Sashe 218
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Karma ki saka wannan a ranki Malika zasu karbi yarsu su hadata da sauran yan uwanta abu daya dai zan kira Hajiyar da kaina na roqi sassaucin janye mana ragowar yaran da sukayi, badan uwarsu ba kodan kasancewar su din jininmu ne su barsu su ringa zuwa muna ganinsu koda ace ba da kwana ba dan Kwanaki da akayi hutu Nuratu ta sanar mun ta kira Khalil din akan tana so ta dauki yaran suje gurinta yace Aa to sassaucin kadai da zan iya nema kenan ita kuma daman lokaci nake jira na zuba mata ido ne naga ko zata hankaltu tayi nadamar abinda ta aikata ta kuma dauki abinda ya sameta a matsayin darasi amma naga sam babu alamar hakan a tattare da ita, zan dauki mataki me tsauri akanta" Abbaya fada se Maman tayi shiru dan harga Allah ta shaqu da Iman din kuma zata so a bar yarinyar amma ya ta iya haka ta sanarwa da Anty nan suka shiga tattara mata duk wani abu da yake nata a gidan, kafin ranar Juma'ar sun hada mata komai tsaf yaran gidan duk sun shiga Alhinin tafiyar Iman din banda Uwarta da bata san dawar garin ba hidimarta kawai takeyi ba kuma ta damu da tambayar hada kayan da akeyi na menene ba.
Misalin qarfe hudu na yamma suka karbi baquncin Khalil da Humaira tareda yaransu. Cikin yanayin jin nauyi, kunya da kuma murnar ganinsu Anty da Maman suka tarbesu a falon Maman dan ko kusa basu kawo cewar da kansa ze zo karbar Iman din ba. Mama ta ringa satar kallon Khalil da yayi wata canzawa da Mamaki. Yayi kyau ya qara cika da girma Alamun nutsuwa da Jin dadi sun bayyana tare dashi kana kallon sa kasan bashida wata damuwa tsayin shekara daya kenan rabon da ta saka shi a idonta tun yana Asibiti dan gara Abba yakan je lokaci lokacin har gidan ya duba shi amma ita ta gaza yin hakan ta kance kunyar Hajiya Aisha ba zata barta iya sake hada ido da ita ba.
Anty ta kasa zama har seda ta cika musu gaba da duk nau'in kayan ciye ciye da suke dasu a gidan danma basu san da zuwansu ba. Cikin girma da mutuntawar daya saba yi musu ya gaida Mama da Antyn, Humaira dake zaune a qasa itama ta gaida su Babu yanda basuyi da ita ba akan ta hau kan kujera ta zauna taqi, Mama dai se kallon Dan Baby dake hannunta take yi gashi nan tamkar Balarabe saboda haske tamkar Uwarsa da itama ta canza ta zama babbar Mace. Anty ta miqa hannu ta karbi Aryaan tana cewa
"Kawo megidan na gani anya kuwa bazan saki na qarfen ba daman ba awo ba cefane wannan kuwa ko babu komai na kalli farar fata naji dadi".
Mu'ayyad ya tura bakin shagwaba dan shi take cewa na qarfen yana kuma jin dadin sunan se ya zura hannu a Aljihu ya ciro dari biyun da Khalil ya bashi kudin Juma'a ya miqawa Antyn yana cewa
"To gashi kiyi cefanen".
Dariya suka saka gaba daya ganin abinda yayin, Anty ta ci gaba da juya yaron tana yaba girma da wayonsa kamar ba dan wata uku ba Mama dai da Khalil surukuta sukeyi ita dai se murmushi take tana kallon rabon daya rabo Umaimah daga gidan Khalil a hannun Antyn shi kuma nauyinta ne ya hanashi sakewa se yanzu yake jin yayi kuskuren zuwa da kansa, daya sani Khalifa ya turo irin yanayin daya ganta ya tabbatar da har yanzu tana cikin radadin zafin abinda ya faru. Dakyar ya iya tambayar Abba suka sanar masa be dawo daga Kasuwa ba amma duk inda yake yana hanya dan ranar Juma'ar da wuri yake dawowa.
Sun zauna kusan Minti sha biyar Anty nata jan Humaira da hira ita dai se murmushi takeyi Khalil kuwa wayarsa yake dannawa Mama kuma tayi shiru tana ta tunani yaran dama sun fice gurin su Momynsu ganin bata dakinta yasa sukayi waje nan suka ci karo da Yasir Autan Anty da yana shigowa ya gansu ya buga tsallen murna ya kwashe su sukayi waje gurin Abokanan sa.
"Amma dai a nan zaku bar mana su suyi week end ko? Munata zuba ido anyi hutu kusan sau nawa ba'a kawo su ba" Anty ta sake katse musu zaman shirun da sukayi se yayi yaqe yace
"Za'a kawo su in sha Allah yanzun dai basu taho da kaya ba"
"Toh ai shikenan Allah ya kaimu toh, Amarya zo muje can kafin a dawo da yar taki wai kitso Sharifa ta tafi kaita tun dazu kinji su shiru" Anty ta sake fada tana miqewa dan su bawa Mama da Khalil din guri tasan ba zasu rasa abinda zasu tattauna ba Humaira tabi bayanta suka fita. A tsakar gida suka ci karo da Umaimah Anty ta kalleta ganin da Hijab a jikinta tace
"Ke kuma se ina"?
"Kati zan karbo gurin Ilu" ta bata amsa tana kallon Humaira da fuskarta tayi mata kamar ta santa a wani guri amma ta manta ina ne dan haka ta juya ta fice karbo katin.
Wata mota ta gani me kyan gaske a qofar gidan, ta matsa jikinta tana kallonta seta bude hanci saboda qamshin da taji yana fitowa daga ciki amkar na Khalil, tsaki tayi ta matsa a ranta tana cewa
"Hasashe ne kawai me ze kawo Khalil nan kuma idan yazo ai ita ze nema" ta qarasa Shagon Ilu dake jikin gidan da yake kallon nasu ta karbi katin, fasa komawa gida tayi ta shige gidan Maman Nana. Babu inda take zuwa kullum tana gida idanta samuta fito siyan kati nema take leqawa gidan Maman Nana dukda babu wanda yace karta fita koda yake wa yake ta sabgarta ma balle ya sakata ko ya hanata? A canta shantake suka shiga hirar duniya, ganin biyar tayi yasa ta miqr tana mata sallama dan tasan Abbana dab da dawowa gida yanzu tana fitowa daga gidan Maman Nanan idonta yayi kyakykyawan gani. Khalil ta gani wanda badan sanin da tayi masa ha zata iya cewa me kama dashi ne saboda yanda ya canza yayi qiba, yana tsaye ya budewa yarinyar data gani tareda Anty yanzu qofar mota ta shiga ya ranqwafa ciki yana mata magana tana iya hango tsadaddan murmushin da yake kan fuskarsa.
KHALIL
Bayan fitar su Anty a hankali Mama ta bude baki tana kallonsa tace
"Khalil ina qara baka haquri akan abunda ya faru.."
"Haba Mama ni ya kamata na baku haquri na kuma nemi yafiyarku bisa cin fuskar danayi muku na saki yarku a gabanku amma Allah ya sani ba'a son raina ba amma haka Allah ya tsara, ina fatan hakan ya zame mana Alkhairi a rayuwar mu gaba daya" Khalil yayi saurin Katse Maman, kasa sake ce masa komai tayi a ranta tana sake takaicin rasa Miji Kamar Khalil da Umaimah tayi amma tana nan ko a jikinta, zuciyarta da kwakwalwarta suna gaya mata qaryar ze dawo gareta wanda a yanzu ko Makaho ya shafashi yasan ya samu canjin rayuwa ya samu nutsuwa babu yanda za'ayi yana sane ya sake maida kansa cikin ramin daya fito dakyar.
Zaman shirun suka ci gaba dayi, shigowar Sharifa da sauran yaran ya katse musu shirun ta miqa Masa Iman dake ta yiwa yan uwanta dariya tamkar ta sansu. Fuskarta data sha kitso ya tsurawa ido yana sake ganin ainihin kamanninta da Umaimah tamkar an tsaga kara, besan irin kallon da yake mata ba seda yaji Mama tana cewa
"Kana mamakin kamanninta da Umaimah ko? Kowa ya ganta se yace kamar har tayi yawa" tana gama fada ta miqe tana sake cewa
"Bari nayiwa Saratu magana tasa a fitar da kayan nata ko zaku jira Abban naku ya dawo kafin ku wuce?"
Kansa ya shafa yace
"Zan samu lokaci in sha Allah na dawo na gaishe shi"
"Shikenan to bari nayi mata magana" ta fada ta fice ta barshi da Iman dan sauran yaran suna rakota daman suka juya sabgarsu. Rungume yarinyar yayi a jikinsa yana jin wani yanayi na taso masa. Salman ne ya shiga da Sallama, ya bashi hannu suka gaisa yana tambayarsa karatu da suke gangara dan Jarabawar qarshe sukeyi. Muqullin motar sa ya bashi saboda yace za'a saka kayan Iman ya gaya masa ya fito da kayan Booth din ya shigo dasu sey miqe da yarinyar a Jikinsa ya fito tsakar gidan, yana tsaye yaran suka fita da Akwatunan Iman harda Mota da Kekenta da sauran tarkacen kayan wasan da yake siya ana kawo mata seda suka gama saka kayan tsaf kafin Salmanya dawo masa da Key din, shiya shiga dakin Anty ya kira Humaira suka fito tareda Anty da seda ta sakata ta sake dan dole sukayi hira. Dakin Mama ta koma tayi mata sallama ta bata Leda Babba tana cewa
"Gashi babu yawa bamu samu munzo barka ba Allah ya raya yayi Albarka sannan ina fatan zaki qara haquri akan wanda kikeyi sabgar yara se an kai zuciya nesa musamman yanzu kin samu qarin wata Allah ya taya miki ya baki lada"
Misalin qarfe hudu na yamma suka karbi baquncin Khalil da Humaira tareda yaransu. Cikin yanayin jin nauyi, kunya da kuma murnar ganinsu Anty da Maman suka tarbesu a falon Maman dan ko kusa basu kawo cewar da kansa ze zo karbar Iman din ba. Mama ta ringa satar kallon Khalil da yayi wata canzawa da Mamaki. Yayi kyau ya qara cika da girma Alamun nutsuwa da Jin dadi sun bayyana tare dashi kana kallon sa kasan bashida wata damuwa tsayin shekara daya kenan rabon da ta saka shi a idonta tun yana Asibiti dan gara Abba yakan je lokaci lokacin har gidan ya duba shi amma ita ta gaza yin hakan ta kance kunyar Hajiya Aisha ba zata barta iya sake hada ido da ita ba.
Anty ta kasa zama har seda ta cika musu gaba da duk nau'in kayan ciye ciye da suke dasu a gidan danma basu san da zuwansu ba. Cikin girma da mutuntawar daya saba yi musu ya gaida Mama da Antyn, Humaira dake zaune a qasa itama ta gaida su Babu yanda basuyi da ita ba akan ta hau kan kujera ta zauna taqi, Mama dai se kallon Dan Baby dake hannunta take yi gashi nan tamkar Balarabe saboda haske tamkar Uwarsa da itama ta canza ta zama babbar Mace. Anty ta miqa hannu ta karbi Aryaan tana cewa
"Kawo megidan na gani anya kuwa bazan saki na qarfen ba daman ba awo ba cefane wannan kuwa ko babu komai na kalli farar fata naji dadi".
Mu'ayyad ya tura bakin shagwaba dan shi take cewa na qarfen yana kuma jin dadin sunan se ya zura hannu a Aljihu ya ciro dari biyun da Khalil ya bashi kudin Juma'a ya miqawa Antyn yana cewa
"To gashi kiyi cefanen".
Dariya suka saka gaba daya ganin abinda yayin, Anty ta ci gaba da juya yaron tana yaba girma da wayonsa kamar ba dan wata uku ba Mama dai da Khalil surukuta sukeyi ita dai se murmushi take tana kallon rabon daya rabo Umaimah daga gidan Khalil a hannun Antyn shi kuma nauyinta ne ya hanashi sakewa se yanzu yake jin yayi kuskuren zuwa da kansa, daya sani Khalifa ya turo irin yanayin daya ganta ya tabbatar da har yanzu tana cikin radadin zafin abinda ya faru. Dakyar ya iya tambayar Abba suka sanar masa be dawo daga Kasuwa ba amma duk inda yake yana hanya dan ranar Juma'ar da wuri yake dawowa.
Sun zauna kusan Minti sha biyar Anty nata jan Humaira da hira ita dai se murmushi takeyi Khalil kuwa wayarsa yake dannawa Mama kuma tayi shiru tana ta tunani yaran dama sun fice gurin su Momynsu ganin bata dakinta yasa sukayi waje nan suka ci karo da Yasir Autan Anty da yana shigowa ya gansu ya buga tsallen murna ya kwashe su sukayi waje gurin Abokanan sa.
"Amma dai a nan zaku bar mana su suyi week end ko? Munata zuba ido anyi hutu kusan sau nawa ba'a kawo su ba" Anty ta sake katse musu zaman shirun da sukayi se yayi yaqe yace
"Za'a kawo su in sha Allah yanzun dai basu taho da kaya ba"
"Toh ai shikenan Allah ya kaimu toh, Amarya zo muje can kafin a dawo da yar taki wai kitso Sharifa ta tafi kaita tun dazu kinji su shiru" Anty ta sake fada tana miqewa dan su bawa Mama da Khalil din guri tasan ba zasu rasa abinda zasu tattauna ba Humaira tabi bayanta suka fita. A tsakar gida suka ci karo da Umaimah Anty ta kalleta ganin da Hijab a jikinta tace
"Ke kuma se ina"?
"Kati zan karbo gurin Ilu" ta bata amsa tana kallon Humaira da fuskarta tayi mata kamar ta santa a wani guri amma ta manta ina ne dan haka ta juya ta fice karbo katin.
Wata mota ta gani me kyan gaske a qofar gidan, ta matsa jikinta tana kallonta seta bude hanci saboda qamshin da taji yana fitowa daga ciki amkar na Khalil, tsaki tayi ta matsa a ranta tana cewa
"Hasashe ne kawai me ze kawo Khalil nan kuma idan yazo ai ita ze nema" ta qarasa Shagon Ilu dake jikin gidan da yake kallon nasu ta karbi katin, fasa komawa gida tayi ta shige gidan Maman Nana. Babu inda take zuwa kullum tana gida idanta samuta fito siyan kati nema take leqawa gidan Maman Nana dukda babu wanda yace karta fita koda yake wa yake ta sabgarta ma balle ya sakata ko ya hanata? A canta shantake suka shiga hirar duniya, ganin biyar tayi yasa ta miqr tana mata sallama dan tasan Abbana dab da dawowa gida yanzu tana fitowa daga gidan Maman Nanan idonta yayi kyakykyawan gani. Khalil ta gani wanda badan sanin da tayi masa ha zata iya cewa me kama dashi ne saboda yanda ya canza yayi qiba, yana tsaye ya budewa yarinyar data gani tareda Anty yanzu qofar mota ta shiga ya ranqwafa ciki yana mata magana tana iya hango tsadaddan murmushin da yake kan fuskarsa.
KHALIL
Bayan fitar su Anty a hankali Mama ta bude baki tana kallonsa tace
"Khalil ina qara baka haquri akan abunda ya faru.."
"Haba Mama ni ya kamata na baku haquri na kuma nemi yafiyarku bisa cin fuskar danayi muku na saki yarku a gabanku amma Allah ya sani ba'a son raina ba amma haka Allah ya tsara, ina fatan hakan ya zame mana Alkhairi a rayuwar mu gaba daya" Khalil yayi saurin Katse Maman, kasa sake ce masa komai tayi a ranta tana sake takaicin rasa Miji Kamar Khalil da Umaimah tayi amma tana nan ko a jikinta, zuciyarta da kwakwalwarta suna gaya mata qaryar ze dawo gareta wanda a yanzu ko Makaho ya shafashi yasan ya samu canjin rayuwa ya samu nutsuwa babu yanda za'ayi yana sane ya sake maida kansa cikin ramin daya fito dakyar.
Zaman shirun suka ci gaba dayi, shigowar Sharifa da sauran yaran ya katse musu shirun ta miqa Masa Iman dake ta yiwa yan uwanta dariya tamkar ta sansu. Fuskarta data sha kitso ya tsurawa ido yana sake ganin ainihin kamanninta da Umaimah tamkar an tsaga kara, besan irin kallon da yake mata ba seda yaji Mama tana cewa
"Kana mamakin kamanninta da Umaimah ko? Kowa ya ganta se yace kamar har tayi yawa" tana gama fada ta miqe tana sake cewa
"Bari nayiwa Saratu magana tasa a fitar da kayan nata ko zaku jira Abban naku ya dawo kafin ku wuce?"
Kansa ya shafa yace
"Zan samu lokaci in sha Allah na dawo na gaishe shi"
"Shikenan to bari nayi mata magana" ta fada ta fice ta barshi da Iman dan sauran yaran suna rakota daman suka juya sabgarsu. Rungume yarinyar yayi a jikinsa yana jin wani yanayi na taso masa. Salman ne ya shiga da Sallama, ya bashi hannu suka gaisa yana tambayarsa karatu da suke gangara dan Jarabawar qarshe sukeyi. Muqullin motar sa ya bashi saboda yace za'a saka kayan Iman ya gaya masa ya fito da kayan Booth din ya shigo dasu sey miqe da yarinyar a Jikinsa ya fito tsakar gidan, yana tsaye yaran suka fita da Akwatunan Iman harda Mota da Kekenta da sauran tarkacen kayan wasan da yake siya ana kawo mata seda suka gama saka kayan tsaf kafin Salmanya dawo masa da Key din, shiya shiga dakin Anty ya kira Humaira suka fito tareda Anty da seda ta sakata ta sake dan dole sukayi hira. Dakin Mama ta koma tayi mata sallama ta bata Leda Babba tana cewa
"Gashi babu yawa bamu samu munzo barka ba Allah ya raya yayi Albarka sannan ina fatan zaki qara haquri akan wanda kikeyi sabgar yara se an kai zuciya nesa musamman yanzu kin samu qarin wata Allah ya taya miki ya baki lada"