Sashe 2
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Oh ni Anya Yaya Malika lamarin Umaimah babu iskokai a ciki kuwa? Kiga dai farin jini irin na yaran gidan nan, tun fa kafin su gama sakandire suke tsaida mazaje amma ace Umaimah har tana shirin gama HND babu wani tsayayye abu kullum watangaririya ake, se an shirya magan rigidi rigidi se wani tsautsayin ya gifta. ita ba mummunar sufa ba bare ace finta sauran sukayi, waccen miskilar ma ta samu tsayayye balle ita me wayayyen kai ace abu ya gagara? Nifa wannan fadan nata ma gani nake bana lafiya bane gaskiya ya kamata mu tashi tsaye" Anty Laure ta fada tana kallon yayar tata.
"Babu wasu iska sedai iskanci Laure kamar baki san wacece Umaimah ba. kuma da like batun tsayayye ai ba samarin me bata dasu ba, kullum zuwa suke amma mugun halinta da baqin kishi na ba gaira babu data dorawa kanta shi yake korar su. Ni damab na deba lissafa kawo mata kudin aure a wani abu, idan ba ji nayi an daurawa Umaimah aure ba shine kadai zan tabbatar da Miji ya tsaya dan a cikin sakanni tana iya tafka wautar da zata sa ace anfasa auranta.
Toh wane gantalalle ne tun be aureta ba zata fara dora masa ciwon kai ya tsaya?
nake gaya miki fa nan tayiwa Qasim cin mutunci ko kare baze ci ba wai kawai dan ya gaisa da abokiyar karatun ta shi kuma junior sace yarinyar tare sukayi secondary wallahi bakiji ba ina sallah a tsakar gidannan ina jiyota Allah Allah nake na idar na fita naci ubanta akayi sa'a yayansu yazo ya faffalla mata mari tayo ciki, ni nayi mamaki ma da har yau basu aiko sun karbi kudin auransu ba" Mama ta fada cikin matuqar takaici.
"Ashsha abu beyi kyau ba amma me yasa take haka ne, ya ilahi ke ace saurayinki baze kula wata mace ba toh inaga anyi aure kuma" Anty Laure ta fada cikin jimami tana juya hannu.
"Kema kya fada dai, shi yasa na dena raba takaici ta da kowa duk abinda tayi wanda ya gani ya gani shikenan fatana dai kullum shine ubangiji ya shiryeta dan dai wannan halin nata ba hali me kyau bane"
"Addu'ar dai kam ita ce amma dai Yaya karki qi ta tawa Allaha binciketa dai qila da sharrin iskar kin san fa daman baa ganewa se abu yayi tsamari baa fata sannan suke bayyana"
"Allah ya rufa asiri" kawai Mama tace mata ta janyo wata hirar dan ita duk wata sabga da zaace ta hada da malamai ba sonta take ba. Balle kuma Umaimah da sarai ta san babu abinda yake damunta, suma mantaqa sukayi amma ai tun tana qanqanuwarta haka take da bala'in kishi wani baze fita ba, idan kuwa abu ne idan bata dashi tofa sedai kowa ya rasa.
Tayi iya qoqarinta gurin canza mata wannan muguwar Dabi'a abin kuma yayi sauqi se a yanzu da shekarun hankali suka zo mata kuma abu ya ke sake ta'azzara, kuma a duk sanda Shedan ya buga mata gangar ta hau bata ji bata gani sedai fatan Allah ya shirya kawai.
UMAIMAH
Suna fita fuskar nan tata a cukule saboda maganar da Maman tayi suka shiga gidan Maman Nana, basu bata lokaci ba ta take mata rigar ta saka. Dinkine akayi mata na dibar Albarka ya fito mata da duk wata sura da take da ita domin kuwa Allah ya mata qira me kyau, tana da wani irin shape da ko mace ta kalleta seta qara kallo ta.
"Yanzu Umaimah da wannan Kayan zaki fita? Wai me yasa kike haka ne, baki san wannan abin da kike cin amanar iyayenki kike ba?
Ya za'ayi ki fito daga gidanku da shigar Mutunchi amma a waje a ganki da wata shiga ta daban? Wallahi ina jiye miki ranar da wani a gidan ku ze san abinda kikeyi nasan se kin gane kurenki wallahi kiyi ta biyewa su Nabila Sani su dai kin san a gida suka samu lasisin yin duk abinda sukeyi sedai su jira Kamun Allah" Rumah ta fada tana qarewa Umaimah dake daukar selfie Kallo. Kayan sun kamata matuqa ga kalar Atamfar data karbi fatarta dole ma ta fuzgi hankalinka ka kalleta.
"Sedai idan ke zakije ki fada, ni wuce muje ga me Napep din nan an samo" Umaimah ta fada ko a jikin ta tana zura wayarta a jaka daidai sanda Nana data aika ta taro musu dan sahu ta dawo, haka Rumah ta bita a baya cike da Takaicin halin qawar tata, badan gudun abinda kaje ka dawo ba wallahi seta fadawa Mama wannan muguwar dabi'ar data koya a gurin su Nabila.
Da sam ba haka take ba, da wuya kaga Umaimah ta saka kayan daya bayyana surar ta dan ba tarbiyyar gidan su bace amma shigar su Poly tunda ta hadu da sababbin qawaye irinsu Halima Mailafiya, Fannah Babagana, Nabila Sani se Fauziyya Kura, Izawaqa Mansur da ita Rumasa'u da daman tun Secondary suke tare . acikin su Ruma ce me sanyin Hali ba kuma tayin irin abinda sukeyi.
Nabila da Fauziyya sun fi kowa budadden ido a cikin su bayan Ruma sune mafiya kusanci da Umaimah kumasu suke qara dorata akan duk wani bigire mara kyau kasancewarta me saurin yarda da sakewa da mutane, gashi ita a rayuwarta tana jin maganar qawa kusan sama data kowa.
Tun tana dardar idan zaayi bikin qawar su aka fitar da Anko su suke kawo Style dinda zaayi na zamani na rashi mutunchi tace baza abarta ta saka a gida ba su suka kawo mata dabarar kin sakawar ta bari seta fito waje, dan a Auran Fannah ma dinki biyu aka mata. Wanda ta saka ta fito daga gida daban haka bayan sunje gurin bikin ta cire ta canza wani.
Rumasa'u na matuqar baqin ciki da wannan dabi'a tasu kuma duk ta yanda zata fahimtar da Umaimah cewar tsakanin ta dasu akwai Banbanci na tarbiyya da mutunchi taqi ta ji, sabo da shaquwar da take tsakaninsu tun yarinta ita tasaka ta kasa fita daga cikin group din nasu amma duk da haka kullum cikin yi musu Nasiha take bata damuwa da kyara da hantara da kiranta bagidajiya da sukeyi ita dai fatanta su dawo kan Hanya.
Haka suka kama hanya, suna cikin tafiya Kiran Fauziyya ya shigo wayar Ruma.
"Bawa Umaimah wayar" ta fada bayan data amsa, seta miqa mata tana tabe baki dan yana yin da tayi mata magana ya sa ta tuna da fadan da sukayi shekaran jiya a makaranta akan zasuje sabon gari a saka musu farce da kitson qari duk na shirin bikin, tayi musu nasihar data saba Shine Fauziyyan ta zageta har tana kiranta bagidajiya batayi sanya ba itama ta rama danta fara gajiya da yanda suke maida ita kamar wata bolar su dan kawai tana da haquri shine ashe ita bata wuce ba.
"Umaimah muna Beejay fa, yanzu zaa fara yiwa Lims kwalliya" Fauziyyan ta fada bayan da Umaimah ta karbi wayar,
"Kai haba dai har yanzu shida saura fa"
"Dalla se waccen yar yawar taji kawai ku wuto nan akwai motocin da zasu dauke mu an kusa gama mata ma fa" Fauziyya tayi saurin kwabarta sukayi sallama.
Me Adaidaitan ta gayawa inda ze juya dasu, Ruma ta kalleta tace
"Ban gane ba ina kuma zamuje?"
"Kin fiya matsala wallahi toh saqo zan karba na manta ne se yanzu" ta fada tana tsuke fuska.
Agogon wayar Rumah ta kalla kamar tayi magana kuma tayi shiru, haka suka qarasa tafiyar babu me cewa wani qala har me Adaidaita ya sauke su a bakin gurin kwalliyar.
"Me kuma zamuyi anan kedai nasan ba kwalliya kike ba bare nace" Rumah ta sake fada bayan sun sauka
"Wallahi Rumah kin fiya matsala, bana gaya miki saqo zan karba ba.." Se tayi shiru ganin Nabila ta nufo su fuskar nan tasha kwalliya kamar Aljana se karairaya take dinki ta irin na jikin Umaimah amma sam be mata kyau ba saboda jikin ba iri daya ba, siririya ce ta gaske ga tsaho tana dashi se ta zama kamar wata bulala.
"Mu shiga ciki an kusa gama mata" ta fada tana kama hannun Rumah dan itace zatayi qorafi, haka suka shiga Reception din, abin takaici Amarya Halima na zaune ashe layi ma bezo kanta ba. Wai wata akeyiwa da an gama se ita.
Hira suka shigayi da daukar Hotuna, Umaimah na daga gefe kadan kadan take saka baki tana danna wayarta da tun suna hanya take ta qoqarin kiran Qasim amma ta kasa samun sa.
Tsaki taja ta kalli Rumah tace "Bani aron wayarki nayi kira please" dan duk cikin clique din nasu ita kadai ta yarda da ita take kuma iya sakata a sabgar samarinta hakan kuma ba shi yake hana idan abin ya motsa mata itama tayi mata horon da ta saba yi ba.
Bugu biyu Qasim ya daga kiran da tayi masa da wayar Rumasa'u, sallama yayi tsabar mamakin abinda yasa ita wayar ta ake ta ce mata not reachable amma gashi kira daya nan ta same shi ya hanata magana. Seda ya maimaita sallama sau uku kafin ta bude baki cikin fushin da yake taso mata tace
"Blocking layina kayi kenan Qasim tunda gashi na same ka da wata wayar"
Qasim kuwa yana jin muryarta daga daya bangaren 'Qit' ya kashe kiran, ta zare wayar daga kunnenta tana dubawa, kashewa yayi da gaske kai lallai yau akwai babban tashin hankali ashe.
Kusan sati kenan tun waccen ranar ya dena kiranta, idan ta kira shi farko farko ze amsa amma yanayin da ya koma yi mata magana a dake ba kamar yanda suka saba bane daga baya ma seta kira ta qaraci ringing di ta baze daga ba toh abin ya qaru jiya zuwa yau ma kwatakwata bata shiga shine yanzu ze qara mata da wannan wulaqancin ai kuwa ze san da ita yake zance.
Wayar ta mayarwa da Rumah ta qara harde qafa akan Kujera tana kadasu, a ranta ayyana irin tijarar da zata masa duk randa ya huce ya kawo kansa take. Ita badan ma tana son yazo ya mayar da ita gida ba ai ba zata kirashi ba amma shi kenan.
"Babu wasu iska sedai iskanci Laure kamar baki san wacece Umaimah ba. kuma da like batun tsayayye ai ba samarin me bata dasu ba, kullum zuwa suke amma mugun halinta da baqin kishi na ba gaira babu data dorawa kanta shi yake korar su. Ni damab na deba lissafa kawo mata kudin aure a wani abu, idan ba ji nayi an daurawa Umaimah aure ba shine kadai zan tabbatar da Miji ya tsaya dan a cikin sakanni tana iya tafka wautar da zata sa ace anfasa auranta.
Toh wane gantalalle ne tun be aureta ba zata fara dora masa ciwon kai ya tsaya?
nake gaya miki fa nan tayiwa Qasim cin mutunci ko kare baze ci ba wai kawai dan ya gaisa da abokiyar karatun ta shi kuma junior sace yarinyar tare sukayi secondary wallahi bakiji ba ina sallah a tsakar gidannan ina jiyota Allah Allah nake na idar na fita naci ubanta akayi sa'a yayansu yazo ya faffalla mata mari tayo ciki, ni nayi mamaki ma da har yau basu aiko sun karbi kudin auransu ba" Mama ta fada cikin matuqar takaici.
"Ashsha abu beyi kyau ba amma me yasa take haka ne, ya ilahi ke ace saurayinki baze kula wata mace ba toh inaga anyi aure kuma" Anty Laure ta fada cikin jimami tana juya hannu.
"Kema kya fada dai, shi yasa na dena raba takaici ta da kowa duk abinda tayi wanda ya gani ya gani shikenan fatana dai kullum shine ubangiji ya shiryeta dan dai wannan halin nata ba hali me kyau bane"
"Addu'ar dai kam ita ce amma dai Yaya karki qi ta tawa Allaha binciketa dai qila da sharrin iskar kin san fa daman baa ganewa se abu yayi tsamari baa fata sannan suke bayyana"
"Allah ya rufa asiri" kawai Mama tace mata ta janyo wata hirar dan ita duk wata sabga da zaace ta hada da malamai ba sonta take ba. Balle kuma Umaimah da sarai ta san babu abinda yake damunta, suma mantaqa sukayi amma ai tun tana qanqanuwarta haka take da bala'in kishi wani baze fita ba, idan kuwa abu ne idan bata dashi tofa sedai kowa ya rasa.
Tayi iya qoqarinta gurin canza mata wannan muguwar Dabi'a abin kuma yayi sauqi se a yanzu da shekarun hankali suka zo mata kuma abu ya ke sake ta'azzara, kuma a duk sanda Shedan ya buga mata gangar ta hau bata ji bata gani sedai fatan Allah ya shirya kawai.
UMAIMAH
Suna fita fuskar nan tata a cukule saboda maganar da Maman tayi suka shiga gidan Maman Nana, basu bata lokaci ba ta take mata rigar ta saka. Dinkine akayi mata na dibar Albarka ya fito mata da duk wata sura da take da ita domin kuwa Allah ya mata qira me kyau, tana da wani irin shape da ko mace ta kalleta seta qara kallo ta.
"Yanzu Umaimah da wannan Kayan zaki fita? Wai me yasa kike haka ne, baki san wannan abin da kike cin amanar iyayenki kike ba?
Ya za'ayi ki fito daga gidanku da shigar Mutunchi amma a waje a ganki da wata shiga ta daban? Wallahi ina jiye miki ranar da wani a gidan ku ze san abinda kikeyi nasan se kin gane kurenki wallahi kiyi ta biyewa su Nabila Sani su dai kin san a gida suka samu lasisin yin duk abinda sukeyi sedai su jira Kamun Allah" Rumah ta fada tana qarewa Umaimah dake daukar selfie Kallo. Kayan sun kamata matuqa ga kalar Atamfar data karbi fatarta dole ma ta fuzgi hankalinka ka kalleta.
"Sedai idan ke zakije ki fada, ni wuce muje ga me Napep din nan an samo" Umaimah ta fada ko a jikin ta tana zura wayarta a jaka daidai sanda Nana data aika ta taro musu dan sahu ta dawo, haka Rumah ta bita a baya cike da Takaicin halin qawar tata, badan gudun abinda kaje ka dawo ba wallahi seta fadawa Mama wannan muguwar dabi'ar data koya a gurin su Nabila.
Da sam ba haka take ba, da wuya kaga Umaimah ta saka kayan daya bayyana surar ta dan ba tarbiyyar gidan su bace amma shigar su Poly tunda ta hadu da sababbin qawaye irinsu Halima Mailafiya, Fannah Babagana, Nabila Sani se Fauziyya Kura, Izawaqa Mansur da ita Rumasa'u da daman tun Secondary suke tare . acikin su Ruma ce me sanyin Hali ba kuma tayin irin abinda sukeyi.
Nabila da Fauziyya sun fi kowa budadden ido a cikin su bayan Ruma sune mafiya kusanci da Umaimah kumasu suke qara dorata akan duk wani bigire mara kyau kasancewarta me saurin yarda da sakewa da mutane, gashi ita a rayuwarta tana jin maganar qawa kusan sama data kowa.
Tun tana dardar idan zaayi bikin qawar su aka fitar da Anko su suke kawo Style dinda zaayi na zamani na rashi mutunchi tace baza abarta ta saka a gida ba su suka kawo mata dabarar kin sakawar ta bari seta fito waje, dan a Auran Fannah ma dinki biyu aka mata. Wanda ta saka ta fito daga gida daban haka bayan sunje gurin bikin ta cire ta canza wani.
Rumasa'u na matuqar baqin ciki da wannan dabi'a tasu kuma duk ta yanda zata fahimtar da Umaimah cewar tsakanin ta dasu akwai Banbanci na tarbiyya da mutunchi taqi ta ji, sabo da shaquwar da take tsakaninsu tun yarinta ita tasaka ta kasa fita daga cikin group din nasu amma duk da haka kullum cikin yi musu Nasiha take bata damuwa da kyara da hantara da kiranta bagidajiya da sukeyi ita dai fatanta su dawo kan Hanya.
Haka suka kama hanya, suna cikin tafiya Kiran Fauziyya ya shigo wayar Ruma.
"Bawa Umaimah wayar" ta fada bayan data amsa, seta miqa mata tana tabe baki dan yana yin da tayi mata magana ya sa ta tuna da fadan da sukayi shekaran jiya a makaranta akan zasuje sabon gari a saka musu farce da kitson qari duk na shirin bikin, tayi musu nasihar data saba Shine Fauziyyan ta zageta har tana kiranta bagidajiya batayi sanya ba itama ta rama danta fara gajiya da yanda suke maida ita kamar wata bolar su dan kawai tana da haquri shine ashe ita bata wuce ba.
"Umaimah muna Beejay fa, yanzu zaa fara yiwa Lims kwalliya" Fauziyyan ta fada bayan da Umaimah ta karbi wayar,
"Kai haba dai har yanzu shida saura fa"
"Dalla se waccen yar yawar taji kawai ku wuto nan akwai motocin da zasu dauke mu an kusa gama mata ma fa" Fauziyya tayi saurin kwabarta sukayi sallama.
Me Adaidaitan ta gayawa inda ze juya dasu, Ruma ta kalleta tace
"Ban gane ba ina kuma zamuje?"
"Kin fiya matsala wallahi toh saqo zan karba na manta ne se yanzu" ta fada tana tsuke fuska.
Agogon wayar Rumah ta kalla kamar tayi magana kuma tayi shiru, haka suka qarasa tafiyar babu me cewa wani qala har me Adaidaita ya sauke su a bakin gurin kwalliyar.
"Me kuma zamuyi anan kedai nasan ba kwalliya kike ba bare nace" Rumah ta sake fada bayan sun sauka
"Wallahi Rumah kin fiya matsala, bana gaya miki saqo zan karba ba.." Se tayi shiru ganin Nabila ta nufo su fuskar nan tasha kwalliya kamar Aljana se karairaya take dinki ta irin na jikin Umaimah amma sam be mata kyau ba saboda jikin ba iri daya ba, siririya ce ta gaske ga tsaho tana dashi se ta zama kamar wata bulala.
"Mu shiga ciki an kusa gama mata" ta fada tana kama hannun Rumah dan itace zatayi qorafi, haka suka shiga Reception din, abin takaici Amarya Halima na zaune ashe layi ma bezo kanta ba. Wai wata akeyiwa da an gama se ita.
Hira suka shigayi da daukar Hotuna, Umaimah na daga gefe kadan kadan take saka baki tana danna wayarta da tun suna hanya take ta qoqarin kiran Qasim amma ta kasa samun sa.
Tsaki taja ta kalli Rumah tace "Bani aron wayarki nayi kira please" dan duk cikin clique din nasu ita kadai ta yarda da ita take kuma iya sakata a sabgar samarinta hakan kuma ba shi yake hana idan abin ya motsa mata itama tayi mata horon da ta saba yi ba.
Bugu biyu Qasim ya daga kiran da tayi masa da wayar Rumasa'u, sallama yayi tsabar mamakin abinda yasa ita wayar ta ake ta ce mata not reachable amma gashi kira daya nan ta same shi ya hanata magana. Seda ya maimaita sallama sau uku kafin ta bude baki cikin fushin da yake taso mata tace
"Blocking layina kayi kenan Qasim tunda gashi na same ka da wata wayar"
Qasim kuwa yana jin muryarta daga daya bangaren 'Qit' ya kashe kiran, ta zare wayar daga kunnenta tana dubawa, kashewa yayi da gaske kai lallai yau akwai babban tashin hankali ashe.
Kusan sati kenan tun waccen ranar ya dena kiranta, idan ta kira shi farko farko ze amsa amma yanayin da ya koma yi mata magana a dake ba kamar yanda suka saba bane daga baya ma seta kira ta qaraci ringing di ta baze daga ba toh abin ya qaru jiya zuwa yau ma kwatakwata bata shiga shine yanzu ze qara mata da wannan wulaqancin ai kuwa ze san da ita yake zance.
Wayar ta mayarwa da Rumah ta qara harde qafa akan Kujera tana kadasu, a ranta ayyana irin tijarar da zata masa duk randa ya huce ya kawo kansa take. Ita badan ma tana son yazo ya mayar da ita gida ba ai ba zata kirashi ba amma shi kenan.