina ta fada a hasale Umaimah na shirin bata amsa Khalil ya turo qofar da sallama qasa qasa kamar wanda akayi qara a Kotun qoli ganinsa yasa Umaimah ta fasa fadar abinda tayi niyya tace mata
"Zan kiraki anjima" daga nan ta kashe wayar tana kallon Khalil daya qwamo wani baqin Glass cikin dare kamar sabon Makaho ya kuna kasa daga kai ya kalli inda take.
"Toh inaga ba Mama kadai ta rikice ba harda ke Anty Laure shiyasa she na ganku wani iri kamar an muku mutuwa to gaskiya ya kamata ku nemi magani tunda wuri kar abin ya zarce haka. Idan ba rashin lafiya ba taya ma tunaninku ze fara baku wai Khalil yayi aure kuma ace ban sani ba? Ai wlh ko na mutu ina cikin kabari na tabbata idan Khalil zeyi aure se yaje kan kabarina ya fada mun saboda kar na tashi na ringa yi musu fatalwa ballantana ace da raina ina zaune cikin gidan nan yaje yayi aure hhhhhh" ta sake yin wata dariya duk se suka saki baki suna kallonta Anty Laure tace
"Eh lallai babu shakka Umaimah kai tsaye kice hauka mukeyi kawai meye wani sakayawa kice bamu da lafiya? Toh karma ki kidina kanki a banza kiyi kamar baki san me muke fada ba, Khalil dai yayi aure bakuma yanda kika iya" bata tsaya qarasa jin abinda Anty Lauren take fada ba ta shige dakinta da sauri ta kullo qofar dan karma su bita cikin. Wayarta ta dauka bayan data zauna gefen gado ko kusa taqi ta bawa kwakwalwarta damar daukar abinda suka fada ballan tana har tayi tunani akai.
Kwanciyarta tayi kusada Mu'ayyad tana jin ana buga qofar dakin tayi banza dasu har suka gaji suka bari daga wajen tana jiyo Anty Laure na qunduma mata zagi ko a jikinta sema ta rufe ido babu dadewa kuwa bacci ya kwasheta bata farka ba se bayan Azahar shima dalilin bugun qofarta da ake tayi babu qaqqautawa.
MAMA
Da ido tabi Umaimah harta shige daki ta bugo musu qofa. Anty Laure ta kwashi salati tana tafa hannu tace
"Yaya kina kallon abinda yar iskar yarinyar nan tayi mana? Mu ta kira da mahaukata sannan ta shige daki ta barmu a zaune kamar wasu gantalallu to dan kanta kuma ni wlh yanzu naji dadin kishiyar da akayi mata yar banza me baqin hali da bamu san a inda ta gado ba"
"Laure ni duk ba wannan ya dameni ba, yarinyar nan fa bata yarda da abunda muke fada ba. Ina tsoron abinda ze biyo baya idan ta farga"
"Toh ba ita ta sani ba Yaya ina cewa tayi bamu da lafiya ita da take lafiyayyar ai shikenan idan taji ana ta matsa za'a shigo da Amarya ai a sannan zata sha jinin jikinta wawiyar yarinya da babu abinda ta sani se hauka da rashin hankali nidai tafiya zanyi idan zaki tafi muje idan kuma se kin zauna kin fahimtar da ita Allah ya bamu Alkhairi ni nayi nan" Anty Laure ta fada tana figar jakarta zata fita se Mama ta miqe a sanyaye itama tabi bayanta.
Gidan Maman suka wuce a can suka tarar da Maman Asad tun kafin ma ta tambayi ba'asi akan ganin yanayin Maman Anty Laure ta kwaza mata zance, Anty na tsakar gida tana aikace aikace da yake cikin daga murya Anty Laure take maganar dan haka taji komai a kidime ta saki tsintsiyar hannunta ta dafe qirji babu shiri ta afka dakin. Maman Asad kuwa sunan zaune tayi, seda ta kwashi wasu mintoci kafin ta iya bude baki tace
"Tashin hankali da ba'a saka masa rana toh yanzu Anty Laure ya zamuyi?"
"Ya zamuyi Hajiyayye ko ya zatayi? Meye namu a ciki ya wuce mu koma gefe musha kallo ba cewa tayi bamu da lafiya ba se mu jira muga yanda tata rashin lafiyar zata bayyana aure dai an rigada an daura"
"Amma tsakani da Allah babu Adalci a cikin wannan abun, yama za'ayi ace Khalil yayi aure ba tareda Umaimah ta sani ba kawai saboda ya jazawa mutane da wanda yaji da wanda beji ba duk jidalinta ya shafe su gaskiya ba'a kyauta ba" Anty ta fada kamar zatayi kuka, ita dai Mama tayi shiru tana jinsu kawai kafin ta nisa ta kalli Maman Asad tace
"Hajiyayye ki kira Nuratu da Hafsa qila ku fimu dabarar da zaku fahimtar da ita ta gane bana son azo ana tashin hankali daga baya gara yanzu duk abinda zatayi ta gama kafin tarewar Amaryar. Bari na shiga ciki na kwanta kaina yana mun ciwo".
Ita dai Maman Asad ta rasa abin cewa se Anty Laure keta bala'i Anty Saratu kuma ta rafka tagumi tana wasiqar jaki. Hasashen abinda ze faru daga sanda Umaimah ta fahimci dagaske Khalil yayi aure.
UMAIMAH
Bacci tasha da gaske dan bata farka ba se kusan qarfe uku na rana dalilin buga mata qofa da akayi. Seda ta wanko fuskarta da bakinta tukunna ta bude qofar jin me bugun har sannan be haqura ba. Fuska a hade ta bude qofar tayi tozali da Lubna, rabonda su hadu ido da ido tun haihuwar Mu'ayyad da sukazo suna.
Wani kallon banza suka aikawa junansu Umaimah ta harde hannu a qirji tana qarewa Lubna Kallo kamar yanda itama take kallonta kafin Lubnan taja tsaki cike da mugun kishin da yake nuqurqusarta na rasa Khalil a karo na biyu tace
"An fito da kaya za'a tafi kaiwa nace be kamata ace uwar gida bata gani ba dan haka ki fito ki saka albarka amma se kin daure fa dan nasan lokacinki baki samu kamarsu ba"
Gajeran murmushi Umaiman tayi kafin ta turo qofar tana cewa
"Kece baquwar saka sutura da har Lefe zeyi intimidating naki, koda yake ba'a taba kawo miki ba shiyasa" tana gama fadar haka ta maido qofarta ta rufe, Lubna ta ciji yatsa cikeda takaici ta daga murya tace
"A banza dai wlh kuma ki shirya duk wano Alqadarinko Allah ya kawo mi karyashi sati i war haka kin zama bora a gidan nan kina ji kina gani Khalil ze ringa ririta yar babynsa sedai bakin ciki ya qumeki kiyi bunga".
Haka suka kwashi Akwatunan suka fita dasu daga gidan ba tareda Umaimah tasan me akeyi bama, da Magriba Bibi take mata surutun biki za'ayi taga Akwati da yawa kuma an ce na Dady ne ko kusa bata maida hankali na, bama wannan ba hatta da zuwan Mama ma ta manta da anyi seda Ruqayya take tambayarta me zata ci, ta gaya mata akwai abincin data hadawa su Hajiya dazu kuma suka tafi basuci ba se a sannan ma ta tuna da zuwan nasu da abinda Maman ta gaya mata.
"Uhm Mama da Mafarkanta mara sa kan gado wanna karon kumai kaina suka fada" ta fada qasa qasa tana taunar Chewing gum.
Kiran wayar Safina ya shigo mata, suka gaisa Safina na tambayarta yaya dazun kuwa ta saka
"To wama ya sani ne na dai saka ban sani ba ko Mama ta gani dan jin muryarta kawai akaina, zan dai sake turara ragowar gobe inma sun shaqa su qara" Umaimah ta fada se Safina ta kwashe da dariyar shaqiyanci tana cewa
"Ke matar nan gara dai ki jira ki gani karki qara guma musu su susuce gaba daya"
"To meya ruwana ciki in ma zaucewa zasuyi su ta shafa gonata suka shiga kuma dole na hukuntasu ko dan su kiyaye faruwar hakan a gaba. Ke ni ba wannan bama kinsan wai Mama zuwan da tayi wai gaya mun takeyi Khalil yayi aure ko zeyi aurene ma ni ban gane kan abin ba"
"Halan Mama nada hawan jini ko kin san idan yayi yawa yana saka mutum ya ringa tunanin abubuwa ba daidai ba, se su ringa tunanin abu suna gani kamar a gaske ya faru Illusion ake kiran abun ko to inaga shi Mama takeyi" Safina ta fada cike da shaqiyanci se Umaimah tace
"Kema kya fada, ni gudun kar abun ya bata mun rai ma daki na shige na barsu"
"Ke kuma ya haka gaskiya baki kyauta ba Maman zaki tashi ki bari a zaune tana miki magana matsala ta dake Qawata kanki akwai ruwa wani lokaci ai duk iskanci a dagawa Mama qafa dai" Safina ta fada se Umaimah ta yanutsa fuska tace
"Ai tashin nawa yafi zaman Alkhairi saboda kalar zancen data zo dashi badan ita bace bama da sena zagi uwar wanda ya fada wlh kafin in gurje masa baki"
"Toh Allah yayi mana tsari da mugun ji da mugun gani, yanzu dai ki turamun da ragowar kudadena dana ranta akayi miki aiki tunda dai aiki yaci ina da buqatar kudi gobe ma Qaraye zanje Sailuba ta hadani da wani sabon Teacher kinsan fa shi aikin Suleiman idan ba rubdugu akayi masa ba baci yake ba dan Uwarsa a tsaye take akansa imata in gaya miki sau da yawa ma da nata aikin nake basaja na cusa nawa idan ta kawo Masa Rubutu dasu hayaqi sena canza na ajiye masa nawa yayi tayi to yanzu ta dena bashi sedai kullum yaje gidanta yayi koma menene shiyasa nake so ayi mun kwaf daya kawai, farraqu nake so ayi masa da uwar ta yanda ko inda take baze ringa zuwa ba balle ta ringa lalata mun aiki"
"Toh Allah ya tsare ni kam bazan iya aikin shuka dusa ba" Umaimah ta fada mata cikin izgili se Safina tace
"Na nawa kuma ai kin shuka sedai kiyita aikin ban ruwa kuma qaryar banza da wofi kawai" Safina ta fada a hasale Umaimah na shirin bata amsa Khalil ya turo qofar da sallama qasa qasa kamar wanda akayi qara a Kotun qoli ganinsa yasa Umaimah ta fasa fadar abinda tayi niyya tace mata
"Zan kiraki anjima" daga nan ta kashe wayar tana kallon Khalil daya qwamo wani baqin Glass cikin dare kamar sabon Makaho ya kuna kasa daga kai ya kalli inda take.