Sashe 220
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk budurin da akayi Mama na zaune a falonta ko gezau batayi, ba qaramin dadin abinda Abban yayi taji ba dan ita kanta ta kusa tashi taje ta kwada mata mari seya fansheta yayiwa Umaiman dukan cire raini. Tana ganin wuce warsa ta tashi tabi bayansa da ruwa me sanyin gaske harda Zobo ta dora a Try ta kai masa dan tasan yanada buqatar abinda ze sanyaya masa zuciya yanzu.
Da kanta ta tsiyaya masa bayan tayi masa sannu da zuwa, be iya amsawa da baki ba se hannu ya daga mata ta miqa masa Cup cike da ruwa tana cewa
"Karbi kasha Alhaji akan me zaka bata ranka a banza akan wadda bata san ciwon kanta ba, Umaimah cefa haukarta ce ta tashi saboda Khalil yazo tareda matarsa ta ganshi cikin nutsuwarsa ba kamar yanda tayi fatan jefa rayuwarsa a cikin garari ba, ai daman duk wanda yace tukunyar wani ba zata tafasa ba tasa ko dumi ba zatayi ba".
Tasya shanye ruwanta sake qara masa yasha sannanya shiga sauke ajiyar zuciya a jere a jere tsahon lokaci kafinya bude baki yace
"Ina tsoron fushin zuciya ya saka na furtawa Yarinyar nan kalmar da ba zata zama Alkhairi a gareta ba". Cikin kulawa Maman tace
"Ka ci gaba da haquri Alhaji, shiyasa kaga nake nesanta kaina daga duk shirginta, banga abinda takeyi ballantana raina ya baci a banza tunda ita bata san daidai, kullum addu'ata Allah ya duba mata yasa ta gane abinda takeyi ba daidai bane tun tana da sauran damar gyarawa".
Jigum sukayi suna zaune aka kawo Nepa cikin dashewar murya yace ta kunna masa heater bandaki, ta shiga ta kunna tana fitowa Anty ta shigo da qaton Flask din ruwan zafi da ka ganta kasan a rikice take. Ita ta shiga ta hada masa ruwan kafin ta fito Maman ta koma dakinta Abba ya shiga wanka ita kuma ta koma kan aikinta tanayi har sannan zuciyarta bata bar tsinkewa ba. Ita dai wannan jaraba ta Umaimah daga tayi sauqi se wata ta bullo tana Addu'a Allah ya fito mata da Miji nan kusa ta daga su samu sa'ida dan idan taci gaba da zama itama seta dora mata hawan Jinin data sakawa uwarta da ubanta sunyi Anko, ina dalili wai gashi ita kamar Afi bata iya dauke kai taga abu ya samu Umaimar, sonta takeyi tsakani da Allah gashi babu abinda son yake tsinana mata se wahala.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 77
UMAIMAH
Daren Ranar bata iya bacci ba seda Anty ta kira wani me Chemist ya dubata yayi mata allurar rage zugi tasha magani sannan, washe gari da safe ta tashi da wani sabon tashin hankalin. Qarfe goma gaba daya yan gidan manya da yara suka hallara bisa umarnin kiran da Abban yayi musu tun daren jiya. Bata san kiran me ya musu ba tadai ga sun shige can bangarensa kuma sun dade suna magana dan har se gurin sha biyu sannan Salman yazo yayi kiranta.
Dakyar take tafiya saboda yanda jikinta yayi tsami, badan kar ta sake yin wani laifin ba daman da bazataje kiran ba. Irin yanda gaba daya suka dauke kai tamkar babu wanda yasan da tsiron halittarta a gurin ya mata ciwo daman tunda ta dawo gidan in ka cire Anty babu me shiga sabgarta Mama kuwa in zasu hadu sau dubu ta gaidata bazata amsa ba daman tun randa tadawo tayi mata iyaka da shiga dakinta tace bata buqatar ganinta a ciki. Tana zama kamar wata Mujiya a cikinsu suka fara darewa daya da daya duk suka fice daga dakin kowanne yazo giftata seya bugamata tsaki sannan su harareta, seda suka fice gaba daya kafin Mama ta kalleta rai babu dadi tace
"Matso ciki".
Gaba kadan ta muskuta amma bata yarda tayi kusa dasu da yawa ba cikin rawar Murya ta shiga gaishe su ta kalli Abba dake Kishingide da gani bashida lafiya, babu wanda ya amsa gaisuwar Tata har Antyn yau tana daga gefe idonta yayi jajir alamar Kuka tayi se Umaimah ta sunkuyar da kanta qasa, muryar Abban taji cikin dakiya yana cewa
"Ina so ku zama shaida tsakanina da Umaimah zan kafa mata sharudda da har idan tana neman zaman lafiya a cikin gidan nan dole ta bisu. Ban yarda Umaimah ta taka ko nan da qofar gida ba tareda izinina ba haka zalika banyarda wani yazo gidannan gurinta ba, sannan zata bani wayarta" Abban ya fada yana kallon Umaimah data sunkuyar da kanta qasa tana hawaye, takaicin yanda gaba daya kowa ya tsaneta ya kamata, babu wanda ya dubi halin da ta tsinci kanta a ciki ita ta rasa Khalil a maimakon su tausaya mata suyi qoqarin kwato mata haqqinta se suka bige da tsanarta kamar ta aikata musu wani mugun laifi.
Tana jin Abban ya gama maganarsa, zancen ba zata fita ba ko ba za'a zo gunta ba be dameta ba kamar na karbe mata waya. Idan ya rabata da wayarta ta ina zata samu damar magana da Khalil harsu daidaita ta koma dakinta? Tsawar da Mama ta daka mata ceta sakata miqewa da sauri dan dakko wayar, tana hawaye kamar yarinya ta bashi wayar tata ya karba a gabanta ya zare layin ya ballashi biyu kafin ya sake kallonta yace
"Abu na gaba
daga yau duk wani aiki na cikin gidan nan ya dawo hannunki, ina nufin daga kan shara girki wanke wanke da duk wasu sauran ayyukan tsakar gida ke zaki cigaba da yinsu har wankin kayanku idan kuna da buqata ku bata tayi muku dan ba zan ringa ciyar da ke a banza ba tunda kinqi zaman aure kiyi na Farilla ki samu lada zakiyi Mustahabi anan. Idan har na kamaki da laifin saba daya daga cikin sharuddan nan ina me tabbatar miki da cewar sekin gane kuskurenki tabbas".
Da sauri ta daga kai ta kalli Abban bakinta na rawa alamar son yin magana amma mugun kallon da Mama ta aika mata dashi yasa ta kasa cewa komai ta maida kanta qasa hawaye suka sake balle mata kamar famfo.
"Rayuwar da kika zabarwa kanki kenan zaman gida ba gaki ga gidannan se kici uwar da kika ajiye a ciki. Kinsan dai ba zamu zauna muna goga kafada dake a cikin gidan nan ba mu dafa mu baki kici ki ajiye kwano mu share guri ki zauna na iya lokacin da aka miki ma Allah ya bamu lada dan haka dolenki kiyi aiki in har kina son zaman lafiya damu koda yake ma bata bakina nakeyi saboda na manta da kin rigada kin zama yar kanki kiyi duk yanda yayi miki Umaimah babu wanda zesake tilasta ki akan kiyi daidai amma kin sani matuqar kika qi ji ba zaki qi gani ba kuma kinji abinda Mahaifinki duk ya fada se ki zaba zama lafiya kibi abinda yace ko ki fara neman wani gidan uban da zakije kici gaba da yanda kika ga dama" Mama ta fada cikin fushi ita dai Umaimah kanta na qasa in banda hawaye babu abinda takeyi.
Shiru sukayi na kusan Minti goma babu wanda ya sake cewa komai se Abban ya yunqura ze tashi Mama da Antyn suka miqe a tare suma dan taimaka masa ganin Anty tafi kusa dashi yasa Maman ta tsaya ita kuma ta kamashi suka shige cikin dakin
"Idan baqin cikin ki ya kashe shi se ki zuba ruwa a qasa kisha" Mama ta sake cewa kafin ta juya ta fice daga falon ta barta tana kuka da tunanin ita me tayi kuma da za'ace baqin cikinta ze kashe Abba? Haka taja qafafunta da suka sake yin tsami saboda zama ta fita daga, a bakin qofa sukaci karo da Sharifa zata shiga da Flask qarami a hannunta ta kalli Umaiman tayi tsaki qasa qasa tace
"Wlh mutum ya kashe mana Uba ba yarda zamuyi ba se munyi shari'a dashi" tayi gaba a hasale Umaiman ta fincikota baya tareda watsa mata maridukda ba wai taji abinda ta fada bane saboda ta sauke fushin su da take cike dashi tace
"Dan uwarki ni sa'arkice da zaki mun qunquni?"
Kuka Sharifan ta fasa, Nuratu data taho da Kwanuka tayi saurin direwa a qasa ta fincike hannun Umaiman data shaqe Sharifan tana cewa
"Karki sake gigin taba lafiyar wani daga cikinsu"
"Ke kuma ina ruwanki ai ban saka ki a ciki ba balle ki shiga" ta sake zaburowa Nuratun seta daga mata hannu tace
"Karki kuskura kice zaki zageni dan nima kinsan ba sa'arki bace ba, kuma iskancin da kika sabayi a baya muna daga miki qafa yanzu kinyi kadan wlh duk wanda kika nemi ki taka se ya mayar miki da raddi dan haka ki kama tsumman rayuwarki kija sauran mutunchin daya rage miki, mtsww" taja tsaki ta dauki kwanon data ajiye tayi cikin falon Sharifa ta faki idon Umaimah tayi mata gwalo kafin tabi bayan Nuratu da sauri.
Kamar yar yarinya haka ta wuce dakin Mama tana kuka da hawaye shabe shabe zata shiga ta tuna da Gargadin data mata dan haka ta coge daga bakin qofa cikin kuka ta kalli Maman da suke magana da Anty Hafsa da Maman Asad tace
"Wlh Mama kiyi mun tsakani da Nuratu karta sake shiga shirgina akan me yarinya zata mun rashin kunya na hukuntata sannan tazo ta bada ni a gabanta ta gaya mun magana wlh karta sake idan ba haka ba..."
"Idan ba haka ba me Umaimah?" Mama ta dakatar da ita kafin taci gaba da cewa
"Ke har kina da kunya ma da zakiji haushi dan wani ya miki fitsara? Yanzu maganar da kika zo kina mun a sama kamar yarki ki ai ladabi da Biyayya ne ya jawo haka ko to kici gaba karki fasa"
Da kanta ta tsiyaya masa bayan tayi masa sannu da zuwa, be iya amsawa da baki ba se hannu ya daga mata ta miqa masa Cup cike da ruwa tana cewa
"Karbi kasha Alhaji akan me zaka bata ranka a banza akan wadda bata san ciwon kanta ba, Umaimah cefa haukarta ce ta tashi saboda Khalil yazo tareda matarsa ta ganshi cikin nutsuwarsa ba kamar yanda tayi fatan jefa rayuwarsa a cikin garari ba, ai daman duk wanda yace tukunyar wani ba zata tafasa ba tasa ko dumi ba zatayi ba".
Tasya shanye ruwanta sake qara masa yasha sannanya shiga sauke ajiyar zuciya a jere a jere tsahon lokaci kafinya bude baki yace
"Ina tsoron fushin zuciya ya saka na furtawa Yarinyar nan kalmar da ba zata zama Alkhairi a gareta ba". Cikin kulawa Maman tace
"Ka ci gaba da haquri Alhaji, shiyasa kaga nake nesanta kaina daga duk shirginta, banga abinda takeyi ballantana raina ya baci a banza tunda ita bata san daidai, kullum addu'ata Allah ya duba mata yasa ta gane abinda takeyi ba daidai bane tun tana da sauran damar gyarawa".
Jigum sukayi suna zaune aka kawo Nepa cikin dashewar murya yace ta kunna masa heater bandaki, ta shiga ta kunna tana fitowa Anty ta shigo da qaton Flask din ruwan zafi da ka ganta kasan a rikice take. Ita ta shiga ta hada masa ruwan kafin ta fito Maman ta koma dakinta Abba ya shiga wanka ita kuma ta koma kan aikinta tanayi har sannan zuciyarta bata bar tsinkewa ba. Ita dai wannan jaraba ta Umaimah daga tayi sauqi se wata ta bullo tana Addu'a Allah ya fito mata da Miji nan kusa ta daga su samu sa'ida dan idan taci gaba da zama itama seta dora mata hawan Jinin data sakawa uwarta da ubanta sunyi Anko, ina dalili wai gashi ita kamar Afi bata iya dauke kai taga abu ya samu Umaimar, sonta takeyi tsakani da Allah gashi babu abinda son yake tsinana mata se wahala.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 77
UMAIMAH
Daren Ranar bata iya bacci ba seda Anty ta kira wani me Chemist ya dubata yayi mata allurar rage zugi tasha magani sannan, washe gari da safe ta tashi da wani sabon tashin hankalin. Qarfe goma gaba daya yan gidan manya da yara suka hallara bisa umarnin kiran da Abban yayi musu tun daren jiya. Bata san kiran me ya musu ba tadai ga sun shige can bangarensa kuma sun dade suna magana dan har se gurin sha biyu sannan Salman yazo yayi kiranta.
Dakyar take tafiya saboda yanda jikinta yayi tsami, badan kar ta sake yin wani laifin ba daman da bazataje kiran ba. Irin yanda gaba daya suka dauke kai tamkar babu wanda yasan da tsiron halittarta a gurin ya mata ciwo daman tunda ta dawo gidan in ka cire Anty babu me shiga sabgarta Mama kuwa in zasu hadu sau dubu ta gaidata bazata amsa ba daman tun randa tadawo tayi mata iyaka da shiga dakinta tace bata buqatar ganinta a ciki. Tana zama kamar wata Mujiya a cikinsu suka fara darewa daya da daya duk suka fice daga dakin kowanne yazo giftata seya bugamata tsaki sannan su harareta, seda suka fice gaba daya kafin Mama ta kalleta rai babu dadi tace
"Matso ciki".
Gaba kadan ta muskuta amma bata yarda tayi kusa dasu da yawa ba cikin rawar Murya ta shiga gaishe su ta kalli Abba dake Kishingide da gani bashida lafiya, babu wanda ya amsa gaisuwar Tata har Antyn yau tana daga gefe idonta yayi jajir alamar Kuka tayi se Umaimah ta sunkuyar da kanta qasa, muryar Abban taji cikin dakiya yana cewa
"Ina so ku zama shaida tsakanina da Umaimah zan kafa mata sharudda da har idan tana neman zaman lafiya a cikin gidan nan dole ta bisu. Ban yarda Umaimah ta taka ko nan da qofar gida ba tareda izinina ba haka zalika banyarda wani yazo gidannan gurinta ba, sannan zata bani wayarta" Abban ya fada yana kallon Umaimah data sunkuyar da kanta qasa tana hawaye, takaicin yanda gaba daya kowa ya tsaneta ya kamata, babu wanda ya dubi halin da ta tsinci kanta a ciki ita ta rasa Khalil a maimakon su tausaya mata suyi qoqarin kwato mata haqqinta se suka bige da tsanarta kamar ta aikata musu wani mugun laifi.
Tana jin Abban ya gama maganarsa, zancen ba zata fita ba ko ba za'a zo gunta ba be dameta ba kamar na karbe mata waya. Idan ya rabata da wayarta ta ina zata samu damar magana da Khalil harsu daidaita ta koma dakinta? Tsawar da Mama ta daka mata ceta sakata miqewa da sauri dan dakko wayar, tana hawaye kamar yarinya ta bashi wayar tata ya karba a gabanta ya zare layin ya ballashi biyu kafin ya sake kallonta yace
"Abu na gaba
daga yau duk wani aiki na cikin gidan nan ya dawo hannunki, ina nufin daga kan shara girki wanke wanke da duk wasu sauran ayyukan tsakar gida ke zaki cigaba da yinsu har wankin kayanku idan kuna da buqata ku bata tayi muku dan ba zan ringa ciyar da ke a banza ba tunda kinqi zaman aure kiyi na Farilla ki samu lada zakiyi Mustahabi anan. Idan har na kamaki da laifin saba daya daga cikin sharuddan nan ina me tabbatar miki da cewar sekin gane kuskurenki tabbas".
Da sauri ta daga kai ta kalli Abban bakinta na rawa alamar son yin magana amma mugun kallon da Mama ta aika mata dashi yasa ta kasa cewa komai ta maida kanta qasa hawaye suka sake balle mata kamar famfo.
"Rayuwar da kika zabarwa kanki kenan zaman gida ba gaki ga gidannan se kici uwar da kika ajiye a ciki. Kinsan dai ba zamu zauna muna goga kafada dake a cikin gidan nan ba mu dafa mu baki kici ki ajiye kwano mu share guri ki zauna na iya lokacin da aka miki ma Allah ya bamu lada dan haka dolenki kiyi aiki in har kina son zaman lafiya damu koda yake ma bata bakina nakeyi saboda na manta da kin rigada kin zama yar kanki kiyi duk yanda yayi miki Umaimah babu wanda zesake tilasta ki akan kiyi daidai amma kin sani matuqar kika qi ji ba zaki qi gani ba kuma kinji abinda Mahaifinki duk ya fada se ki zaba zama lafiya kibi abinda yace ko ki fara neman wani gidan uban da zakije kici gaba da yanda kika ga dama" Mama ta fada cikin fushi ita dai Umaimah kanta na qasa in banda hawaye babu abinda takeyi.
Shiru sukayi na kusan Minti goma babu wanda ya sake cewa komai se Abban ya yunqura ze tashi Mama da Antyn suka miqe a tare suma dan taimaka masa ganin Anty tafi kusa dashi yasa Maman ta tsaya ita kuma ta kamashi suka shige cikin dakin
"Idan baqin cikin ki ya kashe shi se ki zuba ruwa a qasa kisha" Mama ta sake cewa kafin ta juya ta fice daga falon ta barta tana kuka da tunanin ita me tayi kuma da za'ace baqin cikinta ze kashe Abba? Haka taja qafafunta da suka sake yin tsami saboda zama ta fita daga, a bakin qofa sukaci karo da Sharifa zata shiga da Flask qarami a hannunta ta kalli Umaiman tayi tsaki qasa qasa tace
"Wlh mutum ya kashe mana Uba ba yarda zamuyi ba se munyi shari'a dashi" tayi gaba a hasale Umaiman ta fincikota baya tareda watsa mata maridukda ba wai taji abinda ta fada bane saboda ta sauke fushin su da take cike dashi tace
"Dan uwarki ni sa'arkice da zaki mun qunquni?"
Kuka Sharifan ta fasa, Nuratu data taho da Kwanuka tayi saurin direwa a qasa ta fincike hannun Umaiman data shaqe Sharifan tana cewa
"Karki sake gigin taba lafiyar wani daga cikinsu"
"Ke kuma ina ruwanki ai ban saka ki a ciki ba balle ki shiga" ta sake zaburowa Nuratun seta daga mata hannu tace
"Karki kuskura kice zaki zageni dan nima kinsan ba sa'arki bace ba, kuma iskancin da kika sabayi a baya muna daga miki qafa yanzu kinyi kadan wlh duk wanda kika nemi ki taka se ya mayar miki da raddi dan haka ki kama tsumman rayuwarki kija sauran mutunchin daya rage miki, mtsww" taja tsaki ta dauki kwanon data ajiye tayi cikin falon Sharifa ta faki idon Umaimah tayi mata gwalo kafin tabi bayan Nuratu da sauri.
Kamar yar yarinya haka ta wuce dakin Mama tana kuka da hawaye shabe shabe zata shiga ta tuna da Gargadin data mata dan haka ta coge daga bakin qofa cikin kuka ta kalli Maman da suke magana da Anty Hafsa da Maman Asad tace
"Wlh Mama kiyi mun tsakani da Nuratu karta sake shiga shirgina akan me yarinya zata mun rashin kunya na hukuntata sannan tazo ta bada ni a gabanta ta gaya mun magana wlh karta sake idan ba haka ba..."
"Idan ba haka ba me Umaimah?" Mama ta dakatar da ita kafin taci gaba da cewa
"Ke har kina da kunya ma da zakiji haushi dan wani ya miki fitsara? Yanzu maganar da kika zo kina mun a sama kamar yarki ki ai ladabi da Biyayya ne ya jawo haka ko to kici gaba karki fasa"