Sashe 163
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nine Ibrahim Khalil, ko akwai wanda kike tsammanin gani daman bayan ni?" Ya sakw tambayarta yana dage mata gira. Yanda tayi da fuskarta seda ya bashi dariya harya kasa hadiyeta. Yanda kasan wanda ya gayawa wani mugun Abu haka ta miqr da sauri tayi cikin gida be tsayar da ita ba shima ya bita da dariya kawai, komai aka hada da yaro dai se an ga quruciya. Wayarsa ya dauka ya shiga kiran Layin Mansur.
"Yaya Mansur ina wuni ko nace barka da dare dan nasan ku daren ku ya shiga" Khalil ya fada bayan daya amsa sallamar da Mansur yayi masa. Daga daya bangaren Mansur yace
"Da alama shaye shaye ka fara ko idan ba haka ba ni zakace wa Yaya saboda Dan iska ne kai? Ni ba surukinka ba ba komai ba kace mun wani Yaya bayan ko a shekaru aka qirga ka girme balle kace hankali ka qaro yau zaka bani girma".
Dariya Khalil ya fashe da ita shima Mansur din na tayashi kafin yace
"Ka sani ko zaka zama surukin nawa ai abun na Allah ne"
"Wa Allah ya tsareni da zama surukinka dadai wannan matar a gidan ka ko yan uwan maqotan mu da na sani bazan bari su baka mata ba" Mansur ya sake fada se Khalil yayi murmushi yace
"Toh Yaya Mansur ya zanyi dakai tunda haka kace"
"Ka gama iskancinka ka fada mun abinda yasa ka kirani Malam" cewar Mansur, se Khalil yayi saurin cewa
"Zan sake kiranka zansu ina tsakiyar wani Important deal ne, kaidai da yayi clicking ka fara saka ranar zuwa Naija nan kusa" be jira amsar Mansur ba ya kashe wayar ganin ta qaraso cikin falon tana tafiya kamar wadda kwai ya fashewa a ciki.
Humaira
Wani fitsari taji ya matsota saboda maganganun Khalil din ba shiri ta miqe dan karya zubo tayi abin kunya, dakin Mama daya fi kusa a cikin corridor ta fada, Mama na waya dukda bata san dawa suke magana ba amma tasan maganar ta akeyi dan taji Maman na cewa
"Wallahi in gaya miki, gashi can a falo" ita dai ta wuce ta tsula fitsarinta. Sink ta dafe bayan data wanke fuskarta ta tsaya tana kallon kanta a mudubi. Tunani takeyi ta yaya akayi Yah Khalil ya zama Ibrahim kodai wasa suke so suyi mata da hankali? Kiran da Mama take mata ya sakata fita ta tsaya a bakin qofar.
"Ke kuma lafiya kika shigo kamar an koroki?" Maman ta fada tana kallonta seta narke fuska tace
"Mama Yah Khalil ne, wai shine Ibrahim yace"
"Aa, ke da baki san Khalil Ibrahim bane ko Yaya?" Maman ta sake fada kamar bata fahimci abinda take nufi ba. Kan gadon Maman ta zauna tana cewa
"Mama bafa suna ba, wai shine Ibrahim din da muke waya dashi wai fa Mama Yah Khalil ne yake sona" ymta qarasa maganar kamar zata fashe da kuka dan tunanin wai Khalil ke sonta ma qara firgitata yakeyi, ita fa Humaira Khalil yake so ai abin ya mata nauyi.
"Ke fa shirmenki yawa ne dashi, to se akayi Yaya dan Khalil nasonki ina nan kike raba rana da dare kina zancen Ibrahim kuma yazo shine zaki bi duk ki kidima kanki kamar wadda tayiwa sarki qarya. Ni da Allah wuce kin baro mutum shi kadai a zaune"
"Mama wai baki gane abinda nake fada ba" ta sake fada ganin babu wata alamar damuwa a zantukan Maman, se kuwa Maman ta miqe tana cewa
"Wuce, idan ya tafi kya ganar dani koma menene". Babu yanda ta iya haka ta fito, tana qarasawa tajishi yana waya a hankali take tafiya harta zauna akan kujera kanta a qasa.
"Kin gama gudun da babu gurin zuwa" ya fada yana zura wayarsa a Aljihu, ita dai bata amsa masa ba kanta na qasa tana sake nanata wai Khalil ne Ibrahim dinta, dashi duk suka ringa wannan waya da hira. Tunanin yanda suka musayar maganganu ta ringayi taji kamar qasa ta bude ta shige, yanda ya ringa mata wayo yana tambayarta abubuwa ita ko ta ware tana bashi amsoshi daidai da saninta ashe duk Yah Khalil ne kai wannan abin kunya ina zata kaishi.
"Haba Mana Aisha, har cewa fa kikayi badan Haramun bane da idan muka hadu har Rungumeni zakiyi saboda yanda kike Jina a ranki ko kin manta" Khalil ya jefo mata maganar, ta daga kai ta kalleshi kafin taha pillow ta rufe fuska se jin shashsheqar kukan ta yayi ba shiri ya isa inda ta ke ya durqusa qasab kujerar yana cewa.
"Subhanallahi me kuma akayi na kuka daga wasa? Allah ya baki haquri baki ce haka ba. Ni ne nace da ze yuwu har rungumeki zanyi dan kiji yanda zuciyata taje bugawa akanki koba haka".
Rarrashinta ya ringayi har seda ta dena kukan ta dago fuskarta da tayi Ja.
"Me yasa ka boye mun baka gaya mun kaine Ibrahim ba?" Ta fada cikin muryar Kuka, Khalil dake tsiyaya ruwan sanyi a cuo ya miqa mata ta karba amma bata sha ba. Murmushi yayi mata yace
"Ki sha zan gaya miki komai".
Seda tasha ruwan ta aje cup din se ajiyar zuciya take shiko a zuciyarsa mamaki yake na abinda ya sakata Kuka, yanzu meye abin zafi a nan da har Mutu zeyi kuka banda dai Humaira da son maida qaramin Abu babba.
"Kinsan me yasa naqi na bayyana miki kaina? Saboda wannan abun da kikayi. Nasan idan na fito kaitsaye nace ina sonki zakiyita koke koke ne na rashin dalili kuma nasan be zama lallai ki yarda ba sannan daga qarshe nayi loosing respect din da kike bani na Yaya saboda ku Mata haka kuke, masu qananun shekaru precisely. Da babba wanda ya zarce shekarunku ya nuna yana sonku se ku maida abun wani daban ku dauka kamar wani babbanlaifi ya aikata dan ya ce yana sonku. Shiyasa na zabi na fara shigar miki da soyayya ta idan na samu karbuwa na yarda da kona bayyana miki kaina ba zakice Aa ba kamar dai yanzu na san na rigada na samu fili a zuciyar Aisha ko kawai nayita baza shanyata".
Kanta ma qaa harya qare magana bata iya dagowa ta kalleshi ba, da gaskeyarsa kamar yanda ya fada din gani takeyi kamar sabo ace kamar sa yana sonta shi kansa Ibrahim din kawai bata san yabda akayi ya shiga ranta ba. Amma ita ko a hanya taga Babba ya kula yar yarinya ma kallon Dan iska take yi masa a ganin ta kowa ya ji da daidai dashi babu dalilin da ze saka babban mutum irinsu Yah Khalil din yazo yana son yan yara irinsu sedai a barsu dasu Noor sune daidai shekarun su.
"Kinga bamuyi haka dake ba, kinyi mun Alqawari duk randa muka hadu zaki gayamun gaskiyar abinda kikeji game dani a zuciyarki babu kwange bare coge amma shine yanzu ina magana kinyi Shiru. Ki dago ki kalleni kiyimun magana. Ni na rigada na fada miki duk abinda ya kamata ki sani game dani, dagaske nake sonki da aure ba wasa ne ya kawoni gurinki ba, kuma saboda bana so na takuraki ko na zama silar da za'ayi miki dole ya saka na zabi neman soyayyarki da kaina kinsan idan naso kai tsaye zan tunkari magabatanki da magana sedai kawai ki ganki a gidana amma banyi haka ba saboda ina son aurenki aka yardarki shine ze bamu damar shimfida rayuwa irin wadda nake fata dake".
Ita dai kamar wadda aka daurewa baki haka tayi shiru tana jinsa harya gaji da magana shima yayi mata shirun kawai yana kallonta.
"Matsalar qananan yara kenan" ya ayyana a zuciyarsa, yanzu da babbar budurwa ce data san kanta ba ruwansa da wannan bata lokacin kai tsaye zeje ga buqatarsa amma yanzu kalleshi yanda ya lalace a gaban Kusan yar cikinsa yana lallabata ta masa shiru kamar gunki. Tsaki yaja saboda ransa daya sosu ya miqe yana daukar muqullin motarsa ya kalli Humaira da itama ta dago jin tsakin nasa suka hada ido.
"Bakya buqatar ki gaya mun baki karbeni ba dan naga hakan a aikace. Nagode da lokacin da kika bani inaso kuma ki dauka Ibrahim be taba wanzuwa a rayuwarki ba. Kici gaba da daukata a Khalil kamar yanda baki karbi alaqata ba bana so ki ringa tunota ballantana har ki kalleni da abinda ya wuce, ki gaida Mama idan kin Shiga ki gaya mata na wuce" ya fada yana kallonta kafin ya juya ya nufi qofa. A sanyaye ta miqr tabi bayansa, maganar bata son Ibrahim bata ma taso ba amma fa Yaya Khalil a matsayin Ibrahim shine abinda ta kasa yarda dashi. Ta yaya ma zata iya zama dashi a matsayin Miji abin da wuya wai gurguwa da auran Nesa.
Binsa ta ringayi a baya har zuwa gurin motarsa. Khalil da besan tana biye dashi ba saboda yanda take tafiyar kamar mara Laka ya juyo ze bude motar ya ganta se ya tsaya yana kallonta.
"Kayi haquri" ta iya fada dakyar idonta yana kawo ruwa
"Haquri kuma name? Ai ni ya kamata na baki haquri bake ba, sannan ki goge wannan hawayen kar mutane su dauka wani abun nayi miki" ya fada ganin Samarin dake zaune a Majalisar Habibu suna kallonsu. Hannu biyu ta saka tana goge hawayen kafin cike da quruciya tace
"Nidai dan Allah idan wasa kuke yimun ku dena, ka gayawa Ibrahim kawai inason sa daman ai cewa yayi sena fada masa sannan ze zo qila ma shiyasa ya turoka kayi mun wayo".
Murmushi yayi yace
"Me yasa ni bakya sona se Ibrahim?"
"Kai ai Yayanane" ta bashi amsa da sauri se ya sakeyin qaramar dariya yace
"Shikenan yanzu dai tunda bakya sona bari na tafi, zan roqi Allah ya bani wadda zata soni tunda nayi baqin jini a gurinki".
Shiru tayi ya bude motar ya zauna kafinya janyo wata Leda me kyau daya ajiye a dayan sit ya miqa mata yana cewa
"Ga Alqawarinki".
Kasa karba tayi ya janyo hannunta ya saka mata ledar kafin ya tada motar. Bata motsa daga gurin ba har yaja motarsa ya tafi bayan ya daga mata hannu, fizgar da akayi mata ce tare da radadin da taji a fuskarta daya tabbatar mata da marinta akayi suka dawo da ita daga tunanin data lula lokacin har Motar Khalil ta bace daga gurin.
"Yaya Mansur ina wuni ko nace barka da dare dan nasan ku daren ku ya shiga" Khalil ya fada bayan daya amsa sallamar da Mansur yayi masa. Daga daya bangaren Mansur yace
"Da alama shaye shaye ka fara ko idan ba haka ba ni zakace wa Yaya saboda Dan iska ne kai? Ni ba surukinka ba ba komai ba kace mun wani Yaya bayan ko a shekaru aka qirga ka girme balle kace hankali ka qaro yau zaka bani girma".
Dariya Khalil ya fashe da ita shima Mansur din na tayashi kafin yace
"Ka sani ko zaka zama surukin nawa ai abun na Allah ne"
"Wa Allah ya tsareni da zama surukinka dadai wannan matar a gidan ka ko yan uwan maqotan mu da na sani bazan bari su baka mata ba" Mansur ya sake fada se Khalil yayi murmushi yace
"Toh Yaya Mansur ya zanyi dakai tunda haka kace"
"Ka gama iskancinka ka fada mun abinda yasa ka kirani Malam" cewar Mansur, se Khalil yayi saurin cewa
"Zan sake kiranka zansu ina tsakiyar wani Important deal ne, kaidai da yayi clicking ka fara saka ranar zuwa Naija nan kusa" be jira amsar Mansur ba ya kashe wayar ganin ta qaraso cikin falon tana tafiya kamar wadda kwai ya fashewa a ciki.
Humaira
Wani fitsari taji ya matsota saboda maganganun Khalil din ba shiri ta miqe dan karya zubo tayi abin kunya, dakin Mama daya fi kusa a cikin corridor ta fada, Mama na waya dukda bata san dawa suke magana ba amma tasan maganar ta akeyi dan taji Maman na cewa
"Wallahi in gaya miki, gashi can a falo" ita dai ta wuce ta tsula fitsarinta. Sink ta dafe bayan data wanke fuskarta ta tsaya tana kallon kanta a mudubi. Tunani takeyi ta yaya akayi Yah Khalil ya zama Ibrahim kodai wasa suke so suyi mata da hankali? Kiran da Mama take mata ya sakata fita ta tsaya a bakin qofar.
"Ke kuma lafiya kika shigo kamar an koroki?" Maman ta fada tana kallonta seta narke fuska tace
"Mama Yah Khalil ne, wai shine Ibrahim yace"
"Aa, ke da baki san Khalil Ibrahim bane ko Yaya?" Maman ta sake fada kamar bata fahimci abinda take nufi ba. Kan gadon Maman ta zauna tana cewa
"Mama bafa suna ba, wai shine Ibrahim din da muke waya dashi wai fa Mama Yah Khalil ne yake sona" ymta qarasa maganar kamar zata fashe da kuka dan tunanin wai Khalil ke sonta ma qara firgitata yakeyi, ita fa Humaira Khalil yake so ai abin ya mata nauyi.
"Ke fa shirmenki yawa ne dashi, to se akayi Yaya dan Khalil nasonki ina nan kike raba rana da dare kina zancen Ibrahim kuma yazo shine zaki bi duk ki kidima kanki kamar wadda tayiwa sarki qarya. Ni da Allah wuce kin baro mutum shi kadai a zaune"
"Mama wai baki gane abinda nake fada ba" ta sake fada ganin babu wata alamar damuwa a zantukan Maman, se kuwa Maman ta miqe tana cewa
"Wuce, idan ya tafi kya ganar dani koma menene". Babu yanda ta iya haka ta fito, tana qarasawa tajishi yana waya a hankali take tafiya harta zauna akan kujera kanta a qasa.
"Kin gama gudun da babu gurin zuwa" ya fada yana zura wayarsa a Aljihu, ita dai bata amsa masa ba kanta na qasa tana sake nanata wai Khalil ne Ibrahim dinta, dashi duk suka ringa wannan waya da hira. Tunanin yanda suka musayar maganganu ta ringayi taji kamar qasa ta bude ta shige, yanda ya ringa mata wayo yana tambayarta abubuwa ita ko ta ware tana bashi amsoshi daidai da saninta ashe duk Yah Khalil ne kai wannan abin kunya ina zata kaishi.
"Haba Mana Aisha, har cewa fa kikayi badan Haramun bane da idan muka hadu har Rungumeni zakiyi saboda yanda kike Jina a ranki ko kin manta" Khalil ya jefo mata maganar, ta daga kai ta kalleshi kafin taha pillow ta rufe fuska se jin shashsheqar kukan ta yayi ba shiri ya isa inda ta ke ya durqusa qasab kujerar yana cewa.
"Subhanallahi me kuma akayi na kuka daga wasa? Allah ya baki haquri baki ce haka ba. Ni ne nace da ze yuwu har rungumeki zanyi dan kiji yanda zuciyata taje bugawa akanki koba haka".
Rarrashinta ya ringayi har seda ta dena kukan ta dago fuskarta da tayi Ja.
"Me yasa ka boye mun baka gaya mun kaine Ibrahim ba?" Ta fada cikin muryar Kuka, Khalil dake tsiyaya ruwan sanyi a cuo ya miqa mata ta karba amma bata sha ba. Murmushi yayi mata yace
"Ki sha zan gaya miki komai".
Seda tasha ruwan ta aje cup din se ajiyar zuciya take shiko a zuciyarsa mamaki yake na abinda ya sakata Kuka, yanzu meye abin zafi a nan da har Mutu zeyi kuka banda dai Humaira da son maida qaramin Abu babba.
"Kinsan me yasa naqi na bayyana miki kaina? Saboda wannan abun da kikayi. Nasan idan na fito kaitsaye nace ina sonki zakiyita koke koke ne na rashin dalili kuma nasan be zama lallai ki yarda ba sannan daga qarshe nayi loosing respect din da kike bani na Yaya saboda ku Mata haka kuke, masu qananun shekaru precisely. Da babba wanda ya zarce shekarunku ya nuna yana sonku se ku maida abun wani daban ku dauka kamar wani babbanlaifi ya aikata dan ya ce yana sonku. Shiyasa na zabi na fara shigar miki da soyayya ta idan na samu karbuwa na yarda da kona bayyana miki kaina ba zakice Aa ba kamar dai yanzu na san na rigada na samu fili a zuciyar Aisha ko kawai nayita baza shanyata".
Kanta ma qaa harya qare magana bata iya dagowa ta kalleshi ba, da gaskeyarsa kamar yanda ya fada din gani takeyi kamar sabo ace kamar sa yana sonta shi kansa Ibrahim din kawai bata san yabda akayi ya shiga ranta ba. Amma ita ko a hanya taga Babba ya kula yar yarinya ma kallon Dan iska take yi masa a ganin ta kowa ya ji da daidai dashi babu dalilin da ze saka babban mutum irinsu Yah Khalil din yazo yana son yan yara irinsu sedai a barsu dasu Noor sune daidai shekarun su.
"Kinga bamuyi haka dake ba, kinyi mun Alqawari duk randa muka hadu zaki gayamun gaskiyar abinda kikeji game dani a zuciyarki babu kwange bare coge amma shine yanzu ina magana kinyi Shiru. Ki dago ki kalleni kiyimun magana. Ni na rigada na fada miki duk abinda ya kamata ki sani game dani, dagaske nake sonki da aure ba wasa ne ya kawoni gurinki ba, kuma saboda bana so na takuraki ko na zama silar da za'ayi miki dole ya saka na zabi neman soyayyarki da kaina kinsan idan naso kai tsaye zan tunkari magabatanki da magana sedai kawai ki ganki a gidana amma banyi haka ba saboda ina son aurenki aka yardarki shine ze bamu damar shimfida rayuwa irin wadda nake fata dake".
Ita dai kamar wadda aka daurewa baki haka tayi shiru tana jinsa harya gaji da magana shima yayi mata shirun kawai yana kallonta.
"Matsalar qananan yara kenan" ya ayyana a zuciyarsa, yanzu da babbar budurwa ce data san kanta ba ruwansa da wannan bata lokacin kai tsaye zeje ga buqatarsa amma yanzu kalleshi yanda ya lalace a gaban Kusan yar cikinsa yana lallabata ta masa shiru kamar gunki. Tsaki yaja saboda ransa daya sosu ya miqe yana daukar muqullin motarsa ya kalli Humaira da itama ta dago jin tsakin nasa suka hada ido.
"Bakya buqatar ki gaya mun baki karbeni ba dan naga hakan a aikace. Nagode da lokacin da kika bani inaso kuma ki dauka Ibrahim be taba wanzuwa a rayuwarki ba. Kici gaba da daukata a Khalil kamar yanda baki karbi alaqata ba bana so ki ringa tunota ballantana har ki kalleni da abinda ya wuce, ki gaida Mama idan kin Shiga ki gaya mata na wuce" ya fada yana kallonta kafin ya juya ya nufi qofa. A sanyaye ta miqr tabi bayansa, maganar bata son Ibrahim bata ma taso ba amma fa Yaya Khalil a matsayin Ibrahim shine abinda ta kasa yarda dashi. Ta yaya ma zata iya zama dashi a matsayin Miji abin da wuya wai gurguwa da auran Nesa.
Binsa ta ringayi a baya har zuwa gurin motarsa. Khalil da besan tana biye dashi ba saboda yanda take tafiyar kamar mara Laka ya juyo ze bude motar ya ganta se ya tsaya yana kallonta.
"Kayi haquri" ta iya fada dakyar idonta yana kawo ruwa
"Haquri kuma name? Ai ni ya kamata na baki haquri bake ba, sannan ki goge wannan hawayen kar mutane su dauka wani abun nayi miki" ya fada ganin Samarin dake zaune a Majalisar Habibu suna kallonsu. Hannu biyu ta saka tana goge hawayen kafin cike da quruciya tace
"Nidai dan Allah idan wasa kuke yimun ku dena, ka gayawa Ibrahim kawai inason sa daman ai cewa yayi sena fada masa sannan ze zo qila ma shiyasa ya turoka kayi mun wayo".
Murmushi yayi yace
"Me yasa ni bakya sona se Ibrahim?"
"Kai ai Yayanane" ta bashi amsa da sauri se ya sakeyin qaramar dariya yace
"Shikenan yanzu dai tunda bakya sona bari na tafi, zan roqi Allah ya bani wadda zata soni tunda nayi baqin jini a gurinki".
Shiru tayi ya bude motar ya zauna kafinya janyo wata Leda me kyau daya ajiye a dayan sit ya miqa mata yana cewa
"Ga Alqawarinki".
Kasa karba tayi ya janyo hannunta ya saka mata ledar kafin ya tada motar. Bata motsa daga gurin ba har yaja motarsa ya tafi bayan ya daga mata hannu, fizgar da akayi mata ce tare da radadin da taji a fuskarta daya tabbatar mata da marinta akayi suka dawo da ita daga tunanin data lula lokacin har Motar Khalil ta bace daga gurin.