Sashe 177
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita dai bata ce komai ba ta samu guri ta zauna tana zare dankwalin kanta ta gaida Hajiyar ta amsa mata a cukule. Me aiki tacewa ta kawo mata abinci taja Flask din gaban Hajiya tana cewa
"Naman kai kuka samu haka duk ya cika falon da qamshi" ta fada tana kaiwa bakinta, Khalifa ya dago yace
"Mutuniyarki ce ta kawowa Hajiya"
"Wa?" Ta tambaya tana tauna na bakinta se ya ce
"Anty Umaimah mana" ai be qarasa fadar sunan ba Jalilah ta tofo naman daga bakinta kafin ta miqe da gudu ta shige kitchen. Gaban sink ta tsaya ta ringa kakarin amai seda ta janyoshi ta amayar da duk abinda yake cikinta kafin hankalinta ya kwanta ta dawo falon tana mayar da numfashi.
Cikin fada Hajiya ta kalleta tace
"Wane irin iskanci ne haka Jalilah zaki dawowa da mutane abincin baki kina kakari se kace wadda taci mushe a rashin sani?"
"Toh ai wallahi Hajiya gara ace Mushen naci ban sani ba Allah baze kamani da laifi ba akan naci abinda ya fito daga hannunta. Yanzu Hajiya ana wannan gabar zata dafo nama ta kawo miki kici hankali kwance babu abinda ya dameki?"
Harararta Hajiya tayi tace
"To se akayi yaya idanta bani nama naci zata bani abin cutarwa ne ko yaya?"
"Toh Allah ya rufa Asiri, koda yakr daman ai ta dade da gamawa daku ta daga ta baku kun cinye dake da Khalil din shiyasa bazaku taba ganin laifinta ba, to mudai munfi qarfinta in sha Allahu duk wani tsubbunta bazeyi tasiri akanmu ba kuma muna muku addu'a Allahya kwato ku"
"Toh Amin dai amma Anty Hajiya da Yah Khalil ai sunyi nisa. Jiya fa ta rotsa masa mota a gidan nan ace yau ta zo salin alin ta kawowa Hajiya abu taci shiyasa da aka mun tayi nace na qoshi to waya aikeni? Daman an ce Asirin da aka ci a abinci yafi tasiri kuma yafi wahalar magani" Khalifa ya fada yana tattara kayansa se Hajiya tayi shiru ta kuma kasa ci gaba da cin naman data qara. Me aiki Jalilah ta kwalawa kira tace tazo ta dauke sauran ta zubar.
"Saura kici nasan ku da shegen son zuciya zubarwa akace kiyi ki kai canbolar qofar gida ki zubar karnuka su samu" ta fada mata ta tattara harda na farantin Hajiya ta fita dashi Umaimah dake labe najin tahowarta tayi saurin barin gurin a ranta tana cewa
"Daga baya kenan wadda nayi dan ita taci kuma baki isa kisa ta amayo shi ba kema ina tafe kanki senayi maganinki wlh.
Basira me aiki kuwa tana fita Sammani ya tareta ganinta da kwano yana tambayarta ina zata, tana fada masa abinda zatayi ya karbe yana cewa
"Amma baki da hankali naman zaki zubar a bola maganin bera aka saka a ciki kome?"
"Nima ban sani ba, Anty ce tace a zubar" ta bashi amsa seya bude kwanon da aka kawo masa nasa da har yaci rabi ya juye a ciki yana cewa
"Ke dallah rabu da wannan matar tafi kowa fitina a yaran gidan nan na rasa meyw hadata da Hajiya Umaimah da bata sonta shine zata saka a zubar da abincin data dafa saboda mugun to mu zamu ci abin mu mayar da kwanon kice kin zubar kawai"
"Toh dan sammun wlh tunda aka kai yawuna ya tsinke" Basira ta fada seya dan yafita mata kadan a kwanon yana cewa
"Kinga wannan sake rabashi biyu zanyi naci rabi da dare rabi seda safe zan dumama abuna, Allah yasa ma Alhaji yayi wo mana tsabar balangu na hafa yau na kashe dadi abuna. Daga yanzu duk randa aka ce ki zubar da abinci ki ringa kawo mun nan kinji ko" ya dauke kwanonsa ya shige dakinsa.
A cikin gida kuwa Jalilah bayan ta zubo abinci ta zauna tana ci ta cewa Khalifa ya fito da kayayyakin da suke ledojin data zo dasu nan ya shiga zazzagewa a qasa kayane iya ganinka Atamfofi, Laces, Material sunfi Kala Hamsin ga Mayafai nan da gani sunfi Dozen biyu suma da sauran tarkacen mata na kwalliya. Da mamaki Hajiya ta kalleta tace
"Ke kuma Kanti zaki bude ko yaya wannan uban kaya haka da kika rakito?"
"Wane kanti Hajiya? Siyayyar Hussaini ce, wata qawata ce tayi sales shine naga an samu ragi sosai na kwaso su, dudduba ki gani manyan Atamfa Super kadai ya rage za'a qara ko guda biyar haka dan nan akwai su Holand da sauransu Chiganvy ce qarama a ciki Laces din kuwa sun isa guda Goma sha biyar ne ga Material biyar Voile biyar, nasa a kawo Lafaya Lace biyar ai sun isa ko?" Ta fada tana kallon Hajiya data saki baki kawai tana jin lissafi.
"To duk na menene haka kafinna gama jin abinda ya rage a ciki din" Hajiya ta fada seta miqe ta tafi gurin Fridge tana cewa
"Bakiji ba nace na Usainina ne kayan lefe na fara hadowa Khalil, ai yau bazan bar gidan nan ba se yazo munyi lissafi tas mun ga abinda ya rage a siya, se kuma inji batun inda ze ajiye Amaryar, daman ni Saman nan da babu kowa nayi mata tanadi ita wannan ta tattaro gaba daya ta dawo qasa daman nan aka san uwar gida ta bar Amarya a sama kusa dashi yanda zasu wataya da kyau babu me saka musu ido"
"Sannu Jalilah da iya tarar Aradu da Ka" Hajiua ta fada tana kallonta.
KHALIL
Qarfe biyar ya tashi aiki, seda ya tsaya yayi mata tsarabar chocolate da Ice cream kafin ya kama hanyar gidan. Maman kadai ya tarar a gida wai Humairan ta tafi Islamiyya.
"In banda shaqiyanci irin nata da tasan zakazo ai zeta haqura yau daya dai da Makarantar" Mama data kawo masa ruwa ta fada se yayi murmushi yace
"Ba laifinta bane Mama, jiya nace mata zanzo banzo ba inaga shiyasa ta dauka yau dinma bada gaske nake ba, daman daga office nake na biyo na kawo mata wannan" ya ajiye mata ledar siyayyar da yiwo seta dauka tana cewa
"To an gode Allah saka da Alkhairi a kuma ci gaba da haquri da mutuniyar kasan akwai quruciya akanta.
Dazun Alhaji Abubakar yazo da safe ai to har ma na bashi number Babban Yayanmu zasuyi magana dashi can se abinda suka zartar Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi yasa yin na Allah ne".
Kasa tantance yanayin da zuciyarsa take ciki yayi, farin ciki zeyi na kasancewar Manya sun shiga maganat auran sa ko kuwa Akasin haka? Ya Umaimah zata karbi Al'amarin abinda yake ta tuani a zuciyarsa kenan. Haka ya kama hanyar gida dukda Maman tace ya zauna ta aika a kira Humairan yace Aa ta barta kawai in ya samu dama da daddare ze dawo.
Yana fitowa a qofar gidan suka ci karo ta taho da sauri kamar wadda aka biyo zata shiga gidan ganinsa yasa ta dakata se kuma tayi sauri ta rabe shi ta shige jin Noor daya biyota yana koran sunanta. Kallonsu Khalil yayi ganin Noor din shima yana neman shiga cikin gidan har yana riqo mata Hijabi Khalil din yayi saurin riqeshi yana cewa
"Kai lafiyar ka qalau kuwa? Baka da hankali zaka kama mata hijab?"
"Malam kai kuma wanene? Dallah sakeni kafin na nuna maka danyan kai a nan gurin" Noor din ya fada yana zare ido tareda qoqarin kwace hannunsa da Khalil ya riqe. Mamakin tsaurin idonsa yayi yaron da befi sa'an Khalifa ba shine yake gaya masa haka take ya sake riqe hannun dakyau ya murde har seda Noor din ya saki qara kafin ya sake shi ya nuna shi yana cewa
"Idan ka kuskura koda wasa hannunka ya sake taba suturarta sena karya ka, wuce ka fita ka bawa mutane guri".
"Wallahi se kayi dana sanin abinda kayi mun, kw kuma ko bajima ko ba dade sena dauki fansa akan abinda kikayi mun zaki san ni kika yaudara" Noor din ya fada cikin wani irin fushi kafin ya juya fuuu ya fita daga gidan Mama da Hayaniyarsu ta fito da ita ta bishi tana cewa
"Babu abinda zata gani se Alkhairi Insha Allah mutumin banza kawai, kema shegen taurin kanki da nace ki fita a sabgarsa bakiji ba kenan".
Kuka Humairan ta saka tana cewa
"Ni Mama babu abinda na masa, haka kawai mun taho a hanya ya tareni wai dole se na tsaya munyi magana ni kuma nace bazan tsaya ba sedai ya zo gida idan maganar yake so muyi shinrme fa yake ta zagina ya biyo ni wai Macuciya mayaudariya zan auri wani bashi ba" ta qarasa tana sake rushewa da Kuka. Kallonta Khalil yakeyi wani mugun kishi na cinsa se kawai ya juya ya fice yana cewa Mama seda safe. Jiki a sanyaye taja Humairan suka shiga ciki ta ringa lallabata seda tayi shiru kafin tace ta kira Khalil ta bashi haquri.
Ransa babu dadi ya shiga gida. Yanasaka qafarsa a falon kansa ya sara kamar jiya, Umaimah na zaune a falon suna kallo da su Mu'ayyad suka tafi da gudu suna masa Oyoyo ya daga su sama daddaya kafin ya kama hannunsu suka shiga ciki. Idonta akan Tv tayi masa sannu da zuwa ya amsa yana zama a kusa da ita Ruqayya ta kawo masa ruwa ya fara sha kenan Wayarsa dake hannun Mu'ayyad ta shiga qara, be kawo ita bace dan haka Mu'ayyad din na miqo masa ya rigada ya daga dan haka ya danna speaker kawai yaci gaba shan ruwan bayan yayi sallama.
"Naman kai kuka samu haka duk ya cika falon da qamshi" ta fada tana kaiwa bakinta, Khalifa ya dago yace
"Mutuniyarki ce ta kawowa Hajiya"
"Wa?" Ta tambaya tana tauna na bakinta se ya ce
"Anty Umaimah mana" ai be qarasa fadar sunan ba Jalilah ta tofo naman daga bakinta kafin ta miqe da gudu ta shige kitchen. Gaban sink ta tsaya ta ringa kakarin amai seda ta janyoshi ta amayar da duk abinda yake cikinta kafin hankalinta ya kwanta ta dawo falon tana mayar da numfashi.
Cikin fada Hajiya ta kalleta tace
"Wane irin iskanci ne haka Jalilah zaki dawowa da mutane abincin baki kina kakari se kace wadda taci mushe a rashin sani?"
"Toh ai wallahi Hajiya gara ace Mushen naci ban sani ba Allah baze kamani da laifi ba akan naci abinda ya fito daga hannunta. Yanzu Hajiya ana wannan gabar zata dafo nama ta kawo miki kici hankali kwance babu abinda ya dameki?"
Harararta Hajiya tayi tace
"To se akayi yaya idanta bani nama naci zata bani abin cutarwa ne ko yaya?"
"Toh Allah ya rufa Asiri, koda yakr daman ai ta dade da gamawa daku ta daga ta baku kun cinye dake da Khalil din shiyasa bazaku taba ganin laifinta ba, to mudai munfi qarfinta in sha Allahu duk wani tsubbunta bazeyi tasiri akanmu ba kuma muna muku addu'a Allahya kwato ku"
"Toh Amin dai amma Anty Hajiya da Yah Khalil ai sunyi nisa. Jiya fa ta rotsa masa mota a gidan nan ace yau ta zo salin alin ta kawowa Hajiya abu taci shiyasa da aka mun tayi nace na qoshi to waya aikeni? Daman an ce Asirin da aka ci a abinci yafi tasiri kuma yafi wahalar magani" Khalifa ya fada yana tattara kayansa se Hajiya tayi shiru ta kuma kasa ci gaba da cin naman data qara. Me aiki Jalilah ta kwalawa kira tace tazo ta dauke sauran ta zubar.
"Saura kici nasan ku da shegen son zuciya zubarwa akace kiyi ki kai canbolar qofar gida ki zubar karnuka su samu" ta fada mata ta tattara harda na farantin Hajiya ta fita dashi Umaimah dake labe najin tahowarta tayi saurin barin gurin a ranta tana cewa
"Daga baya kenan wadda nayi dan ita taci kuma baki isa kisa ta amayo shi ba kema ina tafe kanki senayi maganinki wlh.
Basira me aiki kuwa tana fita Sammani ya tareta ganinta da kwano yana tambayarta ina zata, tana fada masa abinda zatayi ya karbe yana cewa
"Amma baki da hankali naman zaki zubar a bola maganin bera aka saka a ciki kome?"
"Nima ban sani ba, Anty ce tace a zubar" ta bashi amsa seya bude kwanon da aka kawo masa nasa da har yaci rabi ya juye a ciki yana cewa
"Ke dallah rabu da wannan matar tafi kowa fitina a yaran gidan nan na rasa meyw hadata da Hajiya Umaimah da bata sonta shine zata saka a zubar da abincin data dafa saboda mugun to mu zamu ci abin mu mayar da kwanon kice kin zubar kawai"
"Toh dan sammun wlh tunda aka kai yawuna ya tsinke" Basira ta fada seya dan yafita mata kadan a kwanon yana cewa
"Kinga wannan sake rabashi biyu zanyi naci rabi da dare rabi seda safe zan dumama abuna, Allah yasa ma Alhaji yayi wo mana tsabar balangu na hafa yau na kashe dadi abuna. Daga yanzu duk randa aka ce ki zubar da abinci ki ringa kawo mun nan kinji ko" ya dauke kwanonsa ya shige dakinsa.
A cikin gida kuwa Jalilah bayan ta zubo abinci ta zauna tana ci ta cewa Khalifa ya fito da kayayyakin da suke ledojin data zo dasu nan ya shiga zazzagewa a qasa kayane iya ganinka Atamfofi, Laces, Material sunfi Kala Hamsin ga Mayafai nan da gani sunfi Dozen biyu suma da sauran tarkacen mata na kwalliya. Da mamaki Hajiya ta kalleta tace
"Ke kuma Kanti zaki bude ko yaya wannan uban kaya haka da kika rakito?"
"Wane kanti Hajiya? Siyayyar Hussaini ce, wata qawata ce tayi sales shine naga an samu ragi sosai na kwaso su, dudduba ki gani manyan Atamfa Super kadai ya rage za'a qara ko guda biyar haka dan nan akwai su Holand da sauransu Chiganvy ce qarama a ciki Laces din kuwa sun isa guda Goma sha biyar ne ga Material biyar Voile biyar, nasa a kawo Lafaya Lace biyar ai sun isa ko?" Ta fada tana kallon Hajiya data saki baki kawai tana jin lissafi.
"To duk na menene haka kafinna gama jin abinda ya rage a ciki din" Hajiya ta fada seta miqe ta tafi gurin Fridge tana cewa
"Bakiji ba nace na Usainina ne kayan lefe na fara hadowa Khalil, ai yau bazan bar gidan nan ba se yazo munyi lissafi tas mun ga abinda ya rage a siya, se kuma inji batun inda ze ajiye Amaryar, daman ni Saman nan da babu kowa nayi mata tanadi ita wannan ta tattaro gaba daya ta dawo qasa daman nan aka san uwar gida ta bar Amarya a sama kusa dashi yanda zasu wataya da kyau babu me saka musu ido"
"Sannu Jalilah da iya tarar Aradu da Ka" Hajiua ta fada tana kallonta.
KHALIL
Qarfe biyar ya tashi aiki, seda ya tsaya yayi mata tsarabar chocolate da Ice cream kafin ya kama hanyar gidan. Maman kadai ya tarar a gida wai Humairan ta tafi Islamiyya.
"In banda shaqiyanci irin nata da tasan zakazo ai zeta haqura yau daya dai da Makarantar" Mama data kawo masa ruwa ta fada se yayi murmushi yace
"Ba laifinta bane Mama, jiya nace mata zanzo banzo ba inaga shiyasa ta dauka yau dinma bada gaske nake ba, daman daga office nake na biyo na kawo mata wannan" ya ajiye mata ledar siyayyar da yiwo seta dauka tana cewa
"To an gode Allah saka da Alkhairi a kuma ci gaba da haquri da mutuniyar kasan akwai quruciya akanta.
Dazun Alhaji Abubakar yazo da safe ai to har ma na bashi number Babban Yayanmu zasuyi magana dashi can se abinda suka zartar Allah dai ya tabbatar mana da Alkhairi yasa yin na Allah ne".
Kasa tantance yanayin da zuciyarsa take ciki yayi, farin ciki zeyi na kasancewar Manya sun shiga maganat auran sa ko kuwa Akasin haka? Ya Umaimah zata karbi Al'amarin abinda yake ta tuani a zuciyarsa kenan. Haka ya kama hanyar gida dukda Maman tace ya zauna ta aika a kira Humairan yace Aa ta barta kawai in ya samu dama da daddare ze dawo.
Yana fitowa a qofar gidan suka ci karo ta taho da sauri kamar wadda aka biyo zata shiga gidan ganinsa yasa ta dakata se kuma tayi sauri ta rabe shi ta shige jin Noor daya biyota yana koran sunanta. Kallonsu Khalil yayi ganin Noor din shima yana neman shiga cikin gidan har yana riqo mata Hijabi Khalil din yayi saurin riqeshi yana cewa
"Kai lafiyar ka qalau kuwa? Baka da hankali zaka kama mata hijab?"
"Malam kai kuma wanene? Dallah sakeni kafin na nuna maka danyan kai a nan gurin" Noor din ya fada yana zare ido tareda qoqarin kwace hannunsa da Khalil ya riqe. Mamakin tsaurin idonsa yayi yaron da befi sa'an Khalifa ba shine yake gaya masa haka take ya sake riqe hannun dakyau ya murde har seda Noor din ya saki qara kafin ya sake shi ya nuna shi yana cewa
"Idan ka kuskura koda wasa hannunka ya sake taba suturarta sena karya ka, wuce ka fita ka bawa mutane guri".
"Wallahi se kayi dana sanin abinda kayi mun, kw kuma ko bajima ko ba dade sena dauki fansa akan abinda kikayi mun zaki san ni kika yaudara" Noor din ya fada cikin wani irin fushi kafin ya juya fuuu ya fita daga gidan Mama da Hayaniyarsu ta fito da ita ta bishi tana cewa
"Babu abinda zata gani se Alkhairi Insha Allah mutumin banza kawai, kema shegen taurin kanki da nace ki fita a sabgarsa bakiji ba kenan".
Kuka Humairan ta saka tana cewa
"Ni Mama babu abinda na masa, haka kawai mun taho a hanya ya tareni wai dole se na tsaya munyi magana ni kuma nace bazan tsaya ba sedai ya zo gida idan maganar yake so muyi shinrme fa yake ta zagina ya biyo ni wai Macuciya mayaudariya zan auri wani bashi ba" ta qarasa tana sake rushewa da Kuka. Kallonta Khalil yakeyi wani mugun kishi na cinsa se kawai ya juya ya fice yana cewa Mama seda safe. Jiki a sanyaye taja Humairan suka shiga ciki ta ringa lallabata seda tayi shiru kafin tace ta kira Khalil ta bashi haquri.
Ransa babu dadi ya shiga gida. Yanasaka qafarsa a falon kansa ya sara kamar jiya, Umaimah na zaune a falon suna kallo da su Mu'ayyad suka tafi da gudu suna masa Oyoyo ya daga su sama daddaya kafin ya kama hannunsu suka shiga ciki. Idonta akan Tv tayi masa sannu da zuwa ya amsa yana zama a kusa da ita Ruqayya ta kawo masa ruwa ya fara sha kenan Wayarsa dake hannun Mu'ayyad ta shiga qara, be kawo ita bace dan haka Mu'ayyad din na miqo masa ya rigada ya daga dan haka ya danna speaker kawai yaci gaba shan ruwan bayan yayi sallama.