Sashe 196
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kaga tashi kaje dakinku ka kwanta kaga nan ma hira mukeyi karmu dameka" ta fada ganin yana shirin yin bacci se Safina tayi saurin tareta tace
"Ki barshi mana mu se mu koma falo ai na gama bude kayan duk da ba zama zanyi bama gara inje in aikata abinda ya kamata" ta fada tana miqewa tsaye. Falon suka koma, suna zama tayi qasa da murya tana kallon Umaimah tace
"Kinga ga dama kin samu duk suna gidan dangi na kusa dana nesa yanzu ki tashi kiyi turaren nan kowa ta shaqa shikenan fa kin gama dasu tsakaninki da dangin Khalil se yanda kikace haka za'ayi"
"Kuma fa hakane, bari to ina tashi" Umaimah tayi na'am da zancen babu bata lokaci ta shiga kitchen ta kunna coal ta saka a kasko ta fito falon, seda ta dakko maganin ta kwance zata zuba Safina tayi saurin tareta tana cewa
"Ke uwar hankali waya ce miki haka zakiyi? Ai se kin je can kin ajiye kaskon a inda kika san idan kin zuba duk zasu shaqi hayaqin sannan ki zuba ki bar gurin. Ki samu kamar bayan windown falon ki saka a can zefi samunsu kuma ki tabbata babu wanda yaga sanda kika zuba maganin haka qa'idar aikin take".
Harararta Umaimah tayi kafin ta dauki kaskon ta fita, harta zagaya ta bayan falon babu wanda ta hadu dashi, tana jiyo hayaniya da shewarsu daga ciki dukda bata tantance abinda suke cewa ta tabe baki a ranta tana tunanin ko taron uban me sukeyi haka se Allah. Seda ta samu guri me kyau ta ajiye kaskonta ta kwance qullin ta debi turaren bayan ta dauke numfashi ta zuba, murmushi ta saki ganin yanda iska take kadawa ta bangaren da haqin yake bi kai tsaye tana sake ingizashi zuwa cikin falon
"Me kikeyi haka Umaimah" taji Muryar Mama kamar a mafarki a bayanta.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 70
"Meye wannan kika zuba?" Maman ta sake fada tana matsawa kusa da ita Umaimah ta saki ragowar qullin hannu ta a qasa saboda kidima cikin rawar baki tace
"Mammma yaushe kika zo ya kika biyo ta nan?"
"Ba wannan na tambayeki ba me kika zuba a cikin kaskon nan nace?" Maman ta sake fada tana qarasawa kusa da ita ta kalli kaskon dake bulbula uban hayaqi mara dadi ta kalli Umaimah da alamun rashin gaskiya suka gama bayyana a jikinta cikin in ina tace
"Am Mama maganin Miyagu ne aka bani"
"Kuma maganin se akace kibi gida gaba daya ki saka musu kuma a boye?" Maman ta sake tambayarta tana tsareta da ido se Umaimaha ta zumbura baki tana kallon gefe tace
"Toh ai Mama haka me maganin yace Mayun na gida ne kuma idan suka sani ba zasu bari na saka ba dan kwanaki ma da aka bani daukewa sukayi na neme shi na rasa"
"Dauki kaskon muje" Maman ta sake fada tana girgiza kai Mamakin Umaiman yana kamata dan ta yarda da gaske maganin Miyagun ne mamakinta kawai yanda tace wai Mayun na gida ne kenan Mijinta ma Mayen ne da Yayanta tunda dai a Barayin uwarsa take kunna maganin itace mayyar kenan.
Umaimah kuwa babu yanda ta iya haka ta dauki kasko gudun kar Maman ta zargi wani abu, addu'arta daya Allah yasa bataga sanda ta zuba maganin ba inda bata gani ba toh ai magana ta qare hayaqin ya shiga kuma ko yaya ne ya gauraya da iskar gidan duk sun shaqa.
A bakin qofa suka ci karo da Safina da uwar jakarta ta rungumo,ta gaida Mama data bita da kallo tana cewa Umaimah zasuyi waya, suka shiga ciki tana gaba Maman na binta a baya. Anty Laure na zaune kan kujera tana girgiza qafa kana ganinta kasan bala'i nacinta Umaimah dai ta wuce Kitchen ta juye garwashin a sink ta kashe kafin ta koma falon gabanta na faduwa wannan zuwan na Mama babu sanarwa tasan ba Alkhairi bane, qila wani sharrin aka qullo mata shine maman ta taddota har gida kenan zata ci mata mutunchi.
A qasa ta zauna ta gaishe su, Anty alaure bata amsa ba Mama dai ta amsa a sanyaye tana kallon Umaiman tunanin yanda zata isar mata da wannan saqo me nauyi take yi. Ruqayya ta fito daga kitchen da Babban Try ta doro Ruwa da Lemo ta ajiye ta gaida Mama cikin girmamawa ta sake komawa ta dakko Babban Bowl data zubo dambun nama, jiya Khalil ya shiga dashi ko Umaiman ma ta manta bata gayawa na se yanzu ta tuna dashi. Seda ta ajiye musu duk wani kalar kayan dadi da suke dashi a gidan kafin ta koka kitchen ta shiga shirin dora abincin rana na Alfarma duk saboda zuwan Hajiya Mama.
Duk kayan da Ruqayya ta ajiye musu babu abinda suka taba, Mama ta kalli Umaimah da duk ta fita a kamanninta tace
"Umaimah haka ciki ya mayar dake? Yaushe ne lokacin haihuwar taki wai?"
"Nima ban sani ba Mama amma sunce na kusa" ta bata amsa ba tareda ta kalleta ba se Mama ta sauke ajiyar zuciya kafin ta sake cewa
"Khalil yana gidan ne?"
"Ya fita tun safe amma nasan qila yana hanyar dawowa saboda yau be cika fita bama indai ba da wani babban dalili ba"
"Toh yayi Allah ya dawo dashi lafiya" Maman ta sake fada se sukayi shiru gaba daya kusan minti biyar Umaimah ta kalli Anty Laure tace
"Anty ya Babanmu ina ta cewa zanzo gashi kin rigani zuwa"
"Kiyi ta kanki yarinya ahto kiji da abinda yake a gabanki ba gulma" Anty Laure ta fada, shirun suka sakeyi, gaba daya Umaimah ta tsargu da yanayin Mama. Da ace laifi tayi fada zata fara mata amma yanda ta ganta a sanyaye gashi se kallon ta takeyi yasa hankalinta ya fara tashi, kodai wani abu ne ya faru a gida? Amma idan haka ne ai ba Mama ce zatazo da kanta ba wani za'a turo to ko qararta Khalil yakai shi kuma me tayi masa kai babu ma wata qara da ze kai da can ma baya kai qararta gida balle yanzu da ya sake zamar mata Mijin tace qila dai wani abun ne na daban ya kawo Maman. Maganar Mama ce ta katse mata tunani jin tana cewa
Cike da qarfin Hali Mama tace
"Ni kam ya maganar qarin auran Mijin ko?"
Tamkar saukar aradu haka taji maganar, seta muskuta tana kallon Maman tace
"Toh ya gaya miki kenan, to ni ina ruwana na hanashi yayi aurene da zeje ya hadani dake? Yayi auransa mana ai ba akaina matar zata zauna ba".
Yanda tayi maganar seka rantse da Allah har ranta kamar yanda ta fada abin be dameta ba, cike da samun kwarin guiwa Mama tace
"Haka ne kam ba akanki zata zauna ba kuma na godewa Allah da kika fahimci hakan in har da gaske kikeyi kenan" Mama ta fada seta gyara zama sosai kafin ta kira sunan Umaiman cikin muryar dake nuna muhimmancin maganar da take so tayi mata.
"A matsayinki na Musulma kinsan cewar Imaninki baze cika ba har se kin yarda da Qaddara me kyau ko Mara kyau haka ne ko ba haka ba?"
A hankali Umaimah ta bude baki tace
"Hakane Mama"
"Toh ina so ki bude kunnenki da kyau ki saurari abinda zan gaya miki sannan ina so kiyiwa maganata kyakykyawar fahimta" Maman ta sake fada Umaimah dai kallonta kawai takeyi tana jin gabanta yana faduwa. A hankali kuma cikin hikima Mama ta fara mata Nasiha irin wadda duk taurin zuciyar mutum seta raunana tayi laushi, seda ta tabbatar da jikin Umaiman yayi sanyi qalau ta yanda ko motsi ta gagarayi daga zaunen da take kafin ta sake gyara zama tana dauke idonta daga kallonta. Cikin nutsuwa ta warware mata zare da abawar abinda yake faruwa ta rufe da cewa
"Kiyita maimaita Hasbunallahu wani'imal wakeel har se kin samu gamsashshiyar nutsuwa, karki yarda ki bawa Shaidan damar shiga zuciyarki yayi wasa, ubangiji ne yayi hukuncinsa kar kice zakiyi fito na fito da umarnin ubangiji Umaimah kiyi addu'a Allah yasa hakan ya zamo muku Alkhairi baki daya, Mijinki yana sonki na tabbatar kuma babu abinda ze canza hakan daga zuciyarsa. Haqurin da zakiyi da juriya su zasu qara girmama soyayyarki da martabarki a zuciyarsa".
Shiru falon ya dauka kamar babu abu me rai a ciki kafin Umaimah da tayi mutuwar zaune ta ja numfashinta daya bar jikinta na wani lokaci, babu yabo babu fallasa ta kalli Maman tace
"Toh Mama nagode da Nasiha ina kuma addu'ar kar Allah ya tabbatar da wannan mafarkin naki"
"Mafarki Umaimah, duk maganganun da na gama yi miki a mafarki kika daukesu?" Mama ta fada cikin mamaki se Umaimah ta miqe tsaye tana kallon Maman tace
"To idan ba mafarki bane Mama tatsuniya ce ko kuma makuwar tunani kima samu da har kikayi irin wannan hasashen?"
A hasale Anty Laure tace mata "Ke shagga idan zaki hada hankalinki guri daya tun wuri kiyi ki fuskanci abinda yake a gabanki, munafunci ne an rigada anyi ruwanki ki maida musu da aniyarsu ruwanki kiyi hauka su samu yanda suke so suyita yawo dake a duniya suna yadaki zabi ya rage naki yanzu ita dai Kishiya kafin ta shigo ne kake yin barazana ko hakan ze sa a fasa idan kuma ta rigada ta shigo sedai kayi yaqin tsira da mutunchi dan ko kin koreta a banza ta rigada ta kafa tarihi ko magana aka tashi se an jinginaki da ita ace tsohuwar Kishiyarki to gara ki rungumi qaddararki kawai ki zauna lafiya ki kuma bawa munafukai kunya dan gasu can sun cika gida suna jiran suga yanda zakiyi".
"Ki barshi mana mu se mu koma falo ai na gama bude kayan duk da ba zama zanyi bama gara inje in aikata abinda ya kamata" ta fada tana miqewa tsaye. Falon suka koma, suna zama tayi qasa da murya tana kallon Umaimah tace
"Kinga ga dama kin samu duk suna gidan dangi na kusa dana nesa yanzu ki tashi kiyi turaren nan kowa ta shaqa shikenan fa kin gama dasu tsakaninki da dangin Khalil se yanda kikace haka za'ayi"
"Kuma fa hakane, bari to ina tashi" Umaimah tayi na'am da zancen babu bata lokaci ta shiga kitchen ta kunna coal ta saka a kasko ta fito falon, seda ta dakko maganin ta kwance zata zuba Safina tayi saurin tareta tana cewa
"Ke uwar hankali waya ce miki haka zakiyi? Ai se kin je can kin ajiye kaskon a inda kika san idan kin zuba duk zasu shaqi hayaqin sannan ki zuba ki bar gurin. Ki samu kamar bayan windown falon ki saka a can zefi samunsu kuma ki tabbata babu wanda yaga sanda kika zuba maganin haka qa'idar aikin take".
Harararta Umaimah tayi kafin ta dauki kaskon ta fita, harta zagaya ta bayan falon babu wanda ta hadu dashi, tana jiyo hayaniya da shewarsu daga ciki dukda bata tantance abinda suke cewa ta tabe baki a ranta tana tunanin ko taron uban me sukeyi haka se Allah. Seda ta samu guri me kyau ta ajiye kaskonta ta kwance qullin ta debi turaren bayan ta dauke numfashi ta zuba, murmushi ta saki ganin yanda iska take kadawa ta bangaren da haqin yake bi kai tsaye tana sake ingizashi zuwa cikin falon
"Me kikeyi haka Umaimah" taji Muryar Mama kamar a mafarki a bayanta.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 70
"Meye wannan kika zuba?" Maman ta sake fada tana matsawa kusa da ita Umaimah ta saki ragowar qullin hannu ta a qasa saboda kidima cikin rawar baki tace
"Mammma yaushe kika zo ya kika biyo ta nan?"
"Ba wannan na tambayeki ba me kika zuba a cikin kaskon nan nace?" Maman ta sake fada tana qarasawa kusa da ita ta kalli kaskon dake bulbula uban hayaqi mara dadi ta kalli Umaimah da alamun rashin gaskiya suka gama bayyana a jikinta cikin in ina tace
"Am Mama maganin Miyagu ne aka bani"
"Kuma maganin se akace kibi gida gaba daya ki saka musu kuma a boye?" Maman ta sake tambayarta tana tsareta da ido se Umaimaha ta zumbura baki tana kallon gefe tace
"Toh ai Mama haka me maganin yace Mayun na gida ne kuma idan suka sani ba zasu bari na saka ba dan kwanaki ma da aka bani daukewa sukayi na neme shi na rasa"
"Dauki kaskon muje" Maman ta sake fada tana girgiza kai Mamakin Umaiman yana kamata dan ta yarda da gaske maganin Miyagun ne mamakinta kawai yanda tace wai Mayun na gida ne kenan Mijinta ma Mayen ne da Yayanta tunda dai a Barayin uwarsa take kunna maganin itace mayyar kenan.
Umaimah kuwa babu yanda ta iya haka ta dauki kasko gudun kar Maman ta zargi wani abu, addu'arta daya Allah yasa bataga sanda ta zuba maganin ba inda bata gani ba toh ai magana ta qare hayaqin ya shiga kuma ko yaya ne ya gauraya da iskar gidan duk sun shaqa.
A bakin qofa suka ci karo da Safina da uwar jakarta ta rungumo,ta gaida Mama data bita da kallo tana cewa Umaimah zasuyi waya, suka shiga ciki tana gaba Maman na binta a baya. Anty Laure na zaune kan kujera tana girgiza qafa kana ganinta kasan bala'i nacinta Umaimah dai ta wuce Kitchen ta juye garwashin a sink ta kashe kafin ta koma falon gabanta na faduwa wannan zuwan na Mama babu sanarwa tasan ba Alkhairi bane, qila wani sharrin aka qullo mata shine maman ta taddota har gida kenan zata ci mata mutunchi.
A qasa ta zauna ta gaishe su, Anty alaure bata amsa ba Mama dai ta amsa a sanyaye tana kallon Umaiman tunanin yanda zata isar mata da wannan saqo me nauyi take yi. Ruqayya ta fito daga kitchen da Babban Try ta doro Ruwa da Lemo ta ajiye ta gaida Mama cikin girmamawa ta sake komawa ta dakko Babban Bowl data zubo dambun nama, jiya Khalil ya shiga dashi ko Umaiman ma ta manta bata gayawa na se yanzu ta tuna dashi. Seda ta ajiye musu duk wani kalar kayan dadi da suke dashi a gidan kafin ta koka kitchen ta shiga shirin dora abincin rana na Alfarma duk saboda zuwan Hajiya Mama.
Duk kayan da Ruqayya ta ajiye musu babu abinda suka taba, Mama ta kalli Umaimah da duk ta fita a kamanninta tace
"Umaimah haka ciki ya mayar dake? Yaushe ne lokacin haihuwar taki wai?"
"Nima ban sani ba Mama amma sunce na kusa" ta bata amsa ba tareda ta kalleta ba se Mama ta sauke ajiyar zuciya kafin ta sake cewa
"Khalil yana gidan ne?"
"Ya fita tun safe amma nasan qila yana hanyar dawowa saboda yau be cika fita bama indai ba da wani babban dalili ba"
"Toh yayi Allah ya dawo dashi lafiya" Maman ta sake fada se sukayi shiru gaba daya kusan minti biyar Umaimah ta kalli Anty Laure tace
"Anty ya Babanmu ina ta cewa zanzo gashi kin rigani zuwa"
"Kiyi ta kanki yarinya ahto kiji da abinda yake a gabanki ba gulma" Anty Laure ta fada, shirun suka sakeyi, gaba daya Umaimah ta tsargu da yanayin Mama. Da ace laifi tayi fada zata fara mata amma yanda ta ganta a sanyaye gashi se kallon ta takeyi yasa hankalinta ya fara tashi, kodai wani abu ne ya faru a gida? Amma idan haka ne ai ba Mama ce zatazo da kanta ba wani za'a turo to ko qararta Khalil yakai shi kuma me tayi masa kai babu ma wata qara da ze kai da can ma baya kai qararta gida balle yanzu da ya sake zamar mata Mijin tace qila dai wani abun ne na daban ya kawo Maman. Maganar Mama ce ta katse mata tunani jin tana cewa
Cike da qarfin Hali Mama tace
"Ni kam ya maganar qarin auran Mijin ko?"
Tamkar saukar aradu haka taji maganar, seta muskuta tana kallon Maman tace
"Toh ya gaya miki kenan, to ni ina ruwana na hanashi yayi aurene da zeje ya hadani dake? Yayi auransa mana ai ba akaina matar zata zauna ba".
Yanda tayi maganar seka rantse da Allah har ranta kamar yanda ta fada abin be dameta ba, cike da samun kwarin guiwa Mama tace
"Haka ne kam ba akanki zata zauna ba kuma na godewa Allah da kika fahimci hakan in har da gaske kikeyi kenan" Mama ta fada seta gyara zama sosai kafin ta kira sunan Umaiman cikin muryar dake nuna muhimmancin maganar da take so tayi mata.
"A matsayinki na Musulma kinsan cewar Imaninki baze cika ba har se kin yarda da Qaddara me kyau ko Mara kyau haka ne ko ba haka ba?"
A hankali Umaimah ta bude baki tace
"Hakane Mama"
"Toh ina so ki bude kunnenki da kyau ki saurari abinda zan gaya miki sannan ina so kiyiwa maganata kyakykyawar fahimta" Maman ta sake fada Umaimah dai kallonta kawai takeyi tana jin gabanta yana faduwa. A hankali kuma cikin hikima Mama ta fara mata Nasiha irin wadda duk taurin zuciyar mutum seta raunana tayi laushi, seda ta tabbatar da jikin Umaiman yayi sanyi qalau ta yanda ko motsi ta gagarayi daga zaunen da take kafin ta sake gyara zama tana dauke idonta daga kallonta. Cikin nutsuwa ta warware mata zare da abawar abinda yake faruwa ta rufe da cewa
"Kiyita maimaita Hasbunallahu wani'imal wakeel har se kin samu gamsashshiyar nutsuwa, karki yarda ki bawa Shaidan damar shiga zuciyarki yayi wasa, ubangiji ne yayi hukuncinsa kar kice zakiyi fito na fito da umarnin ubangiji Umaimah kiyi addu'a Allah yasa hakan ya zamo muku Alkhairi baki daya, Mijinki yana sonki na tabbatar kuma babu abinda ze canza hakan daga zuciyarsa. Haqurin da zakiyi da juriya su zasu qara girmama soyayyarki da martabarki a zuciyarsa".
Shiru falon ya dauka kamar babu abu me rai a ciki kafin Umaimah da tayi mutuwar zaune ta ja numfashinta daya bar jikinta na wani lokaci, babu yabo babu fallasa ta kalli Maman tace
"Toh Mama nagode da Nasiha ina kuma addu'ar kar Allah ya tabbatar da wannan mafarkin naki"
"Mafarki Umaimah, duk maganganun da na gama yi miki a mafarki kika daukesu?" Mama ta fada cikin mamaki se Umaimah ta miqe tsaye tana kallon Maman tace
"To idan ba mafarki bane Mama tatsuniya ce ko kuma makuwar tunani kima samu da har kikayi irin wannan hasashen?"
A hasale Anty Laure tace mata "Ke shagga idan zaki hada hankalinki guri daya tun wuri kiyi ki fuskanci abinda yake a gabanki, munafunci ne an rigada anyi ruwanki ki maida musu da aniyarsu ruwanki kiyi hauka su samu yanda suke so suyita yawo dake a duniya suna yadaki zabi ya rage naki yanzu ita dai Kishiya kafin ta shigo ne kake yin barazana ko hakan ze sa a fasa idan kuma ta rigada ta shigo sedai kayi yaqin tsira da mutunchi dan ko kin koreta a banza ta rigada ta kafa tarihi ko magana aka tashi se an jinginaki da ita ace tsohuwar Kishiyarki to gara ki rungumi qaddararki kawai ki zauna lafiya ki kuma bawa munafukai kunya dan gasu can sun cika gida suna jiran suga yanda zakiyi".