Sashe 246
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muna yiwa Ubangiji laifi ya yafe mana wani ma ba tareda mun roqi afuwarsa ba me yasa bazamuyi koyi da haka ba muma mu zama masuyin uzuri ga junanmu? Mu rungumeta mu tayata fuskantar duk wani qalubale daze taradda ita bawai muci gaba da tunzurata ba harta sare nutsuwar data saukar mata ta barta ta koma ruwa abinda zata aikata se sunfi na baya muni sannan duniya taci gaba dayi mana tofin ala tsine saboda baza'a zagi Umaimah ita kadai ba tilas duk wanda labarinta ya riske shi seya hada da ahalinta".
Kalaman Anty suka kashe musu jiki muqus suka kasa yin ko wani kwakwkwaran motsi a gurin se jan majina da ajiyar zuciya sukeyi. Tabbas Anty batayi qarya ba suna da hannu cikin tabarbarewar Umaimah kuskurensu kuwa shine fushin zuciya da sukeyi akan lamuranta da kuma qin tsanantawa da cusa kai yanda bata daukarsu da muhimmanci suma suka saketa ta hadu da masu tunani irin nata suka qara dulmiyata ruwa gashi yanzu suna raba bacin randa ita dan duk inda suka shiga a shekarun baya se anyi zundensu wasu ma suna fadin da saka hannunsu tayi abinda tayin, a lokacin Maman Asad Mijinta fasa auran dayayi niyya yayi saboda ya tsorata da abinda Umaimah ta aikata. dukda be taba ce mata komai akan maganar ba itace dataji zancen fasa auran tayi masa magana kai tsaye kuma yace mata
"Daman bawai na matsu danayi auran bane kuma na haqura tunda ina sonki kar nayi biyu babu" maganarsa ta daure mata kai sosai kuka bata fahimce shi ba seda yan uwansa suka tasata a gaba suka ringa yada mata da magana sannan ta fuskanci tsoratar da yayi, har kuka seda tayi tana ce masa ko a tunani bata taba kawo cewar ta cutar dashi saboda zeyi abinda Allah ne ya halasta masa ba shi kuwa yace mata babu wannan maganar, daman rashin nuna damuwar da tayi ya bashi mamaki to maganin kar ayi kar a fara aure dai ya haqura har gaban Abada na bar maganar qara aure Hajiyayye ta ishe shi shikenan maganar ta mutu.
Ranar dai haka sukayi wunin jigum jigum Abba ya dawo Anty ta kwashe yanda akayi ta mayar masa ya ringa fada kamar ze ari baki ga baccin da Umaimah take tayi ya sake rufe Nuratu da bala'in me ta bata har yana rantsuwar idan suka kashe masa Ya duk se yayi qararsu ai badan basa son ta bane laifi tayi suke nuna mata kuskurenta ba kuma hakan ne yake nuna basa qaunarta ba. Nuratu ta ringa rantse rantae akanita maganin bacvi kawaita bata saboda damuwar data shiga komai ze iya faruwa da jininta ko zuciyarta amma idan ta samu bacci zata huta kuma hankalinta ya kwanta, be barta ta fita daga gidan ba se qarfe goma bayan Umaimah ta farka kuma Mijinta Dr Sagir yazo ya qara tabbatar masa da maganindata bata bashi da illah, wai ranar har Abba ne yakecewa shi be gama yarda da sahihancin Likitancin ta ba, ya manta da cewar ita take kula dashi, kaf jinyar hawan jinin da Umaimah ta sababamas aita ce take lura dashi amma yau da yake antabo tsomar zuciyarsa ya fitittike, daman abinda take amfani dashi kenan ta karanci sunfi sonta shiyasa take wahal dasu, kuma daman a rubuce take, duk abinda mutum ya kwallafa rai a kansa se an jarabce su dashi, babu wata soyayya data cancanci dukkan zuciya data wuci ta Allah da Manzonsa.
Wannan dambaruwa ta ninka damuwar Umaimah, duk yanda suka yi qoqarin nuna mata komai ya wuce hatta da Naziyya da kanta ta bata haquri ta kuma nemi afuwarta ta akan abinda ta fada ta gagara samun nutsuwa. Kalaman Naziyyar sunyi matuqar yi mata tasiri kuma sun qara tsoratata tareda maido mata da abubuwan da suka wuce tana hasaso ta inda haqqindata fada ze fara bibiyarta, a kullum ta daga hannu sama takance
"Allah ka bani ikon neman yafiyar wadanda na zalunta tun ina da sauran numfashi, ubangiji na roqeka karka karbi raina na dawo gareka da nauyin wani akaina Allah ka dubeni ka karbi tubana ka kawo mun dauki a cikin al'amurana", a haka rayuwa taci gaba da tafiya, duk yanda take tunanin samun sauqi abun ya faskara, damuwa ta mata yawa, hatta da zobon data fara ta saki dan masu siyan zobon da yawa da biyu suke mata cinikin izgili da wulaqanci yake sakasu siyan zobon dan hatta gidansu an canza masa suna zuwa gidansu Umaimah me zobo irin abubuwan da ake mata idan an shigo siyan zobo na izgili da wulanci ya saka Abba ya hanatayi, ta roqeshi akan ya barta taci gaba amma zata samu Almajiri ya ringa fita dashi waje a dena shigowa cikin gida siya dan har sannan dubi dayan nan yake bata zobo kuwa ba qaramin rufin Asiri yake kawo mata ba sannan suma yan gidan susha, na musamman takeyiwa Abban saboda yana da Sugar kullum kuma yasha ze saka mata albarka ko babu komai zata tasiranci bacin ran data sakasu a baya shiyasa ta nace akan ya barta taci gaba, sedai sau biyu tayi ta bari gaba daya dan ranar farko na dubu biyu tayi bama kamar yanda ta sabayi a cikin gida ba zubin Hamsin da Dari takeyi seta yi na dubu biyar ya qare tas har ana nema se gashi a na dubu biyun dakyar akayi dari bakwai, dari biyar ma Almajirin ya kai mata wai sauran bashi aka karba Jikokin gidan suka shanye dan ranar suna nan washe gari yanda aka fita dashi haka aka dawo mata dashi dan taja masa kunne akan karya bada bashi yace kuma duk wanda yaje wai se yace bashi shiyasa ya dawo mata dashi shikenan sana'ar zobo ta gurgunce ta tasa dan abinda ta tara a gaba da buqatu suka qare ta sake komawa yar gidan jiya amma duk wannanbe wani dameta sosai ba domin tasan kowanne tsanani yana tareda sauqi kuma wata rana komai ze zama tarihi.
Babban tashin hankalinta a yanzu fitinar Bibi da a kullum qara bunqasa takeyi, a yanzu bata kwana uku bataje gidanba haka zata tasata a gaba da kuka akan ta dawo gidansu idan tayiwa Dady magana se yace ta tambayeta shi babu ruwansa itace taqi dawowa, idan ta saka mata wannan darun seta ce mata
"Idan kinyi sallah kullum ki ringa mana addu'a idan da Alkhairi tsakanina da Dadynku Allah ya daidaita mu".
Bibin bama gane hausar takeyi ba, data gaji da nacin tambayar Umaiman ta ranar ta tambayi Mama yaushe Momynsu zata koma, kai tsaye tace mata
"Momynki da Dadynki sun rabu ya saketa ba zata sake komawa gidanku ba ga sabuwar Momy nan ya samo muku kuma tana sonku tana kula daku keda kanki kina fadamun koba haka ba? Dan haka itace matar Dadynku yanzu Momynku kuma gata nan anan gidan kina zuaa kina ganinta karki sake damun wani da tambayar yaushe zata koma gidanku dan ba zata koma ba".
Umaimah tayi tsam dan kalaman Maman basu mata dadi ba sannan gani takeyi ai sunyiwa Bibi girma ba zata fahimci abinda take nufi ba, ga mamakinsu gaba daya se ji sukayi yarinyar tace
"Dama Halima ta gaya mun indai Mamah tana gidan mu Momy ba zata taba komawa ba dan haka zan gayawa Dady sedai ya zaba ko Momy ko Mamah"
Umaimah ta riqe baki, Mama ta fizgota tana cewa
"Dan ubanki wacece wannan Halimar da kika samu da duk wani abu na diban albarka idan kinayi zakice Halima ce takeyi ko ita ta fada? Tun yanzu kema kin fara tara qawayen banza masu gurbata tunani ko to kuwa baze sabu ba da kaina zan kira uban naki sedai ya canza miki makaranta ya rabaki da koma wacece da take nema dasa miki mummunar dabi'ar qin matar ubanki" ta sata a hammata ta kileta, tana kuka take cewa
"Wlh sena gaya masa kuma ai yana sona nasan zeyi abinda nace" ta ringa birgima tana tijara, Mama ta dakko wata dorinar Yasir da yake zane yara a Islamiyya wai shi prefect ta ringa caula mata ba shiri ta miqe ta bita seda tayi mata lilis kafin ta watso mata hijabinta da wata yar Berbi bag tace
"Wuce ki tafi, daman zanzo har gidan naku Allah yasa naji wani labari mara dadi zaki gane kurenki yar banza me kunne kamar Area", ita dai bata ko debi takalmanta ba tayi waje seta dawo da gudu tana kuka tace wa Maman
"Kuma Hajiya tace na gaya miki Mamah ta haihu amma bazan fada ba tunda kika dokeni kuma dan kiji Babyn qato fari irin Aryaan sunansa ma Mukhtar Dady yace" tana gama fada ta diba da gudu ta fice, daman ita kadai aka kawo Manniru ya dauketa suka wuce gida tun kuma daga wannan zuwan seda aka kwashi tsahon lokaci basu je ba.
Wani irin Duum, kunnen Umaimah yayi mata, ta kalli Mama data bi Bibin da dariyar yarintarta tana cewa
"Ja'ira to ai kin fadi saqon Masha Allahu Allah ya dayyaba wannan karon ko zamuje barka in Allah ya yarda bari Alhaji ya dawo na gaya masa gashi ma Takwara ya samu, Allah ya rayashi yayi masa Albarka" har Mama tagama addu'arta ta juya tana zaune inda take wani irin abu ya shiga bijiro mata seta dafe zuciyarta a fili ta shiga maimaita Innalillahi, Mama ta kalleta ta gyada kai tana cewa
"Iska na wahal dame kayan kara, to ke yanzu Kishi za'ace yana damunki ko kuwa baqin cikin kinji matarsa ta haihu lahanin da kika masa beyi tasiri ba se kije ki dauki ruwan sanyi kisha kiyi maimaita Hasbunallahu ko kya samu ciwon naki ya lafa" taja tsaki ta shige daki hali irin na Umaimah dai Allah ya canzawa masu shi. Ita kuwa daki ta cige ta kife akan Gado ta shiga kukan da bata san dalilinsa ba, Khalil dai rayuwarsa yake yi ya manta da ita da alama ita ce take ta dakon soyayyarsa da yaqinin wata rana ze iya sake dubanta amma daga alamun da take gani bata da wannan sauran damar.
GIDAN KHALIL
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 84
Kalaman Anty suka kashe musu jiki muqus suka kasa yin ko wani kwakwkwaran motsi a gurin se jan majina da ajiyar zuciya sukeyi. Tabbas Anty batayi qarya ba suna da hannu cikin tabarbarewar Umaimah kuskurensu kuwa shine fushin zuciya da sukeyi akan lamuranta da kuma qin tsanantawa da cusa kai yanda bata daukarsu da muhimmanci suma suka saketa ta hadu da masu tunani irin nata suka qara dulmiyata ruwa gashi yanzu suna raba bacin randa ita dan duk inda suka shiga a shekarun baya se anyi zundensu wasu ma suna fadin da saka hannunsu tayi abinda tayin, a lokacin Maman Asad Mijinta fasa auran dayayi niyya yayi saboda ya tsorata da abinda Umaimah ta aikata. dukda be taba ce mata komai akan maganar ba itace dataji zancen fasa auran tayi masa magana kai tsaye kuma yace mata
"Daman bawai na matsu danayi auran bane kuma na haqura tunda ina sonki kar nayi biyu babu" maganarsa ta daure mata kai sosai kuka bata fahimce shi ba seda yan uwansa suka tasata a gaba suka ringa yada mata da magana sannan ta fuskanci tsoratar da yayi, har kuka seda tayi tana ce masa ko a tunani bata taba kawo cewar ta cutar dashi saboda zeyi abinda Allah ne ya halasta masa ba shi kuwa yace mata babu wannan maganar, daman rashin nuna damuwar da tayi ya bashi mamaki to maganin kar ayi kar a fara aure dai ya haqura har gaban Abada na bar maganar qara aure Hajiyayye ta ishe shi shikenan maganar ta mutu.
Ranar dai haka sukayi wunin jigum jigum Abba ya dawo Anty ta kwashe yanda akayi ta mayar masa ya ringa fada kamar ze ari baki ga baccin da Umaimah take tayi ya sake rufe Nuratu da bala'in me ta bata har yana rantsuwar idan suka kashe masa Ya duk se yayi qararsu ai badan basa son ta bane laifi tayi suke nuna mata kuskurenta ba kuma hakan ne yake nuna basa qaunarta ba. Nuratu ta ringa rantse rantae akanita maganin bacvi kawaita bata saboda damuwar data shiga komai ze iya faruwa da jininta ko zuciyarta amma idan ta samu bacci zata huta kuma hankalinta ya kwanta, be barta ta fita daga gidan ba se qarfe goma bayan Umaimah ta farka kuma Mijinta Dr Sagir yazo ya qara tabbatar masa da maganindata bata bashi da illah, wai ranar har Abba ne yakecewa shi be gama yarda da sahihancin Likitancin ta ba, ya manta da cewar ita take kula dashi, kaf jinyar hawan jinin da Umaimah ta sababamas aita ce take lura dashi amma yau da yake antabo tsomar zuciyarsa ya fitittike, daman abinda take amfani dashi kenan ta karanci sunfi sonta shiyasa take wahal dasu, kuma daman a rubuce take, duk abinda mutum ya kwallafa rai a kansa se an jarabce su dashi, babu wata soyayya data cancanci dukkan zuciya data wuci ta Allah da Manzonsa.
Wannan dambaruwa ta ninka damuwar Umaimah, duk yanda suka yi qoqarin nuna mata komai ya wuce hatta da Naziyya da kanta ta bata haquri ta kuma nemi afuwarta ta akan abinda ta fada ta gagara samun nutsuwa. Kalaman Naziyyar sunyi matuqar yi mata tasiri kuma sun qara tsoratata tareda maido mata da abubuwan da suka wuce tana hasaso ta inda haqqindata fada ze fara bibiyarta, a kullum ta daga hannu sama takance
"Allah ka bani ikon neman yafiyar wadanda na zalunta tun ina da sauran numfashi, ubangiji na roqeka karka karbi raina na dawo gareka da nauyin wani akaina Allah ka dubeni ka karbi tubana ka kawo mun dauki a cikin al'amurana", a haka rayuwa taci gaba da tafiya, duk yanda take tunanin samun sauqi abun ya faskara, damuwa ta mata yawa, hatta da zobon data fara ta saki dan masu siyan zobon da yawa da biyu suke mata cinikin izgili da wulaqanci yake sakasu siyan zobon dan hatta gidansu an canza masa suna zuwa gidansu Umaimah me zobo irin abubuwan da ake mata idan an shigo siyan zobo na izgili da wulanci ya saka Abba ya hanatayi, ta roqeshi akan ya barta taci gaba amma zata samu Almajiri ya ringa fita dashi waje a dena shigowa cikin gida siya dan har sannan dubi dayan nan yake bata zobo kuwa ba qaramin rufin Asiri yake kawo mata ba sannan suma yan gidan susha, na musamman takeyiwa Abban saboda yana da Sugar kullum kuma yasha ze saka mata albarka ko babu komai zata tasiranci bacin ran data sakasu a baya shiyasa ta nace akan ya barta taci gaba, sedai sau biyu tayi ta bari gaba daya dan ranar farko na dubu biyu tayi bama kamar yanda ta sabayi a cikin gida ba zubin Hamsin da Dari takeyi seta yi na dubu biyar ya qare tas har ana nema se gashi a na dubu biyun dakyar akayi dari bakwai, dari biyar ma Almajirin ya kai mata wai sauran bashi aka karba Jikokin gidan suka shanye dan ranar suna nan washe gari yanda aka fita dashi haka aka dawo mata dashi dan taja masa kunne akan karya bada bashi yace kuma duk wanda yaje wai se yace bashi shiyasa ya dawo mata dashi shikenan sana'ar zobo ta gurgunce ta tasa dan abinda ta tara a gaba da buqatu suka qare ta sake komawa yar gidan jiya amma duk wannanbe wani dameta sosai ba domin tasan kowanne tsanani yana tareda sauqi kuma wata rana komai ze zama tarihi.
Babban tashin hankalinta a yanzu fitinar Bibi da a kullum qara bunqasa takeyi, a yanzu bata kwana uku bataje gidanba haka zata tasata a gaba da kuka akan ta dawo gidansu idan tayiwa Dady magana se yace ta tambayeta shi babu ruwansa itace taqi dawowa, idan ta saka mata wannan darun seta ce mata
"Idan kinyi sallah kullum ki ringa mana addu'a idan da Alkhairi tsakanina da Dadynku Allah ya daidaita mu".
Bibin bama gane hausar takeyi ba, data gaji da nacin tambayar Umaiman ta ranar ta tambayi Mama yaushe Momynsu zata koma, kai tsaye tace mata
"Momynki da Dadynki sun rabu ya saketa ba zata sake komawa gidanku ba ga sabuwar Momy nan ya samo muku kuma tana sonku tana kula daku keda kanki kina fadamun koba haka ba? Dan haka itace matar Dadynku yanzu Momynku kuma gata nan anan gidan kina zuaa kina ganinta karki sake damun wani da tambayar yaushe zata koma gidanku dan ba zata koma ba".
Umaimah tayi tsam dan kalaman Maman basu mata dadi ba sannan gani takeyi ai sunyiwa Bibi girma ba zata fahimci abinda take nufi ba, ga mamakinsu gaba daya se ji sukayi yarinyar tace
"Dama Halima ta gaya mun indai Mamah tana gidan mu Momy ba zata taba komawa ba dan haka zan gayawa Dady sedai ya zaba ko Momy ko Mamah"
Umaimah ta riqe baki, Mama ta fizgota tana cewa
"Dan ubanki wacece wannan Halimar da kika samu da duk wani abu na diban albarka idan kinayi zakice Halima ce takeyi ko ita ta fada? Tun yanzu kema kin fara tara qawayen banza masu gurbata tunani ko to kuwa baze sabu ba da kaina zan kira uban naki sedai ya canza miki makaranta ya rabaki da koma wacece da take nema dasa miki mummunar dabi'ar qin matar ubanki" ta sata a hammata ta kileta, tana kuka take cewa
"Wlh sena gaya masa kuma ai yana sona nasan zeyi abinda nace" ta ringa birgima tana tijara, Mama ta dakko wata dorinar Yasir da yake zane yara a Islamiyya wai shi prefect ta ringa caula mata ba shiri ta miqe ta bita seda tayi mata lilis kafin ta watso mata hijabinta da wata yar Berbi bag tace
"Wuce ki tafi, daman zanzo har gidan naku Allah yasa naji wani labari mara dadi zaki gane kurenki yar banza me kunne kamar Area", ita dai bata ko debi takalmanta ba tayi waje seta dawo da gudu tana kuka tace wa Maman
"Kuma Hajiya tace na gaya miki Mamah ta haihu amma bazan fada ba tunda kika dokeni kuma dan kiji Babyn qato fari irin Aryaan sunansa ma Mukhtar Dady yace" tana gama fada ta diba da gudu ta fice, daman ita kadai aka kawo Manniru ya dauketa suka wuce gida tun kuma daga wannan zuwan seda aka kwashi tsahon lokaci basu je ba.
Wani irin Duum, kunnen Umaimah yayi mata, ta kalli Mama data bi Bibin da dariyar yarintarta tana cewa
"Ja'ira to ai kin fadi saqon Masha Allahu Allah ya dayyaba wannan karon ko zamuje barka in Allah ya yarda bari Alhaji ya dawo na gaya masa gashi ma Takwara ya samu, Allah ya rayashi yayi masa Albarka" har Mama tagama addu'arta ta juya tana zaune inda take wani irin abu ya shiga bijiro mata seta dafe zuciyarta a fili ta shiga maimaita Innalillahi, Mama ta kalleta ta gyada kai tana cewa
"Iska na wahal dame kayan kara, to ke yanzu Kishi za'ace yana damunki ko kuwa baqin cikin kinji matarsa ta haihu lahanin da kika masa beyi tasiri ba se kije ki dauki ruwan sanyi kisha kiyi maimaita Hasbunallahu ko kya samu ciwon naki ya lafa" taja tsaki ta shige daki hali irin na Umaimah dai Allah ya canzawa masu shi. Ita kuwa daki ta cige ta kife akan Gado ta shiga kukan da bata san dalilinsa ba, Khalil dai rayuwarsa yake yi ya manta da ita da alama ita ce take ta dakon soyayyarsa da yaqinin wata rana ze iya sake dubanta amma daga alamun da take gani bata da wannan sauran damar.
GIDAN KHALIL
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 84