Sashe 149
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin ladabi yayi musu sannu da zuwa, suka gaisa da Nasir kafin yaja motarsa ya tafi yana jimanta abinda Khalil din ya gaya masa Umaimah tayi. Yanzun ma yana kallon yanda taja hijabi ta rufe fuskarta ruf kallonta yake mamakinta na kashe shi gaba daya ji yake kamar shine silar janyowa Khalil din wannan tashin hankali, da beje gurinsa ba ranar da beganta ba. Qila da yanzu ya auri wata matar yana cikin kwanciyar hankali da nutsuwa.
A falon Hajiya rasa inda zata ajiye su tayi murnar dawowar Umaiman da kunyar Iyayenta duk suka dabaibayeta. Anty Amina, Jamila da Jalila da suka tarar a zaune suka gaishe su kafin gaba daya suka miqe dan su basu guri. Dakin Habiba suka shiga, Jalilah ta tabe baki tace
"Ai dole su maidota dan na tabbatar su kansu zaman ta addabarsu zeyi haba yarinya kamar jikar shaidan"
"Kedai Jalila kin fiya daukar dumi, tunda Mijinta yace ta dawo ai dole ta dawo nasan baze wuce sunzo su qara bada haquri bane kawai amma duk mugun halin da ai iyayensa bazasu gujeshi ba" cewar Jamila se Jalilan ta sake cewa
"Banda dai me irin halin matar Khalil, kana zaune ta jefaka a masifar da za'a kulleka a kurkuku haba ai wallahi Khalil dai beyi sa'ar aure ba kwata kwata kuma wallahi bari a nutsa, ko bokan kan dutse ne yake mata tsafi qarewar bin malamai se mun karya alqadarinta Khalil yayi aure dan bazan zuba ido ina kallo ta kashe mun dan uwa a tsaye ba haba".
"Rigimar gidan Khalil dai in kika shiga ke zakiji kunya, kuma ma keda yar dakin taki ina ta kinfi kowa shigar mata idan anje gidan tawa mutane iskanci kice tsokanarta sukayi?
Qiri qiri ta daki Lubnan Kaduna amma keda Hajiya kuka daure mata qugu wai rashin kunya tayi mata ni wallahi tun sannan nasan bata da mutunchi in ba haba daga zuwan baquwa dangin Mijinki ki kamata da duka ai kome ta miki kya jira Mijin yazo ya dauki mataki amma gata isashshiya to ai yanzu da abin yazo kan kowa kwa kiyayeta" Anty Amina ta fada.
A can Falon Hajiya kuwa bayan sun gaisa Abba ya shiga bawa Khalil harda Hajiyar haquri akan abinda ya faru, Hajiya ta tare shi da cewa
"Haba Alhaji, ai mune ya kamata mu bada haquri dan mu mukayi laifi. Ai dukiya bata fi lafiya ba kuma shima na nasa fada sosai akan abinda yayi be kyauta ba duk neman da yakeyi dan su wa yakeyi? Badan dai itan da Yayanta bane kuma dan an rasa wani abu shikeban se yace zeyi fushi da hukuncin Allah bayan ba laifinta bane?
Abu in rabonka ne kana kwance ze same ka in kuwa ba nakan bane ko ka saka a baki se kayi amansa balle kuma abinda tun farko a ka qullo shi ta sigar yaudara Allah nema ya kama shi yaga nufinsa nason cutar da yarinyar mutane ya hana qulluwar abun".
"Maganar gaskiya Hajiya abinda tayi ko kusa da daidai beje ba kuma mutum me cikakken hankali baze ringa tunani irin na Umaimah ba. Sannan Hajiya irin wannan goyon bayan da take samu a gurinki shiyake sakawa take raina Mijinta take masa duk iskancin data ga dama dan tasan zaki tsaya mata wanda ba daidai bane. Ni na haifi Umaimah nafi kowa sanin halinta zuma ce ita seda wuta ake cinta dan haka na roqeki Hajiya da ki dubi Allah ki ringa tsawatar mata idan tayi ba daidai ba. Idan ba zaki iya ba ki bar Khalil ya dauki matakin daya dace akanta ki dena dakatar dashi.
Hajiya Alkhairin Umaimah kawai kika sani na yarda kuma kina Qaunarta dalilin daya sa kike kasa hango duk tarin laifin da aka ce ta aikata amma a Yanzu Khalil Shi yake zaune da ita, koni bazan gaya masa Umaimah ba a yanzu tunda ta fita daga hannunmu shi yake tareda ita. Duk wasu mugayen dabi'u da take koya a gurin qawayen banzan da take mu'amala dasu ya sani dan haka idan yace ta masa abu ki yarda ki kuma kirata ki tsawatar mata saboda kin fimu kusa da ita a yanzu" Mama ta fada se Hajiya tayi shiru gaba daya jikinta yayi sanyi.
Gani takeyi kamar Maman tana nuna cewar cutar Umaimah take ta hanyar qin nuna mata gaskiya tabi bayanta a koda yaushe wanda ita tsakaninta da Allah har a yanzu rashin kyautawar ta data gani bata kai irin yanda suke zuzuta abin ba. Tana yi mata uzuri saboda ta kasance itama a lokacin da take ganiyar quruciya kamar ta Macece me tsananin kishi sedai ko kwatan abinda Umaiman takeyi bata aikata ba dan ita nata kishin baya ko barinta ta kula Mijin ballantana wadda yake tareda ita. Lokacin Babansu Khalil din ya auri Mahaifiyar Jamila wanda auran gaba daya sun yarda qaddara ce da rabon samun Jamilar harta rayu shekara daya tareda Mijinta ta rasu a yayin haihuwar Jamilan magana bata taba hadata da ita ba, haka shima Babansu Khalil din, daga randa Fatiman ta tare ta raba shimfida dashi seda suka kwashe tsayin shekara biyu har bayan rasuwarta kafin ta iya danne zuciyarta ta karbeshi a matsayin Miji shiyasa ko kadan bata ganin laifin Umaimah dan tasan menene kishi, ta san zafinsa da abinda ze iya ingizaka ka aikata idan har bakayi takatsantsan ba.
Har suka tafi jikin Hajiya a sanyaye yake, seda ta rakasu ta dawo kafin ta kalli Umaimah da tunda suka shigo ta rabe a jikin kujera bata motsa ba. Maganganun da Abba da Maman sukayi mata a hanya ne suketa nuqurqusarta, nasiha ce me ratsa jini da jijiya sukayi mata a hanya har suka iso gidan. Idan da ace kunnenta najin magana ne daga lokacin ko kallon banza ba zata sake iya daga ido tayiwa wani ba albarkacin roqon da iyayenta sukayi mata na ta tausaya musu ta zauna lafiya a gidan auranta.
Kusada ita Hajiya ta zauna tareda dafata Umaimah ta dago fuskarta data canza kamannin saboda marin Baba Abdullahi idonta ya kawo kwalla Hajiya tace
"Subhanallahi, wa yayi miki wannan aiki haka?"
Seta saki hawayen suka fara zuba, cikin tausayi Hajiya tace
"Ki dena kuka kinji komai ya wuce yanzu tunda dai gashi kin dawo. Dan Allah ki koyi haquri Umaimah duk abinda ya faru tsakaninku kizo nan ki gaya mun kar ki dauki hukunci a hannunki dan kinga dai har iyayenki sun fara ganin ni nake goya miki baya kina abinda kika ga dama ina ga sauran mutanen gari?
Yanzu ki tashi maza kije dakinki kiyi wanka ki huta babu komai in Allah ya yarda".
"Toh Hajiya Amma Khalil be haqura ba, kinga fa ko kallona beyi ba tsoro nakeji kar na koma ya sake yi mun wani abun ni dai zan zauna anan har zuwa sanda ze sakko daga fushin Hajiya" Umaiman ta fada tana kuka. Hajiya tayi murmushi kafin ta kalli bangaren da Khalil ke zaune bayan ya dawo daga rakiyar su Abban tace
"Ki rabu dashi babu abinda zeyi miki ko kallon banza ya sake yi miki a cikin gidan nan sena saba masa balle yace ze taba lafiyarki. Maza share hawayenki ki kuma cire damuwar komai daga ranki kodan saboda halin da kike ciki, ni se naga cikin ma ya rage girma gaba daya ma kin rame da alama bakya cin abinci, bari na kawo miki Tuwo maza kici kiyi wanka cikinsu Jamila wata ta raka ki Asibiti su sake dubaki dan bazan ma hadaki dashi balle kuje ya ringa miki muzurai".
Yanda kasan gunki haka yayi musu bema nuna alamar yaji abinda Hajiyar take fada ba balle ya tanka. Laptop din dake kan cinyarsa kawai yake dannanwa amma tunaninsa yana kan abinda Abban Umaimah ya gaya masa yanzu.
"Idan ka gaji da halinta babu me takura maka Khalil ka sawwaqe mata ni na haifi Umaimah idan kuma da ace kaine a matsayin Dana tabbas bazan goyi bayan kaci gaba da zama da kafaffiyar mace mara jin magana irinta ba. Ka bawa zuciyarka damar yin tunani in har kaga da cutuwa a zamanku ka sawwaqe mata kawai kowa ya huta" nazarin maganar yakeyi tausayin dattijon yana sake shigarsa. Sukam dai tasu jarabawar kenan kuma ze cigaba da haquri da ita saboda su zataci albarkacin su da kuma na Yaran dake tsakaninsa da ita amma wallahi da ace be haihu da Umaimah ba a wannan gabar da tuni ya sallameta dan be tabajin ta fitar masa a rai duk wani abu nata yayi masa baqi ba se a wannan karon, ya kuma tabbatar babu wani abu da zata sakeyi da ze wanke ta a idonsa ya dena tuna abinda tayi masa.
Jin Hajiya zata dame shi ma dan se magana take tana sako sunansa a ciki ya saka ya tattara ya bar gidan gaba daya, su Jalila ma dai datayi musu zancen daya daga ciki ta raka Umaimah Asibitin gaba daya zamewa sukayi kowacce tace tana da uzuri suka yi tafiyarsu gaba daya. Qarshe se ita da kanta ta rakata bayan tayi wanka sabon Driver da Khalil ya daukarwa Hajiyan saboda Khalifa ya koma makaranta ya kaisu. Likita ya dubata ya tabbatar musu da komai lafiya cikin kuma daman tun wancan karon ya sanar musu da yuwuwar ya qara lokaci akan lokacin daya kamata ta haihun a farko saboda jinin data zubar ze iya sakawa ya koma baya ga rashin nutsuwar da take ciki zata iya affecting cigaban girman jaririn dan haka dole seta haqura da duk ma abinda yake sakata damuwar kodan lafiyarta data abin cikinta. Ya rubuta mata yan magubgunan da zasu taimaka mata yace taje taci gaba dasha daga nan suka kama hanya tsabar daurewa qarya Ass Hajiyan harda saka Driver ya kaisu gurin da ake siyar da kayan maqulashe ta siyowa Umaiman da sam bakinta babu appetite. Tunanin yanda zata kwashe da Khalil kadai ya saka jininta yana neman hawa, idan ya kuma maimaita mata irin waccen shaqar ta tabbatar kafin azo ceto ta margaya ta yuwu ma ajaline yasa su Maman suka dawo da ita gidan ganin qarshe ta musu toh Allah ya jiqanta kawai.
A falon Hajiya rasa inda zata ajiye su tayi murnar dawowar Umaiman da kunyar Iyayenta duk suka dabaibayeta. Anty Amina, Jamila da Jalila da suka tarar a zaune suka gaishe su kafin gaba daya suka miqe dan su basu guri. Dakin Habiba suka shiga, Jalilah ta tabe baki tace
"Ai dole su maidota dan na tabbatar su kansu zaman ta addabarsu zeyi haba yarinya kamar jikar shaidan"
"Kedai Jalila kin fiya daukar dumi, tunda Mijinta yace ta dawo ai dole ta dawo nasan baze wuce sunzo su qara bada haquri bane kawai amma duk mugun halin da ai iyayensa bazasu gujeshi ba" cewar Jamila se Jalilan ta sake cewa
"Banda dai me irin halin matar Khalil, kana zaune ta jefaka a masifar da za'a kulleka a kurkuku haba ai wallahi Khalil dai beyi sa'ar aure ba kwata kwata kuma wallahi bari a nutsa, ko bokan kan dutse ne yake mata tsafi qarewar bin malamai se mun karya alqadarinta Khalil yayi aure dan bazan zuba ido ina kallo ta kashe mun dan uwa a tsaye ba haba".
"Rigimar gidan Khalil dai in kika shiga ke zakiji kunya, kuma ma keda yar dakin taki ina ta kinfi kowa shigar mata idan anje gidan tawa mutane iskanci kice tsokanarta sukayi?
Qiri qiri ta daki Lubnan Kaduna amma keda Hajiya kuka daure mata qugu wai rashin kunya tayi mata ni wallahi tun sannan nasan bata da mutunchi in ba haba daga zuwan baquwa dangin Mijinki ki kamata da duka ai kome ta miki kya jira Mijin yazo ya dauki mataki amma gata isashshiya to ai yanzu da abin yazo kan kowa kwa kiyayeta" Anty Amina ta fada.
A can Falon Hajiya kuwa bayan sun gaisa Abba ya shiga bawa Khalil harda Hajiyar haquri akan abinda ya faru, Hajiya ta tare shi da cewa
"Haba Alhaji, ai mune ya kamata mu bada haquri dan mu mukayi laifi. Ai dukiya bata fi lafiya ba kuma shima na nasa fada sosai akan abinda yayi be kyauta ba duk neman da yakeyi dan su wa yakeyi? Badan dai itan da Yayanta bane kuma dan an rasa wani abu shikeban se yace zeyi fushi da hukuncin Allah bayan ba laifinta bane?
Abu in rabonka ne kana kwance ze same ka in kuwa ba nakan bane ko ka saka a baki se kayi amansa balle kuma abinda tun farko a ka qullo shi ta sigar yaudara Allah nema ya kama shi yaga nufinsa nason cutar da yarinyar mutane ya hana qulluwar abun".
"Maganar gaskiya Hajiya abinda tayi ko kusa da daidai beje ba kuma mutum me cikakken hankali baze ringa tunani irin na Umaimah ba. Sannan Hajiya irin wannan goyon bayan da take samu a gurinki shiyake sakawa take raina Mijinta take masa duk iskancin data ga dama dan tasan zaki tsaya mata wanda ba daidai bane. Ni na haifi Umaimah nafi kowa sanin halinta zuma ce ita seda wuta ake cinta dan haka na roqeki Hajiya da ki dubi Allah ki ringa tsawatar mata idan tayi ba daidai ba. Idan ba zaki iya ba ki bar Khalil ya dauki matakin daya dace akanta ki dena dakatar dashi.
Hajiya Alkhairin Umaimah kawai kika sani na yarda kuma kina Qaunarta dalilin daya sa kike kasa hango duk tarin laifin da aka ce ta aikata amma a Yanzu Khalil Shi yake zaune da ita, koni bazan gaya masa Umaimah ba a yanzu tunda ta fita daga hannunmu shi yake tareda ita. Duk wasu mugayen dabi'u da take koya a gurin qawayen banzan da take mu'amala dasu ya sani dan haka idan yace ta masa abu ki yarda ki kuma kirata ki tsawatar mata saboda kin fimu kusa da ita a yanzu" Mama ta fada se Hajiya tayi shiru gaba daya jikinta yayi sanyi.
Gani takeyi kamar Maman tana nuna cewar cutar Umaimah take ta hanyar qin nuna mata gaskiya tabi bayanta a koda yaushe wanda ita tsakaninta da Allah har a yanzu rashin kyautawar ta data gani bata kai irin yanda suke zuzuta abin ba. Tana yi mata uzuri saboda ta kasance itama a lokacin da take ganiyar quruciya kamar ta Macece me tsananin kishi sedai ko kwatan abinda Umaiman takeyi bata aikata ba dan ita nata kishin baya ko barinta ta kula Mijin ballantana wadda yake tareda ita. Lokacin Babansu Khalil din ya auri Mahaifiyar Jamila wanda auran gaba daya sun yarda qaddara ce da rabon samun Jamilar harta rayu shekara daya tareda Mijinta ta rasu a yayin haihuwar Jamilan magana bata taba hadata da ita ba, haka shima Babansu Khalil din, daga randa Fatiman ta tare ta raba shimfida dashi seda suka kwashe tsayin shekara biyu har bayan rasuwarta kafin ta iya danne zuciyarta ta karbeshi a matsayin Miji shiyasa ko kadan bata ganin laifin Umaimah dan tasan menene kishi, ta san zafinsa da abinda ze iya ingizaka ka aikata idan har bakayi takatsantsan ba.
Har suka tafi jikin Hajiya a sanyaye yake, seda ta rakasu ta dawo kafin ta kalli Umaimah da tunda suka shigo ta rabe a jikin kujera bata motsa ba. Maganganun da Abba da Maman sukayi mata a hanya ne suketa nuqurqusarta, nasiha ce me ratsa jini da jijiya sukayi mata a hanya har suka iso gidan. Idan da ace kunnenta najin magana ne daga lokacin ko kallon banza ba zata sake iya daga ido tayiwa wani ba albarkacin roqon da iyayenta sukayi mata na ta tausaya musu ta zauna lafiya a gidan auranta.
Kusada ita Hajiya ta zauna tareda dafata Umaimah ta dago fuskarta data canza kamannin saboda marin Baba Abdullahi idonta ya kawo kwalla Hajiya tace
"Subhanallahi, wa yayi miki wannan aiki haka?"
Seta saki hawayen suka fara zuba, cikin tausayi Hajiya tace
"Ki dena kuka kinji komai ya wuce yanzu tunda dai gashi kin dawo. Dan Allah ki koyi haquri Umaimah duk abinda ya faru tsakaninku kizo nan ki gaya mun kar ki dauki hukunci a hannunki dan kinga dai har iyayenki sun fara ganin ni nake goya miki baya kina abinda kika ga dama ina ga sauran mutanen gari?
Yanzu ki tashi maza kije dakinki kiyi wanka ki huta babu komai in Allah ya yarda".
"Toh Hajiya Amma Khalil be haqura ba, kinga fa ko kallona beyi ba tsoro nakeji kar na koma ya sake yi mun wani abun ni dai zan zauna anan har zuwa sanda ze sakko daga fushin Hajiya" Umaiman ta fada tana kuka. Hajiya tayi murmushi kafin ta kalli bangaren da Khalil ke zaune bayan ya dawo daga rakiyar su Abban tace
"Ki rabu dashi babu abinda zeyi miki ko kallon banza ya sake yi miki a cikin gidan nan sena saba masa balle yace ze taba lafiyarki. Maza share hawayenki ki kuma cire damuwar komai daga ranki kodan saboda halin da kike ciki, ni se naga cikin ma ya rage girma gaba daya ma kin rame da alama bakya cin abinci, bari na kawo miki Tuwo maza kici kiyi wanka cikinsu Jamila wata ta raka ki Asibiti su sake dubaki dan bazan ma hadaki dashi balle kuje ya ringa miki muzurai".
Yanda kasan gunki haka yayi musu bema nuna alamar yaji abinda Hajiyar take fada ba balle ya tanka. Laptop din dake kan cinyarsa kawai yake dannanwa amma tunaninsa yana kan abinda Abban Umaimah ya gaya masa yanzu.
"Idan ka gaji da halinta babu me takura maka Khalil ka sawwaqe mata ni na haifi Umaimah idan kuma da ace kaine a matsayin Dana tabbas bazan goyi bayan kaci gaba da zama da kafaffiyar mace mara jin magana irinta ba. Ka bawa zuciyarka damar yin tunani in har kaga da cutuwa a zamanku ka sawwaqe mata kawai kowa ya huta" nazarin maganar yakeyi tausayin dattijon yana sake shigarsa. Sukam dai tasu jarabawar kenan kuma ze cigaba da haquri da ita saboda su zataci albarkacin su da kuma na Yaran dake tsakaninsa da ita amma wallahi da ace be haihu da Umaimah ba a wannan gabar da tuni ya sallameta dan be tabajin ta fitar masa a rai duk wani abu nata yayi masa baqi ba se a wannan karon, ya kuma tabbatar babu wani abu da zata sakeyi da ze wanke ta a idonsa ya dena tuna abinda tayi masa.
Jin Hajiya zata dame shi ma dan se magana take tana sako sunansa a ciki ya saka ya tattara ya bar gidan gaba daya, su Jalila ma dai datayi musu zancen daya daga ciki ta raka Umaimah Asibitin gaba daya zamewa sukayi kowacce tace tana da uzuri suka yi tafiyarsu gaba daya. Qarshe se ita da kanta ta rakata bayan tayi wanka sabon Driver da Khalil ya daukarwa Hajiyan saboda Khalifa ya koma makaranta ya kaisu. Likita ya dubata ya tabbatar musu da komai lafiya cikin kuma daman tun wancan karon ya sanar musu da yuwuwar ya qara lokaci akan lokacin daya kamata ta haihun a farko saboda jinin data zubar ze iya sakawa ya koma baya ga rashin nutsuwar da take ciki zata iya affecting cigaban girman jaririn dan haka dole seta haqura da duk ma abinda yake sakata damuwar kodan lafiyarta data abin cikinta. Ya rubuta mata yan magubgunan da zasu taimaka mata yace taje taci gaba dasha daga nan suka kama hanya tsabar daurewa qarya Ass Hajiyan harda saka Driver ya kaisu gurin da ake siyar da kayan maqulashe ta siyowa Umaiman da sam bakinta babu appetite. Tunanin yanda zata kwashe da Khalil kadai ya saka jininta yana neman hawa, idan ya kuma maimaita mata irin waccen shaqar ta tabbatar kafin azo ceto ta margaya ta yuwu ma ajaline yasa su Maman suka dawo da ita gidan ganin qarshe ta musu toh Allah ya jiqanta kawai.