Sashe 170
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da wannan suka rufe zaman, kuma basu tashi ba seda Hajiyan ta kira Baba Abu ta sanar masa kuma shima yayi na'am da al'amarin har yana cewa
"Ai Hajiya Ibrahim me haquri ne wallahi saboda tunda naji halayyar yarinyar nan a bakin iyayenta na tabbatar da ba qaramin haquri yake dashi ba da aka dauki wannan lokaci babu wanda yaji kansu kinga kuwa yanzu tunda ya nuna yana da buqatar qari babu me hanashi, zan samu Alhaji Garba da Alhaji Shehu se muji ta bakin Ibrahim din inda za'aje masa neman auran, Allah ya tabbatar da Alkairi yasa zamu gani".
Guraren sha daya da rabi Jamia ta miqe zata tafi dan tana da duty a Asibiti sha biyu zata karba, tare suka fita da Anty Amina datace itama zata koma gida dan babu abinda tayi kafin ta fito nan suka bar Jalilah da zata wuni tana sake jaddada musu kowa ta hado gudummawarta su fara hada lefe Jamila na mata tsiyar ita da yar dakin nata yau kuma itace ja gaba a kan qaro mata abokiyar zama suka fita suna dariya.
Turus sukayi a compound gurin da Khalil yake ajiye motoci, cikin kaduwa Anty Amina ta shiga kwalawa Sammani kira se gashi nan kamar an jefoshi ya fado gurin.
KHALIL
Tun qarfe bakwai ya shirya saboda zeje Qunchi, suna aikin gina makarantar kwaleji ya manta shaf be sanar mata da fitar safe zeyi ba dan haka bayan ya gama shirinsa dakansa ya tafasa ruwan zafi ya hada shayi yasha da sauran Gurasar jiya da sukayi ya dumamata. Yana cikin karyawar Ruqayya ta shiga kitchen din, cikin girmamawa ta gaidashi ya amsa yana tambayarta ko Umaiman ta tashi tace masa Eh yanzun ma ita zata damawa Kunun Gyada dan haka ya fita daga kitchen din ya wuce dakinta na qasa. Tana zaune akan gadon ta jingine bayanta da Allon gadon tana danna waya ya shiga ta dago ta kalle shi tareda amsa sallamar da yayi kafin ta mayar da kai tana ci gaba da danna wayar.
A gaban mudubi ya tsaya yana kallonta, gani yayi ta kumbura tun daga fuskarta har zuwa yatsun qafarta dan haka ya matsa kan gadon ya danna qafarta da yatsun hannunsa ta janye qafar tana ya mutsa fuska kafin ta gaidashi a hankali. Be amsa ba ya zauna gefenta yana cewa
"Meya sameki haka, kinga yanda kika kumbura gaba daya kuwa? Amma jiya da dare naga ba haka kike ba".
Baki ta dan tabe kafin tace
"Nima haka na tashi na ganni ai"
"Kuma shine kike zaune ba zaki kirani muje Asibiti ba, ina ne yake miki ciwo?" Ya fada yana miqewa tsaye seta kalle shi tace
"Nifa lafiya ta qalau inda ina jin wani ciwo ai da na tafi Asibitin da kaina, kuma kumburi daman in ciki ya tsufa ai mutum yana yi ba wani sabon abu bane"
"Amma ba irin wannan ba, duk cikin da kikayi baki taba kumbura haka ba ki tashi kawai muje Asibiti su duba ki idan sun tabbatar da babu wata matsala sannan zan yarda" ya sake fada yana janyo Hijabinta da tayi sallah ta bari akan Sallayar. Baki ta zumbura tana zaune bata da niyyar tashi kuma bata ce masa komai ba se ya ja tsaki yana kallonta cikin bacin rai yace
"Kina da matsala, lafiyar jikinki ma baki damu da ita ba komai se kin saka shirme da shiririta a cikinsa ki tashi nace tun ban bata miki rai ba saboda kin san ni bama wasa da duk abinda ya shafi lafiya".
Dole ta miqe badan taso ba, dakyar taken daga qafa saboda yanda jikinta yayi nauyi, ita kanta tasan kumburin ya zarce na yanda ta saba amma saboda bataji wani ciwo ba kuma da rashin daukar abu da muhimmanci kamar yanda yace din yasa tayi zamanta. A hanya yana ta faman yi mata mita ita kuwa ta doni baki gaba kamar zata tabo glass din motar, daidai zasu shiga Gate din Asibitin watarsa dake ajiye tayi qara, yanda kasan ita aka kira ta kalli wayar da sauri 'Shatunah' sunan data gani yana yawo kenan akan screen din wayar ta kalli Khalil wanda shima kallo daya yayiwa wayar ya dauke kai tamkar bashi ake kira ba a haka ya nemi guri yayi parking motar ya kashe kafin ya dauki wayar tasa da Wallet kuma har sannan yaqi yarda su hada ido da Umaimah data kafa masa nata idanun kamar wata sabuwar Mayya.
Seda ya kusa shiga Reception din Asibitin ya lura da bata biyo shi ba, yawu ya hadiye kafin ya qara hade fuska ya juya gurin Motar, tana ciki hat sannan ta hada uban zuba kamar me naquda se numfarfashi takeyi yanda kasan ana tsira mata allura zata fashe saboda fushi.
"Ki fito muje" ya fada cikin tsare gida kamar tana jiransa kuwa tace
"Bazan fito ba, idan kuma ka isa kazo ka fiddani ta qarfi".
Kallonta yayi ganin yanda fuskarta tayi ya tabbatar da ba abinda ya mata zafi yanzu zata tara masa mutane ta zubar masa da mutunchi a gurin dan haka ya bude sit dinsa ya shiga seda ya kulle motar kafin ya kalleta babu yabo babu fallasa yace
"Ki yi haquri muje a dubaki bayan nan koma menene idan muka koma gida se muyi magana akai".
"Ashe kasan akwai abinda zamuyi magana akai kenan, to jikina ne kuma lafiyata ko nace bazan shiga ba, ko ka gaya mun wace yar iska ce ta kiraka da har kake dangantata da taka ko kuma wallahi yanzu a nan gurin nayi maka Tijarar da baka zata ba" Umaiman ta fada tana kallonsa Khalil dayaji ransa ya baci nan da nan saboda yar iska data kira Humairansa da shi yasaka shima cikin fushi yace mata
"Kin dade bakiyi Tijara ba ko kuwa an gaya miki ina tsoron haukanki ne? Jiki kuma kamar yanda kika fada nakine lafiyarki ce duk abinda ya sameki ke kadai ya shafa bani ba dan nan bada dadewa ba zan dakko wata dake ko babu ke rayuwata zanyi bani da Asara" yana gama fadar haka ya tada motar a tsiyace ya fizgeta ya fice daga Asibitin Umaimah da tayi suman zaune saboda jin abubuwan da yake fada fizgar da yayiwa motar ce ta tabbatar mata da cewar a Raye take kuma gaske ne ba mafarki ba Khalil ne yake fada mata wadannan maganganun.
"Dake ko babu ke zanyi rayuwata bani da Asara" maganar ta caki zuciyarta kamar shigar mashi, cikin azamar da bata san tana da ita ba ta kaiwa Sitiyarin cafka suka shiga kokawa yana qoqarin riqe kan motar tana fizgewa, abin yazo masa a bazata gashi sun rigada sun hau titi cikin taimakon Allah ya hankadeta ya samu ya riqe kan motar daya kwace masa saura qiris su afkawa murhun wata me qosai ga mutane a gurin sun baibayeta dan har seda ya ture mutum biyu Allah ya rufa asiri basu ji ciwo ba suka miqe da sauri suka matsa daga gurin. Motar na tsayawa ya kasheta gaba daya ya zare muqullin kafin ya juya ya zabga mata wani lafiyayyen mari da seda jinta da ganinta suka dauke na wani lokaci kafin ta fasa qara saboda gigitaccen zafin daya ziyarci kwakwalwarta.
"Ke wace irin mahaukaciya ce Umaimah, me kike shirin yi? Kashe mu kike so kiyi kome akan Titi zaki gwada wannan haukar?" Ya fada cikin fushi yana kallonta tuni idanunsa sunyi jaa saboda bacin rai haka jijiyar kansa sun tashi rudu rudu alamun ya kai qololuwar bacin rai kenan. Umaimah ko bata iya bashi amsa ba kururuwa kawai takeyi saboda radadin Azabar marin daya kwasa mata, yaja tsaki kamar ze tsinke harshensa kafin ya balle murfin motar ya fita. Be bi takan masu motocin da suka tsatstsaya wasu na zaginsa wasu na neman jin ba'asin abinda ya faru ba ya wuce Gurin mutanen daya afkawa sunyi cirko cirko suna kallon motar tsabar bacin rai ya kasa bude baki yayi musu magana se hade hannayensa biyu yayi alamar ban haquri, wani dan dattijo da yazo siyan qosan ya matsa kusa dashi, ya daga kafadarsa. Akan idonsa ta kama Sitiyarin dan yana daya tsallaken lokacin cikin tausasa murya yace
"Kayi haquri kaji Dana, su Mata wani lokacin ka kan rasa inda hankali da tunaninsu yake tafiya, dukda bansan meya hadaku ba amma tayi wauta. Ka jaku a hankali ku tafi gida koma menene ku warware ka kuma kula karka bari ta sake samun damar maimaita abinda tayi yanzu domin ba daban Allah ya taqaita ba qila da yanzu wata maganar akeyi ba wannan ba Allah kadai yasan Adadin mutanen da hatsarin nan ze ritsa dasu".
Dakya ya iya cewa mutumin
"Nagode Baba" kafin ya juya ya shiga motar, Umaimah dake kuka kamar wadda ake zarewa rai ta dago ta kalleshi, ya kunna motar yana fara tafiya ta sake yunqura zata kama sitiyarin be bata lokaci ba ya riqe motar da hannu daya ya sake zabga mata wani marin da daya hannun
"Na rantse da Allah kika sake kwata mun hauka sena nuna miki na fiki rashin hankali, budeki zanyi ki fada kan Titin mota tabi ta kanki kowa ya huta tunda abinda kike nema kenan" ya fada cikin bacin rai ba tareda ya kalleta ba.
Cikin kukan radadin Azabar Marin data sha tace
"Ai wallahi sedai mu mutu tare dan na grantse da Allah babu wata mace data isa ka hadani da ita, duk kuma wadda tayi gigin shigowa rayuwarmu ka tabbata cikin biyu se daya ta faru, ko dai ita ta mutu ko kai ka mutu idan yaso gaba dayan mu muyi Asara" taci gaba da kuka wiwi dan jin fuskarta takeyi kamar ya watsa mata tafasashshen ruwan zafi. Khalil kuwa dariya ma maganar tata ta bashi dan haka ya dara kadan kafin ya kalleta yace
"Ai Hajiya Ibrahim me haquri ne wallahi saboda tunda naji halayyar yarinyar nan a bakin iyayenta na tabbatar da ba qaramin haquri yake dashi ba da aka dauki wannan lokaci babu wanda yaji kansu kinga kuwa yanzu tunda ya nuna yana da buqatar qari babu me hanashi, zan samu Alhaji Garba da Alhaji Shehu se muji ta bakin Ibrahim din inda za'aje masa neman auran, Allah ya tabbatar da Alkairi yasa zamu gani".
Guraren sha daya da rabi Jamia ta miqe zata tafi dan tana da duty a Asibiti sha biyu zata karba, tare suka fita da Anty Amina datace itama zata koma gida dan babu abinda tayi kafin ta fito nan suka bar Jalilah da zata wuni tana sake jaddada musu kowa ta hado gudummawarta su fara hada lefe Jamila na mata tsiyar ita da yar dakin nata yau kuma itace ja gaba a kan qaro mata abokiyar zama suka fita suna dariya.
Turus sukayi a compound gurin da Khalil yake ajiye motoci, cikin kaduwa Anty Amina ta shiga kwalawa Sammani kira se gashi nan kamar an jefoshi ya fado gurin.
KHALIL
Tun qarfe bakwai ya shirya saboda zeje Qunchi, suna aikin gina makarantar kwaleji ya manta shaf be sanar mata da fitar safe zeyi ba dan haka bayan ya gama shirinsa dakansa ya tafasa ruwan zafi ya hada shayi yasha da sauran Gurasar jiya da sukayi ya dumamata. Yana cikin karyawar Ruqayya ta shiga kitchen din, cikin girmamawa ta gaidashi ya amsa yana tambayarta ko Umaiman ta tashi tace masa Eh yanzun ma ita zata damawa Kunun Gyada dan haka ya fita daga kitchen din ya wuce dakinta na qasa. Tana zaune akan gadon ta jingine bayanta da Allon gadon tana danna waya ya shiga ta dago ta kalle shi tareda amsa sallamar da yayi kafin ta mayar da kai tana ci gaba da danna wayar.
A gaban mudubi ya tsaya yana kallonta, gani yayi ta kumbura tun daga fuskarta har zuwa yatsun qafarta dan haka ya matsa kan gadon ya danna qafarta da yatsun hannunsa ta janye qafar tana ya mutsa fuska kafin ta gaidashi a hankali. Be amsa ba ya zauna gefenta yana cewa
"Meya sameki haka, kinga yanda kika kumbura gaba daya kuwa? Amma jiya da dare naga ba haka kike ba".
Baki ta dan tabe kafin tace
"Nima haka na tashi na ganni ai"
"Kuma shine kike zaune ba zaki kirani muje Asibiti ba, ina ne yake miki ciwo?" Ya fada yana miqewa tsaye seta kalle shi tace
"Nifa lafiya ta qalau inda ina jin wani ciwo ai da na tafi Asibitin da kaina, kuma kumburi daman in ciki ya tsufa ai mutum yana yi ba wani sabon abu bane"
"Amma ba irin wannan ba, duk cikin da kikayi baki taba kumbura haka ba ki tashi kawai muje Asibiti su duba ki idan sun tabbatar da babu wata matsala sannan zan yarda" ya sake fada yana janyo Hijabinta da tayi sallah ta bari akan Sallayar. Baki ta zumbura tana zaune bata da niyyar tashi kuma bata ce masa komai ba se ya ja tsaki yana kallonta cikin bacin rai yace
"Kina da matsala, lafiyar jikinki ma baki damu da ita ba komai se kin saka shirme da shiririta a cikinsa ki tashi nace tun ban bata miki rai ba saboda kin san ni bama wasa da duk abinda ya shafi lafiya".
Dole ta miqe badan taso ba, dakyar taken daga qafa saboda yanda jikinta yayi nauyi, ita kanta tasan kumburin ya zarce na yanda ta saba amma saboda bataji wani ciwo ba kuma da rashin daukar abu da muhimmanci kamar yanda yace din yasa tayi zamanta. A hanya yana ta faman yi mata mita ita kuwa ta doni baki gaba kamar zata tabo glass din motar, daidai zasu shiga Gate din Asibitin watarsa dake ajiye tayi qara, yanda kasan ita aka kira ta kalli wayar da sauri 'Shatunah' sunan data gani yana yawo kenan akan screen din wayar ta kalli Khalil wanda shima kallo daya yayiwa wayar ya dauke kai tamkar bashi ake kira ba a haka ya nemi guri yayi parking motar ya kashe kafin ya dauki wayar tasa da Wallet kuma har sannan yaqi yarda su hada ido da Umaimah data kafa masa nata idanun kamar wata sabuwar Mayya.
Seda ya kusa shiga Reception din Asibitin ya lura da bata biyo shi ba, yawu ya hadiye kafin ya qara hade fuska ya juya gurin Motar, tana ciki hat sannan ta hada uban zuba kamar me naquda se numfarfashi takeyi yanda kasan ana tsira mata allura zata fashe saboda fushi.
"Ki fito muje" ya fada cikin tsare gida kamar tana jiransa kuwa tace
"Bazan fito ba, idan kuma ka isa kazo ka fiddani ta qarfi".
Kallonta yayi ganin yanda fuskarta tayi ya tabbatar da ba abinda ya mata zafi yanzu zata tara masa mutane ta zubar masa da mutunchi a gurin dan haka ya bude sit dinsa ya shiga seda ya kulle motar kafin ya kalleta babu yabo babu fallasa yace
"Ki yi haquri muje a dubaki bayan nan koma menene idan muka koma gida se muyi magana akai".
"Ashe kasan akwai abinda zamuyi magana akai kenan, to jikina ne kuma lafiyata ko nace bazan shiga ba, ko ka gaya mun wace yar iska ce ta kiraka da har kake dangantata da taka ko kuma wallahi yanzu a nan gurin nayi maka Tijarar da baka zata ba" Umaiman ta fada tana kallonsa Khalil dayaji ransa ya baci nan da nan saboda yar iska data kira Humairansa da shi yasaka shima cikin fushi yace mata
"Kin dade bakiyi Tijara ba ko kuwa an gaya miki ina tsoron haukanki ne? Jiki kuma kamar yanda kika fada nakine lafiyarki ce duk abinda ya sameki ke kadai ya shafa bani ba dan nan bada dadewa ba zan dakko wata dake ko babu ke rayuwata zanyi bani da Asara" yana gama fadar haka ya tada motar a tsiyace ya fizgeta ya fice daga Asibitin Umaimah da tayi suman zaune saboda jin abubuwan da yake fada fizgar da yayiwa motar ce ta tabbatar mata da cewar a Raye take kuma gaske ne ba mafarki ba Khalil ne yake fada mata wadannan maganganun.
"Dake ko babu ke zanyi rayuwata bani da Asara" maganar ta caki zuciyarta kamar shigar mashi, cikin azamar da bata san tana da ita ba ta kaiwa Sitiyarin cafka suka shiga kokawa yana qoqarin riqe kan motar tana fizgewa, abin yazo masa a bazata gashi sun rigada sun hau titi cikin taimakon Allah ya hankadeta ya samu ya riqe kan motar daya kwace masa saura qiris su afkawa murhun wata me qosai ga mutane a gurin sun baibayeta dan har seda ya ture mutum biyu Allah ya rufa asiri basu ji ciwo ba suka miqe da sauri suka matsa daga gurin. Motar na tsayawa ya kasheta gaba daya ya zare muqullin kafin ya juya ya zabga mata wani lafiyayyen mari da seda jinta da ganinta suka dauke na wani lokaci kafin ta fasa qara saboda gigitaccen zafin daya ziyarci kwakwalwarta.
"Ke wace irin mahaukaciya ce Umaimah, me kike shirin yi? Kashe mu kike so kiyi kome akan Titi zaki gwada wannan haukar?" Ya fada cikin fushi yana kallonta tuni idanunsa sunyi jaa saboda bacin rai haka jijiyar kansa sun tashi rudu rudu alamun ya kai qololuwar bacin rai kenan. Umaimah ko bata iya bashi amsa ba kururuwa kawai takeyi saboda radadin Azabar marin daya kwasa mata, yaja tsaki kamar ze tsinke harshensa kafin ya balle murfin motar ya fita. Be bi takan masu motocin da suka tsatstsaya wasu na zaginsa wasu na neman jin ba'asin abinda ya faru ba ya wuce Gurin mutanen daya afkawa sunyi cirko cirko suna kallon motar tsabar bacin rai ya kasa bude baki yayi musu magana se hade hannayensa biyu yayi alamar ban haquri, wani dan dattijo da yazo siyan qosan ya matsa kusa dashi, ya daga kafadarsa. Akan idonsa ta kama Sitiyarin dan yana daya tsallaken lokacin cikin tausasa murya yace
"Kayi haquri kaji Dana, su Mata wani lokacin ka kan rasa inda hankali da tunaninsu yake tafiya, dukda bansan meya hadaku ba amma tayi wauta. Ka jaku a hankali ku tafi gida koma menene ku warware ka kuma kula karka bari ta sake samun damar maimaita abinda tayi yanzu domin ba daban Allah ya taqaita ba qila da yanzu wata maganar akeyi ba wannan ba Allah kadai yasan Adadin mutanen da hatsarin nan ze ritsa dasu".
Dakya ya iya cewa mutumin
"Nagode Baba" kafin ya juya ya shiga motar, Umaimah dake kuka kamar wadda ake zarewa rai ta dago ta kalleshi, ya kunna motar yana fara tafiya ta sake yunqura zata kama sitiyarin be bata lokaci ba ya riqe motar da hannu daya ya sake zabga mata wani marin da daya hannun
"Na rantse da Allah kika sake kwata mun hauka sena nuna miki na fiki rashin hankali, budeki zanyi ki fada kan Titin mota tabi ta kanki kowa ya huta tunda abinda kike nema kenan" ya fada cikin bacin rai ba tareda ya kalleta ba.
Cikin kukan radadin Azabar Marin data sha tace
"Ai wallahi sedai mu mutu tare dan na grantse da Allah babu wata mace data isa ka hadani da ita, duk kuma wadda tayi gigin shigowa rayuwarmu ka tabbata cikin biyu se daya ta faru, ko dai ita ta mutu ko kai ka mutu idan yaso gaba dayan mu muyi Asara" taci gaba da kuka wiwi dan jin fuskarta takeyi kamar ya watsa mata tafasashshen ruwan zafi. Khalil kuwa dariya ma maganar tata ta bashi dan haka ya dara kadan kafin ya kalleta yace