Sashe 181
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har Allah Allah ya ringayi lokacin tashi yayi ya tafi gurinya, yanayin sallar La'asar kuwa ya fita, seda ya tsaya yayiwa yaran Unaizatu tsarabar chocolate itama ya siya mata kalar wanda ya saba kai mata kafin ya kama hanya. Har cikin falo tayi masa iso wanda aka gyara tsaf ko ina se qamshi yakeyi, yaranta biyar duk suka shiga suka gaidashi ya basu tsarabar daya tafi da ita kafin Unaizan ta shiga itama. Har qasa ta tsugunna ta gaidashi ya amsa mata cikin kulawa a ransa yana mamakin yanda ta zama wata big madam kamar ba Unaiza Lilo sunan da suke tsokanarta dashi lokacin suna yara, ita take bin Mansur dan haka basa shiri a sanann Khalil ne abokinta komai da Yah Khalil ake qullashi danshi Mansur ya fiya tsokana shine ma ya saka mata sunan Lilon kuma har a makaranta haka yake kiranta kuma ya bita tayita kuka harta haqura take amsawa.
"Ikon Allah Unaiza, ashe zakiyi qiba" Khalil daya kasa shiru ya fada se ta fashe da dariya ita kanta abin mamaki yake bata tace
"Wlh Yah Khalil gashi kuwa kuma qibar ta lokaci daya abin mamaki"
"Shine nima na gani ai, yaushe na ganki na qarshe ai baki kai haka ba yanzu nasan ko Sumayya ai seta buda miki"
"Kai rabani da kamo Sumayya qiba Yah Khalil wannan Mata kamar Bijimar Sa kuma a qaryarta Najib din ne yake son qibar shi yasa taqi ta rage" Unaizan ta fada tana riqe baki, hirar baya suka dakko ana tuna yanda kowa yake da yanda ya zama yanzu Humaira ta shigo da Try data doro kayan ciye ciye Khalil ya kalleta yace
"Kice wannan ma wata rana zata zama giwa kenan" seta waiwaya ta kalleta tana yar dariya tace
"Wannan kuma kiwonka ne ze tabbatar" daga haka ta miqe ta basu guri.
Beyi niyyar jimawa ba amma hirarta me cike da quruciya da labarai da basa qarewa yasa ya shantake se ji sukayi ana magriba. Seda yayi salla a masallacin layin kafin ya koma yayi mata sallama, sun fito ta rakoshi yake sanar mata da zancen zuwansu Jalingo ranar Juma'a se tayi shiru tana juya zoben hannunta.
"Ya naga kinyi shiru, ko bakiyi farin ciki da magana bane?" Ya fada yana kallonta, ba tareda ta dago kanta ba tace
"Amma Yaya cewa kayi fa se na fara makaranta"
"Maganar makaranta Humaira ni nayi miki Alqawari indai karatune zakiyi harse kince kin gaji, nida zaki zama business partner ta, idan na ginawa mutane gida ke kuma kiyi musu furnishing da kayayyaki na yan gayu ko kin fasa bude Interior design company din?" Ya fada cikin lallashi, nan sabuwar hira ta balle, burinta kenan ita a ringa bata kwangilar gidaje tana saka kaya a ciki ta zabi fenti da duk kalar abinda ze dace da gida.
"Karki damu ni zan fara employing naki da na gama miki gidanki zan baki dama ki shiryashi mu gani, kinga idan yayi kyau daga nan zan fara recommending ma abokan kasuwanci na ke amma tare zamu ringa raba ribar fa kin yarda" Khalil ya fada ganin Isha na neman yi suna tsaye seta daga masa kai alamar ta yarda tana murmushi daga nan ya shiga mota yana ce mata
"Karki manta ki gayawa Mama dukda nasan zasuyi magana da Hajiya amma dai ki gaya mata dan ta san da yardarki za'aje" daga haka yaja mota tana daga masa hannu ya bar gurin. Ciki ta koma tana shiga ta gayaqa Unaizatu yanda sukayi dashi.
"Wallahi Humaira kinyi dacen Miji matsala daya ce matarsa amma itan ma Allah ya fita in sha Allahu zakuyi auranku ku zauna lafiya" Unaiza ta fada, Humaira ta rafka tagumi tace
"Nima wlh Anty ita nake tsoro, kinsan fa ranar nan tazo gida, nan ta bata labarin zuwan Umaimah Unaiza ta bude baki tana jinta harta gama tana cewa
"Amma fa karki gayawa kowa dan Mama tace karna fada koshi Yayan be sani ba. Kuma kinga Yaya Mansur ma baya so, kwanaki kirana yayi yana tamun fada akan nacewa Mama banason Yah Khalil ita kuma ta kirashi tayi masa fada shine fa har yanzu yake fushi dani shima Yah Khalil din yace koya kirashi baya dauka to kinga ai shi yasan halin matar abokinsa toh ita Mama taqi ganewa"
"Toh ke kina son Khalil din?" Unaiza ta tambayeta tana kallonta, seta rufe fuska da hannunta tace
"Kai Anty baki san Yah Khalil bane indai kuka fara magana dole ka fara sonsa baka sani ba"
'Toh ai shikenan se kiyita addu'a in sha Allahu babu abinda ze faru se Alkhairi. Yanzu dai ki ajiye shirme ki maida hankali dan kinsan abinda ya kawoki gidan nan, gobe zaki fara zuwa gidan Maman Ayman inaga sau hudu tace a sati zaku ringa Classes din, nasan kin iya girki se ki qara maida hankali ki gane dabarunda zata qara miki sannan akwai saqon da za'a kawo gobe suma ki fara amfanj dasu, bari ma kiga na tashi na hada Miki TULA-TULA ki fara sha wannan qirjin dake nan kamar na yara a samu su taso dan matarsa idan kikaji ana Figure 8 toh itace gara kema kidan qara auki yawwa".
Dariya ta shiga kyalkyalawa jij wani suna wai TULA-TULA, Unaiza ta dawo Salalan ta ajiye mata da madara ta dauka tana cewa
"Wai Anty shine TULA TULAN? ina jira naga wata balloon ni ashe ma kunu ne"
"Ba zaki gane ba yarinya kedai dauki kisha a jikinki zakiga tula tulan da ake magana nan duk da kika ganmu shi yake taimakar mu gamun mun haihu nawa amma Qirji na nan a cike" se ta rufe fuska kuma wai kunya Unaizatu tace
"Kyaji da munafuncinki Malam ni maza ki shanye ki bani kofina.
(Domin mallakar naki ki tuntubi Maman Ilham mai Tula Tula akan 08135613021 tana Kaduna tana aikawa da kaya ko ina a fadin Nigeria).
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 66
UMAIMAH
Kasa zama tayi ta jira Safina ta gwammace ita ta tafi gidanta, a Get suka hadu da Jalilah zata shigo ita kuma zata fita suka jefi juna da kallon Banza motar Jalilah na shiga ta Anty Amina ta biyo baya dole Umaimah ta jira suka shige dan a jere suke se hararar su take tamkar idanunta zasu fado. Jalilah ce ta kwalawa Sammani kira ya bar bakin Get da gudu ya shiga cuki, ta bude masa boot ya dakko wani kwali da Umaimah ke da tabbacin na akwati ne gasu nan guda biyu ya dauki daya ya shige bangaren Hajiya ita kuma Jalilan ta fara fito da kayayyaki daga back sit dinta Haka ma Anty Amina cikinsu babu wanda ya sakw kallon koda inda motarta take. Kwafa taja kafin ta taka motar da qarfi ta bar gidan, a falon Safina ta baje bayan ta soya musu kwai da dankali sunci Wanda turawa kawai Umaimah take amma komai daci yake mata a baki.
"Qawata ki kwantar da hankalinki na kira Malam tun jiya kuma yace kwana zeyi yana aikinki, yace in tambayeki hayaqin daya baki yace kiyi a tsakar gida kinyi kuwa?" Safina ta fada se Umaiman ta tabe baki tace
"Ni hayaqi daya na gani wanda yace na ringayi a dakinsa kuma nayi"
"Sun dauke abinsu kenan" Safinan ta fada kafin taci gaba da cewa
"Haka fa suke wlh se Malam ya baka abu me ci subi dare su dauke abinsu, bari toh na gaya masa ya sake hado miki dashi se kiyi Azama da an kawo ki turara dan alamu sun nuna Faka faka ne" haka tayi ta subadadi ita dai Umaimah jinta takeyi har aka kira Safinan a waya ta fita se gata tareda wnai saurayi se bayan ya zauna Umaimah ta ganeshi Almajirin Malam din da sukaje gurinsa ne.
Wasu sababbin tarkace ya kawo mata harda layu ya bata wasu qananu da yace a abinci zata sakawa Khalil din ta tabbatar da ya hafiye se wata lafceciya da zata tsaga pillow ta saka a ciki, se Rubutu irin na farko yace ta qara ruwa ta bashi dana Abincin shima harda qarin na Nama kamar yaji yake amma shi da gasashshen nama za'aci yaron ya miqa mata yana cewa
"Dandanonsa kamar yaji yake amma fa ki kula koke karki dandana kuma kar ki bashi yaci sama da sau dan qarfi ne dashi wlh, yace wancan turarenya qare amma idan an hada wani za'a kawo miki kuma wai ki ringa haquri kina danne zuciyarki dan kinada saurin fushi da hasala ga qawa zuci shi yasa aikinki baze ci da sauri ba". Daze tafi wasu uban nin kudin Safina ta debo ta bashiya kaiwa Malam sannan ta bashi na mota ya wuce yana musu godiya.
"Nifa bazanyi amfani dasu ba ingaya miki wanda ya banin ma me suka mun balle na qara wasu, tashi zanyi ma na tafi yanzu naje naci kutumar ubansu gaba daya dan nasam sun hadu a gidanda zan fito yar iskar Jalilan nan da Amina sunzo nasan Jamilan ma tana tafe duk zan hada naci uwarsu la'ada waje" Umaimah ta fada Safina dake hade mata kan tarkacenta tace
"Umaimah ikon Allah, na roqeki sau daya a rayuwa ki gwada juriya ki dauke kai ki bawa aikin nan sati daya kedai ki tabbata kinyi komai yanda Malam yace se ki koma gefe ki zubawa sarautar Allah ido wlh na tabbata se kin sha Mamaki"
"Ikon Allah Unaiza, ashe zakiyi qiba" Khalil daya kasa shiru ya fada se ta fashe da dariya ita kanta abin mamaki yake bata tace
"Wlh Yah Khalil gashi kuwa kuma qibar ta lokaci daya abin mamaki"
"Shine nima na gani ai, yaushe na ganki na qarshe ai baki kai haka ba yanzu nasan ko Sumayya ai seta buda miki"
"Kai rabani da kamo Sumayya qiba Yah Khalil wannan Mata kamar Bijimar Sa kuma a qaryarta Najib din ne yake son qibar shi yasa taqi ta rage" Unaizan ta fada tana riqe baki, hirar baya suka dakko ana tuna yanda kowa yake da yanda ya zama yanzu Humaira ta shigo da Try data doro kayan ciye ciye Khalil ya kalleta yace
"Kice wannan ma wata rana zata zama giwa kenan" seta waiwaya ta kalleta tana yar dariya tace
"Wannan kuma kiwonka ne ze tabbatar" daga haka ta miqe ta basu guri.
Beyi niyyar jimawa ba amma hirarta me cike da quruciya da labarai da basa qarewa yasa ya shantake se ji sukayi ana magriba. Seda yayi salla a masallacin layin kafin ya koma yayi mata sallama, sun fito ta rakoshi yake sanar mata da zancen zuwansu Jalingo ranar Juma'a se tayi shiru tana juya zoben hannunta.
"Ya naga kinyi shiru, ko bakiyi farin ciki da magana bane?" Ya fada yana kallonta, ba tareda ta dago kanta ba tace
"Amma Yaya cewa kayi fa se na fara makaranta"
"Maganar makaranta Humaira ni nayi miki Alqawari indai karatune zakiyi harse kince kin gaji, nida zaki zama business partner ta, idan na ginawa mutane gida ke kuma kiyi musu furnishing da kayayyaki na yan gayu ko kin fasa bude Interior design company din?" Ya fada cikin lallashi, nan sabuwar hira ta balle, burinta kenan ita a ringa bata kwangilar gidaje tana saka kaya a ciki ta zabi fenti da duk kalar abinda ze dace da gida.
"Karki damu ni zan fara employing naki da na gama miki gidanki zan baki dama ki shiryashi mu gani, kinga idan yayi kyau daga nan zan fara recommending ma abokan kasuwanci na ke amma tare zamu ringa raba ribar fa kin yarda" Khalil ya fada ganin Isha na neman yi suna tsaye seta daga masa kai alamar ta yarda tana murmushi daga nan ya shiga mota yana ce mata
"Karki manta ki gayawa Mama dukda nasan zasuyi magana da Hajiya amma dai ki gaya mata dan ta san da yardarki za'aje" daga haka yaja mota tana daga masa hannu ya bar gurin. Ciki ta koma tana shiga ta gayaqa Unaizatu yanda sukayi dashi.
"Wallahi Humaira kinyi dacen Miji matsala daya ce matarsa amma itan ma Allah ya fita in sha Allahu zakuyi auranku ku zauna lafiya" Unaiza ta fada, Humaira ta rafka tagumi tace
"Nima wlh Anty ita nake tsoro, kinsan fa ranar nan tazo gida, nan ta bata labarin zuwan Umaimah Unaiza ta bude baki tana jinta harta gama tana cewa
"Amma fa karki gayawa kowa dan Mama tace karna fada koshi Yayan be sani ba. Kuma kinga Yaya Mansur ma baya so, kwanaki kirana yayi yana tamun fada akan nacewa Mama banason Yah Khalil ita kuma ta kirashi tayi masa fada shine fa har yanzu yake fushi dani shima Yah Khalil din yace koya kirashi baya dauka to kinga ai shi yasan halin matar abokinsa toh ita Mama taqi ganewa"
"Toh ke kina son Khalil din?" Unaiza ta tambayeta tana kallonta, seta rufe fuska da hannunta tace
"Kai Anty baki san Yah Khalil bane indai kuka fara magana dole ka fara sonsa baka sani ba"
'Toh ai shikenan se kiyita addu'a in sha Allahu babu abinda ze faru se Alkhairi. Yanzu dai ki ajiye shirme ki maida hankali dan kinsan abinda ya kawoki gidan nan, gobe zaki fara zuwa gidan Maman Ayman inaga sau hudu tace a sati zaku ringa Classes din, nasan kin iya girki se ki qara maida hankali ki gane dabarunda zata qara miki sannan akwai saqon da za'a kawo gobe suma ki fara amfanj dasu, bari ma kiga na tashi na hada Miki TULA-TULA ki fara sha wannan qirjin dake nan kamar na yara a samu su taso dan matarsa idan kikaji ana Figure 8 toh itace gara kema kidan qara auki yawwa".
Dariya ta shiga kyalkyalawa jij wani suna wai TULA-TULA, Unaiza ta dawo Salalan ta ajiye mata da madara ta dauka tana cewa
"Wai Anty shine TULA TULAN? ina jira naga wata balloon ni ashe ma kunu ne"
"Ba zaki gane ba yarinya kedai dauki kisha a jikinki zakiga tula tulan da ake magana nan duk da kika ganmu shi yake taimakar mu gamun mun haihu nawa amma Qirji na nan a cike" se ta rufe fuska kuma wai kunya Unaizatu tace
"Kyaji da munafuncinki Malam ni maza ki shanye ki bani kofina.
(Domin mallakar naki ki tuntubi Maman Ilham mai Tula Tula akan 08135613021 tana Kaduna tana aikawa da kaya ko ina a fadin Nigeria).
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 66
UMAIMAH
Kasa zama tayi ta jira Safina ta gwammace ita ta tafi gidanta, a Get suka hadu da Jalilah zata shigo ita kuma zata fita suka jefi juna da kallon Banza motar Jalilah na shiga ta Anty Amina ta biyo baya dole Umaimah ta jira suka shige dan a jere suke se hararar su take tamkar idanunta zasu fado. Jalilah ce ta kwalawa Sammani kira ya bar bakin Get da gudu ya shiga cuki, ta bude masa boot ya dakko wani kwali da Umaimah ke da tabbacin na akwati ne gasu nan guda biyu ya dauki daya ya shige bangaren Hajiya ita kuma Jalilan ta fara fito da kayayyaki daga back sit dinta Haka ma Anty Amina cikinsu babu wanda ya sakw kallon koda inda motarta take. Kwafa taja kafin ta taka motar da qarfi ta bar gidan, a falon Safina ta baje bayan ta soya musu kwai da dankali sunci Wanda turawa kawai Umaimah take amma komai daci yake mata a baki.
"Qawata ki kwantar da hankalinki na kira Malam tun jiya kuma yace kwana zeyi yana aikinki, yace in tambayeki hayaqin daya baki yace kiyi a tsakar gida kinyi kuwa?" Safina ta fada se Umaiman ta tabe baki tace
"Ni hayaqi daya na gani wanda yace na ringayi a dakinsa kuma nayi"
"Sun dauke abinsu kenan" Safinan ta fada kafin taci gaba da cewa
"Haka fa suke wlh se Malam ya baka abu me ci subi dare su dauke abinsu, bari toh na gaya masa ya sake hado miki dashi se kiyi Azama da an kawo ki turara dan alamu sun nuna Faka faka ne" haka tayi ta subadadi ita dai Umaimah jinta takeyi har aka kira Safinan a waya ta fita se gata tareda wnai saurayi se bayan ya zauna Umaimah ta ganeshi Almajirin Malam din da sukaje gurinsa ne.
Wasu sababbin tarkace ya kawo mata harda layu ya bata wasu qananu da yace a abinci zata sakawa Khalil din ta tabbatar da ya hafiye se wata lafceciya da zata tsaga pillow ta saka a ciki, se Rubutu irin na farko yace ta qara ruwa ta bashi dana Abincin shima harda qarin na Nama kamar yaji yake amma shi da gasashshen nama za'aci yaron ya miqa mata yana cewa
"Dandanonsa kamar yaji yake amma fa ki kula koke karki dandana kuma kar ki bashi yaci sama da sau dan qarfi ne dashi wlh, yace wancan turarenya qare amma idan an hada wani za'a kawo miki kuma wai ki ringa haquri kina danne zuciyarki dan kinada saurin fushi da hasala ga qawa zuci shi yasa aikinki baze ci da sauri ba". Daze tafi wasu uban nin kudin Safina ta debo ta bashiya kaiwa Malam sannan ta bashi na mota ya wuce yana musu godiya.
"Nifa bazanyi amfani dasu ba ingaya miki wanda ya banin ma me suka mun balle na qara wasu, tashi zanyi ma na tafi yanzu naje naci kutumar ubansu gaba daya dan nasam sun hadu a gidanda zan fito yar iskar Jalilan nan da Amina sunzo nasan Jamilan ma tana tafe duk zan hada naci uwarsu la'ada waje" Umaimah ta fada Safina dake hade mata kan tarkacenta tace
"Umaimah ikon Allah, na roqeki sau daya a rayuwa ki gwada juriya ki dauke kai ki bawa aikin nan sati daya kedai ki tabbata kinyi komai yanda Malam yace se ki koma gefe ki zubawa sarautar Allah ido wlh na tabbata se kin sha Mamaki"