Sashe 183
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh ki jirani na shirya mu tafi tare ai dai kema kinsan ba'a fadamun za'ayi wani taro ba kuma taron menene ma akeyi?"
"Kiyi zamanki mun gama abinda zamuyi tun kafin na fito, daman magana ce akan Yayan Yah Aminu Anty Mami ta samu Miji zatayi aure shine ta ce zata dauki yaran Mijin yace ze riqe Mata"
"Agolanci? Allah ya rufa asiri yayan mu suyi Agolanci suje wani gida cin Arziqi a ringayi musu gani gani ana musu gori, taje can tayi auranta tsabar jaraba ko shekara biyu beyi da mutuwa ba zatace zata wani yi aure kamar daman jira takeyi ya mutun" Umaimah ta shiga kumfar baki, tsaki Nuratu taja ta taka mota tana ce mata
"Idan kinga dama ki kirasu ki basu haquri ki kuma gyara alaqarki da kowa dan ranar Naka dole se Naka, duk tarin qawayen da kike ganin sun fiye miki mu akwai gabat da za'azo da dole mudin dai mu zamu miki rana" daga haka ta daga Sammani ya bude mata Get ta fice daga gidan a fuska zaka dauka babu abinda ua faru amma cikin ranta kalaman Umaimah na nan suna nuqurqusarta.
Umaimah kuwa Nuratu na fita ta juya har ta kai bakin qofa kuma ta fasa shiga ta dawo nan Compound din taja kujera ta zauna bayan ta cewa Ruqayya ta kawo mata wayarta. Tafi qarfin awa daya a gurin a zaune, jira takeyi taga jama'ar da suka taru a bangaren Hajiyar sun fara fitowa amma shiru gashi tana tsoron ta shiga dan bata san su nawa bane a gurin haka ta gaji da zaman jira ta koma ciki suka ci gaba da Chatting da Safina dakw sake tausarta akan ta danne zuciyarta ta jira taga aikin Malam. Seda tayi sallar Magriba kafin tayi wanka ta saka Ruqayya ta shirya yara suka tafi gidansu.
Yanda Mama ta karbeta ya sa ta sake shan jinin jikin damanga Yah Naziyya na gidan itama gaisawa kadai sukayi ta fita a sabgarta, bata wani jima sosai ba suka tafi bayan Abba ya dawo sun gaisa shidai faran faran ya tarbeta yana tambayarta Khalil yaja jikokinsa yana musu wasa da zasu tafi ya basu kudi ita kuma ya sake nanata mata karatun da kullum suka hadu se yayi mata na ta nutsu ta zauna da Mijinta lafiya ya rufe da saka mata Albarka. Duk setaji babu dadi yanda Maman tayi mata, ita bata ga fushin me takeyi ba kawai sunje sun taru an hado da abunda tayi da wanda ba tayi ba sun gayawa Maman ita kuma ta hau ta zauna suda Allah ita basu san abinda yake a gabanta ba za'a qara mata wata damuwar.
KHALIL
Tun yana office Jalilah ta kirashi akan ta qarasa duk siyayar kayayyaki shi kawai take jira yazo ya gani, be samu ya shigo da wuri ba dan bayan ya bar gurin Humairah seda ya sake biyawa wani gurin dan haka be tarar da Jalilan ba se ubannin akwatuna na garari daya tarar a bangaren Hajiya guda goma sha biyu da sunan kayan lefen Humaira.
Buda baki yayi kawai yana kallon kayan, Hajiya tace
"Ai Rigimar Jalilah babu me iya mata, nan fa kudaden jama'a babu a gun wanda bata karba ba ta harhada ta siyo kayan nan, ina jinsu dazu lissafin bashin Miliyan kusan uku suke maka wai harda Sarqa zasu siya a saka a ciki nace musu sun baka ajiyar kudin ne ko Yaya?
Ga Lafayu can guda biyar Hajiya yagana ta aiko dasu magana kamar wutar daji labari ya watsu dangi wai zakayi aure ai da da wuri ka dawo gidan nan babu masaka tsinke yanda kasan yau ake bikin, nidai addu'a na ringayi su tafi salin alin ba tareda matarka tayi wani abun ba kuma Allah ya amsa mun har suka watse babu abinda akayi kuma tana gidan, ni yanzu da safe ma zuwa zasuyi su kwashe kayan nan kafin wani tsautsayin ya afka musu tun baka biya kudin ba".
Kansa na qasa yake sauraron Hajiyar dan ya kasa hada ido da ita. Kunyarta yake ji ace matarsa ta zageta amma ya gagara daukar mataki akai, a hankali ya daga kansa ya kalli gefe yace
"Daman itama tace zata dawo ta kwashe goben, munyi magana da Baba Abu Dazu yace ranar Juma'a zamu tafi can Jalingon, to ban sani ba ko ze yuwu ace an tafi da kayan ko kuma se daga baya dai wannan se kunyi magana dashi kun yanke yanda za'ayi"
"Eh nima ya kirani da yamma, da na gaya masa ga Lefe ma har an hada yace babu damuwa ze tuntubesu yaji, idan cam za'a kai gara a hada ayi tafiya daya idan kuma nan gidan Hauwa za'a kai kaga za'a iya bari se lokaci ya matso tukunna. Nadai yi musu zancen kayan ita Umaiman Jalilah tayi tsalle tace ba za'ayi ba to ni babu ruwana ba kuma zan goyi bayan rashin Adalci ba, idan kudi zaka bata ta siyi abinda take so to idan kuma kayan zaka mata toh gasu nan ka duba abubuwan da suke ciki ka siya mata itama" Hajiyan ta sake fada se ya daga kai ya kalleta ganin itama shi take kallo yasa ya mayar da kansa qasa cikin taushin murya yace
"Hajiya, kiyi haquri da abinda ya faru jiya dan Allah"
"Haqurin me kake bani Babana ni baka yimun komai ba, idan ma dan abinda Matarka tayi ne ni ya wuce a gurina na kuma yafe mata kaima kuma ina so kaci gaba da haquri dan daman ai kasan abinda ka dakko dole ka shirya karbar duk wani sakamako daya biyo ba. Kawai kaci gaba da Addu'a ka kuma ci gaba da lallabata". Shiru yayi yana sauraron Hajiyar, idan ya tuna zagin da Umaiman tayi mata zuciyarsa bugawa takeyi amma ya gagara daukar mataki me yasa?
Abinci ya buqaci Habiba ta kawo masa yaga Taliya ce yace ta mayar se ya miqe yayiwa Hajiya sallama ya fita. Kai tsaye ya wuce bangarensu, tunda ya shigo bega motarta ba daman yasan bata nan, seda yayi wanka ya canza kaya kafin ya sakko qasan lokacin har Ruqayya ta jera Abinci, Sakwara tayi musu da Miyar Agushi, se farfesun naman rago yana bude kwanon maganar Jalilah ta fado masa da tace jiya Umaimah ta dafa nama da magani ta bawa Hajiya taci se ya maida kwanon gefe ya zuba Sakwarar yayi bismillah tafi qafa dari kafin yayi shahada ya faraci.
A falon Umaimah ta tarar dashi yana cin abinci, shaf ta manta da saqon da ta taho dasu dazu da bazata fita ba har se an gama abincin ta zuba masa amma akwai gobe. Da ido ya bita ganin ta dauke kai ta kalli wani guri daban yaran kuma gurin sa suka tafi da gudu. Khalil ya sauke ajiyar zuciya yaci gaba da cin Abincinsa tareda yaran. Seda suka qare Mu'ayyad ya zaro kudin da Abba ya basu ya bawa Khalil din yace ya ajiye musu, se sannan ya san daga inda suke, yana nan zauneda yaran suna kallo har qarfe tara kafin yace suje su kwanta. Dakin da Umaimah take ya shiga da sallama bayan da yayi knocking ta bada Umarnin a shiga. Tana zaune gaban mudubi tana shafa mai da alama wanka tayi gashinta data wanke ya manne a fatar wuyanta zuwa bayanta, kallo daya yayi mata tsigar jikinsa ta tashi wani abu daya dade beji akan mace ba ya taso masa seya qarasa bayanta a hankali ya dora hannayensa kan kafadarta yana matsawa.
Umaimah, yanda yayi matan seda yasa tsikar jikinta itama suka zuba amma a fili bata nuna ta karbi saqon nasa ba sema qara tamke fuska da tayi ta ture hannun nasa daga jikinta ba tareda tayi magana ba ta miqe, rigar baccinta data ajiye ta dauka ta saka fuskar nan kamar Kunu ta haye gado ba tareda ta kalli inda yake tsaye yana binta da kallo ba. Seda ta kwanta taja bargo ta rufe qafarta zuwa cikinta kafin yabita shima ya shiga qoqarin kwanciya a bayanta.
"Meye haka Malam zaka shigowa mutane daki harda hawar musu gado?" Ta fada a fusace tana tashi zaune, da yasan yanda take ji a zuciyarta da be kuskura yaje kusa da ita ba dan tsaf idan da makamo kusa zata iya qaddamar masa yanzu.
Khalil kuwa dan murmushi yayi jin abinda ta fada seya sauke qafafunsa qasa, taja wani dogon tsaki kafin ta sake kwanciya ta juya masa baya tana qunquni.
"Umaimah" ya kira sunanta, bata amsa ba shima be saka ran zata amsa din ba dan haka yaci gaba da cewa
"Ina so duk abinda zakiyi ya tsaya iya kaina nida ke karki sake sako Mahaifiyata a ciki ballantana har ki iya bude baki ki zageta, ban taba zaton ko kallon banza kika ga wani yayiwa Hajiya zaki yi shiru ba se gashu keda kanki baki ji nauyin komai ba kika zageta"
"Khalil, nace Hajiya munafuka ce qarya nayi ko batayi munafuncin ba? Ta nunamun tana sona ta jani a jiki har ta fifitani akanka sata haifa she duk na yaudara ne rana daya ta nemo maka auran yar Qawarta idan ban kirata da Munafuka ba Annamimiya kake so nace mata kome?" Umaimah data tashi zaune ta fada tana kallonsa ido cikin ido babu tsoro ko shakkar komai a fuskarta.
Wani yawu me daci ya hadiye ya rufe idonsa da lokaci daya ya rikida yayi ja saboda bacin ran da kalamanta suka dira masa, yana jinta taci gaba da cewa
"Ai na gaya maka kaida zaman lafiya har abada a gidan nan Khalil ba dai aure kace zakayi ba toh mu zuba mu gani" taja wani tsaki kamar zata katse harshenta kafin ta yunqura ta shige bandaki ta barshi a gurin.
"Kiyi zamanki mun gama abinda zamuyi tun kafin na fito, daman magana ce akan Yayan Yah Aminu Anty Mami ta samu Miji zatayi aure shine ta ce zata dauki yaran Mijin yace ze riqe Mata"
"Agolanci? Allah ya rufa asiri yayan mu suyi Agolanci suje wani gida cin Arziqi a ringayi musu gani gani ana musu gori, taje can tayi auranta tsabar jaraba ko shekara biyu beyi da mutuwa ba zatace zata wani yi aure kamar daman jira takeyi ya mutun" Umaimah ta shiga kumfar baki, tsaki Nuratu taja ta taka mota tana ce mata
"Idan kinga dama ki kirasu ki basu haquri ki kuma gyara alaqarki da kowa dan ranar Naka dole se Naka, duk tarin qawayen da kike ganin sun fiye miki mu akwai gabat da za'azo da dole mudin dai mu zamu miki rana" daga haka ta daga Sammani ya bude mata Get ta fice daga gidan a fuska zaka dauka babu abinda ua faru amma cikin ranta kalaman Umaimah na nan suna nuqurqusarta.
Umaimah kuwa Nuratu na fita ta juya har ta kai bakin qofa kuma ta fasa shiga ta dawo nan Compound din taja kujera ta zauna bayan ta cewa Ruqayya ta kawo mata wayarta. Tafi qarfin awa daya a gurin a zaune, jira takeyi taga jama'ar da suka taru a bangaren Hajiyar sun fara fitowa amma shiru gashi tana tsoron ta shiga dan bata san su nawa bane a gurin haka ta gaji da zaman jira ta koma ciki suka ci gaba da Chatting da Safina dakw sake tausarta akan ta danne zuciyarta ta jira taga aikin Malam. Seda tayi sallar Magriba kafin tayi wanka ta saka Ruqayya ta shirya yara suka tafi gidansu.
Yanda Mama ta karbeta ya sa ta sake shan jinin jikin damanga Yah Naziyya na gidan itama gaisawa kadai sukayi ta fita a sabgarta, bata wani jima sosai ba suka tafi bayan Abba ya dawo sun gaisa shidai faran faran ya tarbeta yana tambayarta Khalil yaja jikokinsa yana musu wasa da zasu tafi ya basu kudi ita kuma ya sake nanata mata karatun da kullum suka hadu se yayi mata na ta nutsu ta zauna da Mijinta lafiya ya rufe da saka mata Albarka. Duk setaji babu dadi yanda Maman tayi mata, ita bata ga fushin me takeyi ba kawai sunje sun taru an hado da abunda tayi da wanda ba tayi ba sun gayawa Maman ita kuma ta hau ta zauna suda Allah ita basu san abinda yake a gabanta ba za'a qara mata wata damuwar.
KHALIL
Tun yana office Jalilah ta kirashi akan ta qarasa duk siyayar kayayyaki shi kawai take jira yazo ya gani, be samu ya shigo da wuri ba dan bayan ya bar gurin Humairah seda ya sake biyawa wani gurin dan haka be tarar da Jalilan ba se ubannin akwatuna na garari daya tarar a bangaren Hajiya guda goma sha biyu da sunan kayan lefen Humaira.
Buda baki yayi kawai yana kallon kayan, Hajiya tace
"Ai Rigimar Jalilah babu me iya mata, nan fa kudaden jama'a babu a gun wanda bata karba ba ta harhada ta siyo kayan nan, ina jinsu dazu lissafin bashin Miliyan kusan uku suke maka wai harda Sarqa zasu siya a saka a ciki nace musu sun baka ajiyar kudin ne ko Yaya?
Ga Lafayu can guda biyar Hajiya yagana ta aiko dasu magana kamar wutar daji labari ya watsu dangi wai zakayi aure ai da da wuri ka dawo gidan nan babu masaka tsinke yanda kasan yau ake bikin, nidai addu'a na ringayi su tafi salin alin ba tareda matarka tayi wani abun ba kuma Allah ya amsa mun har suka watse babu abinda akayi kuma tana gidan, ni yanzu da safe ma zuwa zasuyi su kwashe kayan nan kafin wani tsautsayin ya afka musu tun baka biya kudin ba".
Kansa na qasa yake sauraron Hajiyar dan ya kasa hada ido da ita. Kunyarta yake ji ace matarsa ta zageta amma ya gagara daukar mataki akai, a hankali ya daga kansa ya kalli gefe yace
"Daman itama tace zata dawo ta kwashe goben, munyi magana da Baba Abu Dazu yace ranar Juma'a zamu tafi can Jalingon, to ban sani ba ko ze yuwu ace an tafi da kayan ko kuma se daga baya dai wannan se kunyi magana dashi kun yanke yanda za'ayi"
"Eh nima ya kirani da yamma, da na gaya masa ga Lefe ma har an hada yace babu damuwa ze tuntubesu yaji, idan cam za'a kai gara a hada ayi tafiya daya idan kuma nan gidan Hauwa za'a kai kaga za'a iya bari se lokaci ya matso tukunna. Nadai yi musu zancen kayan ita Umaiman Jalilah tayi tsalle tace ba za'ayi ba to ni babu ruwana ba kuma zan goyi bayan rashin Adalci ba, idan kudi zaka bata ta siyi abinda take so to idan kuma kayan zaka mata toh gasu nan ka duba abubuwan da suke ciki ka siya mata itama" Hajiyan ta sake fada se ya daga kai ya kalleta ganin itama shi take kallo yasa ya mayar da kansa qasa cikin taushin murya yace
"Hajiya, kiyi haquri da abinda ya faru jiya dan Allah"
"Haqurin me kake bani Babana ni baka yimun komai ba, idan ma dan abinda Matarka tayi ne ni ya wuce a gurina na kuma yafe mata kaima kuma ina so kaci gaba da haquri dan daman ai kasan abinda ka dakko dole ka shirya karbar duk wani sakamako daya biyo ba. Kawai kaci gaba da Addu'a ka kuma ci gaba da lallabata". Shiru yayi yana sauraron Hajiyar, idan ya tuna zagin da Umaiman tayi mata zuciyarsa bugawa takeyi amma ya gagara daukar mataki me yasa?
Abinci ya buqaci Habiba ta kawo masa yaga Taliya ce yace ta mayar se ya miqe yayiwa Hajiya sallama ya fita. Kai tsaye ya wuce bangarensu, tunda ya shigo bega motarta ba daman yasan bata nan, seda yayi wanka ya canza kaya kafin ya sakko qasan lokacin har Ruqayya ta jera Abinci, Sakwara tayi musu da Miyar Agushi, se farfesun naman rago yana bude kwanon maganar Jalilah ta fado masa da tace jiya Umaimah ta dafa nama da magani ta bawa Hajiya taci se ya maida kwanon gefe ya zuba Sakwarar yayi bismillah tafi qafa dari kafin yayi shahada ya faraci.
A falon Umaimah ta tarar dashi yana cin abinci, shaf ta manta da saqon da ta taho dasu dazu da bazata fita ba har se an gama abincin ta zuba masa amma akwai gobe. Da ido ya bita ganin ta dauke kai ta kalli wani guri daban yaran kuma gurin sa suka tafi da gudu. Khalil ya sauke ajiyar zuciya yaci gaba da cin Abincinsa tareda yaran. Seda suka qare Mu'ayyad ya zaro kudin da Abba ya basu ya bawa Khalil din yace ya ajiye musu, se sannan ya san daga inda suke, yana nan zauneda yaran suna kallo har qarfe tara kafin yace suje su kwanta. Dakin da Umaimah take ya shiga da sallama bayan da yayi knocking ta bada Umarnin a shiga. Tana zaune gaban mudubi tana shafa mai da alama wanka tayi gashinta data wanke ya manne a fatar wuyanta zuwa bayanta, kallo daya yayi mata tsigar jikinsa ta tashi wani abu daya dade beji akan mace ba ya taso masa seya qarasa bayanta a hankali ya dora hannayensa kan kafadarta yana matsawa.
Umaimah, yanda yayi matan seda yasa tsikar jikinta itama suka zuba amma a fili bata nuna ta karbi saqon nasa ba sema qara tamke fuska da tayi ta ture hannun nasa daga jikinta ba tareda tayi magana ba ta miqe, rigar baccinta data ajiye ta dauka ta saka fuskar nan kamar Kunu ta haye gado ba tareda ta kalli inda yake tsaye yana binta da kallo ba. Seda ta kwanta taja bargo ta rufe qafarta zuwa cikinta kafin yabita shima ya shiga qoqarin kwanciya a bayanta.
"Meye haka Malam zaka shigowa mutane daki harda hawar musu gado?" Ta fada a fusace tana tashi zaune, da yasan yanda take ji a zuciyarta da be kuskura yaje kusa da ita ba dan tsaf idan da makamo kusa zata iya qaddamar masa yanzu.
Khalil kuwa dan murmushi yayi jin abinda ta fada seya sauke qafafunsa qasa, taja wani dogon tsaki kafin ta sake kwanciya ta juya masa baya tana qunquni.
"Umaimah" ya kira sunanta, bata amsa ba shima be saka ran zata amsa din ba dan haka yaci gaba da cewa
"Ina so duk abinda zakiyi ya tsaya iya kaina nida ke karki sake sako Mahaifiyata a ciki ballantana har ki iya bude baki ki zageta, ban taba zaton ko kallon banza kika ga wani yayiwa Hajiya zaki yi shiru ba se gashu keda kanki baki ji nauyin komai ba kika zageta"
"Khalil, nace Hajiya munafuka ce qarya nayi ko batayi munafuncin ba? Ta nunamun tana sona ta jani a jiki har ta fifitani akanka sata haifa she duk na yaudara ne rana daya ta nemo maka auran yar Qawarta idan ban kirata da Munafuka ba Annamimiya kake so nace mata kome?" Umaimah data tashi zaune ta fada tana kallonsa ido cikin ido babu tsoro ko shakkar komai a fuskarta.
Wani yawu me daci ya hadiye ya rufe idonsa da lokaci daya ya rikida yayi ja saboda bacin ran da kalamanta suka dira masa, yana jinta taci gaba da cewa
"Ai na gaya maka kaida zaman lafiya har abada a gidan nan Khalil ba dai aure kace zakayi ba toh mu zuba mu gani" taja wani tsaki kamar zata katse harshenta kafin ta yunqura ta shige bandaki ta barshi a gurin.