Sashe 86
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da suka koma gida kuwa yasha mita yayi mata banza dan kanta tayi shiru, doka ya kafa mata ta bacci qarfe goma kuma ta kashe wayarta ta bashi. Yanda ya hade fuska yana gaya mata dokar dole ta amsa a lokacin dan yanzu lallabashi takeyi bata so nan kusa ace an sake samun wata matsalar musamman da take da buqata a gurinsa so take a kwana biyu komai yayi daidai ta nemi abinda take so.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 37
Motar ya koma yana tunanin wanene wannan din kuma me yake dauka? Ganin bashi da me bashi amsa ya saka ya mayar da hankalinsa kan tuqin da yakeyi yana yi yana lallashin Hadiza dake kuka, har qofar gidansu ya kaita, be barta ta fita ba seda ya tabbatar ta sakko kuma ta dena kukan da takeyi ya lallabeta ya kuma tabbatar mata da In sha Allahu ze aureta amma tayi haquri ta bashi lokaci kuma ta ringa musu Addu'a.
"Ina son Matata sosai bansan ta yanda zan kalleta nace mata zan qara aure ba" ya fada yana kallon Hadizan ta buga masa wata harara tareda jan tsaki kafin ta kama murfin motar ta fice batareda ta tanka masa ba ya rakata da Murmushi, haega Allah yana son Hadiza kodan sanyin Halinta da kulawar da take bashi kuma tafi sonsa akan wanda yake mata yasan zata riritashi ta kiyaye bacin ransa to amma damuwar ta inda ze tunkari ita Uwargidan da wannan magana dan ta Hajiya da duk wani da ze iya kawo cikas me sauqi ne.
Gaba ya danyi ya bar qofar gidan nasu ya samu guri ya tsaya. Jalila ya kira ringing biyu ta daga tana cewa
"Aa Hussaina yau ka tuna dani kenan"
"Dama na taba cewa na manta dake ne?" Ya bata amsa se tayi yar dariya tace
"Toh ai muj sallamawa Maman Mu'ayyad kai, ta tsare gaba ta tsare baya Hajiya kadai ake bawa damar ganinka da magana dakai sanda taso mu kuwa idan mun gaji da neman ka sedai mu kirata mu bada saqo"
"Kina da Matsala Jalila yanzu duk meya kawo wannan qorafin" ya katseta, seta sake cewa
"Gaskiya ce kawai ba qorafi ba gaba daya ka maqalewa Mace baka da lokacin kowa yanzu se nata duk sunkasa fasa maka ne ni kasan bazanyi shiru ba"
Qaramin tsaki yaja yace
"Mutum na cikin wata damuwar zaki zo ki qara masa, kiranki nayi ki bani shawara amma zaki cikamun kunne da mita haba" yanda yayi maganar cikin alamun abu na damunsa ya sakata sassauta murya tace
"Yi haquri toh dan qanina meya faru, wace damuwa kake ciki kuma shawarar me zamuyi?"
"Aure nake so na qara Jalila" ya bata amsa kaitsaye dan bayaso aja maganar se tayi shiru kusan minti daya kafin ta numfasa tace
"Aure Khalil, ka gayawa Hajiya kuma ta yarda?"
"Ban gayawa kowa ba shawararki nake nema me kike gani akai nayi ko Aa?" Ya mayar mata da wata tambayar se Jalila ta ajiye numfashi tace
"Wannan ai ba maganar da kai tsaye zance maka yi ko karkayi bace. Qarin aure yana zuwa ne akan abu biyu, buqatuwar yin hakan ko kuma yazo maka baqatatan daga Allah dukda dukka biyun nufin Allah ne amma kashin farko da niyya kuma mutum yaso yin hakan kai wannene naka a ciki?"
"Nima ban sani ba" bata amsa kamar me shirin fasa kuka, baya so Hadiza ta zarge shi da laifin yaudara dukda wani mummunan abu be taba shiga tsakaninsu ba ze iya cewa ko hannunta be taba ba sedai bisa kuskure amma dukda haka bazeso haqqin Soyayyar da takeyi mishi ya kamashi ba kuma tsoron sa Allah tsoronsa yanda ze tunkari Umaimah musamman da yanzu suke zaune lafiya babu wata matsala a tsakaninsu. Dariyar Jalila ce ta dawo dashi hayyacinsa yaji tana cewa
"Dan qanina maganar nan bata waya bace, ka samu lokaci kazo mu tattauna in fahimceka kafin nasan abin da zan baka shawara akai"
Yayi Na'am da shawararta dan haka yace mata
"Shikenan zanzo, amma dan Allah kar wanda yasan wannan maganar ko da Hajiya ce na gaya miki ban sanar da kowa ba seke, ba kuma naso suji se na gama yanke shawarar yi ko akasin haka"
"Haba kaima kasan babu meji, ko mun taba kashewa mun rufe kaji wani ya tada maganar?"
"Naga kin koyi tsogumi ne yanzu shiyasa musamman tunda kun sakawa Matata ido qila ku kuke ta mata Addu'a har naji abin ya darsu a zuciyata" se Jalila ta saka dariya tana cewa
"Ai ko ace muna da wata matsala da Matarka bazamu goyi bayan haka kawai kayi mata kishiya ba indai ba da wani babban dalili ba ballantana ma babu, ka samu lokacin ka shigo se mutattauna kaji" daga haka sukayi sallama ya tada motar yaci gaba da tafiya.
Office ya koma amma gaba daya ranar be iya gane abinda yakeyi ba dan hankalinsa ya rabu da yawa.
Kwana biyu a tsakani cikin damuwa yayi su, tunanin yanda ze magance Matsalar Hadiza yakeyi gashi tayi fushi koya kirata a waya se taga dama zata dauka har tana cewa ashe yana da lokaci daman niyyar kiranta ne kawai bashi dashi se yanzu se ya ringaji toh kawai ya rabu da ita mana salin alin su rabu ga mafita ya samu amma yana tsoron haqqinta, yasan zafin soyayya tunda yanzu haka cikin karbar gashinta yake idan har haka Hadiza takeji a kansa idan ya barta beyi mata Adalci ba.
Umaimah kanta ta lura da rashin walwalarsa data tambaye shi yace mata bayajin dadi ne ga kuma ayyuka da suka yi masa yawa ta ringa mitar ai shi yake dorawa kansa me yasa duk Architects din da suke a kamfaninsu ace duk wani babban aiki shi ze ringa kula dashi ai se a bawa wasu dama. Sanda take maganar kallonta kawai yayi, shi kam Umaimah ta dena bashi mamaki yanzu dan duk abinda tayi yana tsammanin zatayi wanda ya fishi, yanzu ita ba Jin dadinta bane ace Allah ya daukaka shi cikin daruruwa shi aka zaba Aa mita takeyi akan me yasa akayi hakan toh Allah ya rufa Asiri, shidai Tsuntsun soyayyar sa beyi masa Adalci ba daya rasa inda ze sauka se akan wannan butsuwar yarinyar.
Be samu zama da Jalila ba se bayan sati daya ranar Weekend yacewa Umaimah ta shirya suje gidan dukda yasan ba zuwa zatayi ba latsine, ya rasa me yasa yanzu take ja baya da yan uwan nasa wanda sam farkon auransu ba haka bane sosai suke shiri take daukarsu tamkar su Yaya Naziyya amma tunda ta haihu abubuwa suka chanza, shi kansa gidan Hajiyar da take yawan zuwa ta rage sedai ta kirata a waya su gaisa wannan dai babu fashi kullum ta Allah seta kirata.
Umaimah ko daya gaya mata zasuje din kaitsaye tace bazata ba saboda akwai sunan Mariya maqociyarsu da za'ayi a ranar Amaryace matar qanin Mijin Maman Hibban da sun fara zama a wata unguwa barayi suka damesu shine ya gina filin jikin gidan Maman Hibban din inda sukayi Suna suka tare a anan.
Ya gama shirinsa tsaf ze fita tana zaune a palour kanta ne yake sara mata haka a kwanakin take yawan fama da ciwon kai wani lokacin harda jiri ta gayawa Khalil yace yawan kallon waya da takeyi gashi bata samun isashshen bacci ta raba dare Online su suka saka shiko ya dena mata magana duk yanda tayi daidai ne tunda tana masa abinda yake so idan ta gama can taje ita ta sani.
"Baka bani kudin barka ba toh zaka fita" Umaimah ta fada jin yana mata sallama, se ya kalleta yace
"Kudin barka kuma? Ina kudin da kike kaiwa can gidan duk sati da kikace kuna tarawa ne saboda irin haka idan hidima ta tasowa wani se a bashi a madadin matan unguwa?"
Baki ta tura tace
"Toh ai wancan na gidauniya ne wannan kuma personal ne da zan bata"
"Ai Namiji kika ce ta haifa ki duba cikin rigunanku ki kai mata ko ki dauka a kudin dana baki jiya ni banda kudi yanzu" yana gama fada ya saka kai ya fita yana mamakinta. Jiyan nan dubu talatin ya bata wai zata siyi kayan gyara, sannan duk satin duniya se ya bata dubu biyu ta zubin gidauniya data ce banda idan ya samu kudi haka kawai ma bata yakeyi ko idan zata fita unguwa duk suna ina da seya bata kudin wata barka ai bashi ya aiketa ba.
Da dai Umaimah bazatace ya bata kudi ba duk abinda yaga dama ya bata zata karba tayi godiya wani lokacin har tace ya rage saboda tana tausayinsa amma yanzu ta zama yar fashi daga zaune. Bill ne take masa harda na banza, ana zaune lafiya zata qirqiro abu tace tana so idan yaqiyi kuma ta ringa fushi da baqin rai kenan da mita har se ya mata abinda take so yanzu a ritsin nan Iphone 13 ta saka seda ya siya mata shi yana fama da X tun kafin auransu be chanza ba ita kuwa 12 take riqewa rana daya tace duk qawayenta 13 ce dasu dole ya karbi ta hannunta ya cika aka bata wata.
Umaimah kuwa harara ta rakashi da ita babu arziqin a dawo lafiya tunda ya hanata kudin barka. Shifa yace dan ita yake nema a da tausaya masa takeyi ganin yana da dawainiya dayawa akan sa amma tunda Rufaida ta wayar mata dakai ta dena. Ita ta koya mata dabarun karbar kudi a hannunsa dukda kota karba ba wata tsiyar take dasu ba sedai rantawa qawaye da zubin Adashi se siyi banza siyi wofi abin kirki kadai da zata ce tana siya shine kayan gyaran jiki wannan ko bata wasa dasu dan da jikin take yaqarsa tayi iskancinta son rai kuma taci riba.
Kiran wayarta ne ya dakatar da ita ta janyota, Rufaida ce tana dagawa tace
"Madam kin shirya mu shiga gidan sunan kuwa?"
"Na dauka seda yamma ai" Umaimah ta bata amsa se tace mata
"Aa zamu shiga yanzu mana muga koda abinda zamu kama musu"
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 37
Motar ya koma yana tunanin wanene wannan din kuma me yake dauka? Ganin bashi da me bashi amsa ya saka ya mayar da hankalinsa kan tuqin da yakeyi yana yi yana lallashin Hadiza dake kuka, har qofar gidansu ya kaita, be barta ta fita ba seda ya tabbatar ta sakko kuma ta dena kukan da takeyi ya lallabeta ya kuma tabbatar mata da In sha Allahu ze aureta amma tayi haquri ta bashi lokaci kuma ta ringa musu Addu'a.
"Ina son Matata sosai bansan ta yanda zan kalleta nace mata zan qara aure ba" ya fada yana kallon Hadizan ta buga masa wata harara tareda jan tsaki kafin ta kama murfin motar ta fice batareda ta tanka masa ba ya rakata da Murmushi, haega Allah yana son Hadiza kodan sanyin Halinta da kulawar da take bashi kuma tafi sonsa akan wanda yake mata yasan zata riritashi ta kiyaye bacin ransa to amma damuwar ta inda ze tunkari ita Uwargidan da wannan magana dan ta Hajiya da duk wani da ze iya kawo cikas me sauqi ne.
Gaba ya danyi ya bar qofar gidan nasu ya samu guri ya tsaya. Jalila ya kira ringing biyu ta daga tana cewa
"Aa Hussaina yau ka tuna dani kenan"
"Dama na taba cewa na manta dake ne?" Ya bata amsa se tayi yar dariya tace
"Toh ai muj sallamawa Maman Mu'ayyad kai, ta tsare gaba ta tsare baya Hajiya kadai ake bawa damar ganinka da magana dakai sanda taso mu kuwa idan mun gaji da neman ka sedai mu kirata mu bada saqo"
"Kina da Matsala Jalila yanzu duk meya kawo wannan qorafin" ya katseta, seta sake cewa
"Gaskiya ce kawai ba qorafi ba gaba daya ka maqalewa Mace baka da lokacin kowa yanzu se nata duk sunkasa fasa maka ne ni kasan bazanyi shiru ba"
Qaramin tsaki yaja yace
"Mutum na cikin wata damuwar zaki zo ki qara masa, kiranki nayi ki bani shawara amma zaki cikamun kunne da mita haba" yanda yayi maganar cikin alamun abu na damunsa ya sakata sassauta murya tace
"Yi haquri toh dan qanina meya faru, wace damuwa kake ciki kuma shawarar me zamuyi?"
"Aure nake so na qara Jalila" ya bata amsa kaitsaye dan bayaso aja maganar se tayi shiru kusan minti daya kafin ta numfasa tace
"Aure Khalil, ka gayawa Hajiya kuma ta yarda?"
"Ban gayawa kowa ba shawararki nake nema me kike gani akai nayi ko Aa?" Ya mayar mata da wata tambayar se Jalila ta ajiye numfashi tace
"Wannan ai ba maganar da kai tsaye zance maka yi ko karkayi bace. Qarin aure yana zuwa ne akan abu biyu, buqatuwar yin hakan ko kuma yazo maka baqatatan daga Allah dukda dukka biyun nufin Allah ne amma kashin farko da niyya kuma mutum yaso yin hakan kai wannene naka a ciki?"
"Nima ban sani ba" bata amsa kamar me shirin fasa kuka, baya so Hadiza ta zarge shi da laifin yaudara dukda wani mummunan abu be taba shiga tsakaninsu ba ze iya cewa ko hannunta be taba ba sedai bisa kuskure amma dukda haka bazeso haqqin Soyayyar da takeyi mishi ya kamashi ba kuma tsoron sa Allah tsoronsa yanda ze tunkari Umaimah musamman da yanzu suke zaune lafiya babu wata matsala a tsakaninsu. Dariyar Jalila ce ta dawo dashi hayyacinsa yaji tana cewa
"Dan qanina maganar nan bata waya bace, ka samu lokaci kazo mu tattauna in fahimceka kafin nasan abin da zan baka shawara akai"
Yayi Na'am da shawararta dan haka yace mata
"Shikenan zanzo, amma dan Allah kar wanda yasan wannan maganar ko da Hajiya ce na gaya miki ban sanar da kowa ba seke, ba kuma naso suji se na gama yanke shawarar yi ko akasin haka"
"Haba kaima kasan babu meji, ko mun taba kashewa mun rufe kaji wani ya tada maganar?"
"Naga kin koyi tsogumi ne yanzu shiyasa musamman tunda kun sakawa Matata ido qila ku kuke ta mata Addu'a har naji abin ya darsu a zuciyata" se Jalila ta saka dariya tana cewa
"Ai ko ace muna da wata matsala da Matarka bazamu goyi bayan haka kawai kayi mata kishiya ba indai ba da wani babban dalili ba ballantana ma babu, ka samu lokacin ka shigo se mutattauna kaji" daga haka sukayi sallama ya tada motar yaci gaba da tafiya.
Office ya koma amma gaba daya ranar be iya gane abinda yakeyi ba dan hankalinsa ya rabu da yawa.
Kwana biyu a tsakani cikin damuwa yayi su, tunanin yanda ze magance Matsalar Hadiza yakeyi gashi tayi fushi koya kirata a waya se taga dama zata dauka har tana cewa ashe yana da lokaci daman niyyar kiranta ne kawai bashi dashi se yanzu se ya ringaji toh kawai ya rabu da ita mana salin alin su rabu ga mafita ya samu amma yana tsoron haqqinta, yasan zafin soyayya tunda yanzu haka cikin karbar gashinta yake idan har haka Hadiza takeji a kansa idan ya barta beyi mata Adalci ba.
Umaimah kanta ta lura da rashin walwalarsa data tambaye shi yace mata bayajin dadi ne ga kuma ayyuka da suka yi masa yawa ta ringa mitar ai shi yake dorawa kansa me yasa duk Architects din da suke a kamfaninsu ace duk wani babban aiki shi ze ringa kula dashi ai se a bawa wasu dama. Sanda take maganar kallonta kawai yayi, shi kam Umaimah ta dena bashi mamaki yanzu dan duk abinda tayi yana tsammanin zatayi wanda ya fishi, yanzu ita ba Jin dadinta bane ace Allah ya daukaka shi cikin daruruwa shi aka zaba Aa mita takeyi akan me yasa akayi hakan toh Allah ya rufa Asiri, shidai Tsuntsun soyayyar sa beyi masa Adalci ba daya rasa inda ze sauka se akan wannan butsuwar yarinyar.
Be samu zama da Jalila ba se bayan sati daya ranar Weekend yacewa Umaimah ta shirya suje gidan dukda yasan ba zuwa zatayi ba latsine, ya rasa me yasa yanzu take ja baya da yan uwan nasa wanda sam farkon auransu ba haka bane sosai suke shiri take daukarsu tamkar su Yaya Naziyya amma tunda ta haihu abubuwa suka chanza, shi kansa gidan Hajiyar da take yawan zuwa ta rage sedai ta kirata a waya su gaisa wannan dai babu fashi kullum ta Allah seta kirata.
Umaimah ko daya gaya mata zasuje din kaitsaye tace bazata ba saboda akwai sunan Mariya maqociyarsu da za'ayi a ranar Amaryace matar qanin Mijin Maman Hibban da sun fara zama a wata unguwa barayi suka damesu shine ya gina filin jikin gidan Maman Hibban din inda sukayi Suna suka tare a anan.
Ya gama shirinsa tsaf ze fita tana zaune a palour kanta ne yake sara mata haka a kwanakin take yawan fama da ciwon kai wani lokacin harda jiri ta gayawa Khalil yace yawan kallon waya da takeyi gashi bata samun isashshen bacci ta raba dare Online su suka saka shiko ya dena mata magana duk yanda tayi daidai ne tunda tana masa abinda yake so idan ta gama can taje ita ta sani.
"Baka bani kudin barka ba toh zaka fita" Umaimah ta fada jin yana mata sallama, se ya kalleta yace
"Kudin barka kuma? Ina kudin da kike kaiwa can gidan duk sati da kikace kuna tarawa ne saboda irin haka idan hidima ta tasowa wani se a bashi a madadin matan unguwa?"
Baki ta tura tace
"Toh ai wancan na gidauniya ne wannan kuma personal ne da zan bata"
"Ai Namiji kika ce ta haifa ki duba cikin rigunanku ki kai mata ko ki dauka a kudin dana baki jiya ni banda kudi yanzu" yana gama fada ya saka kai ya fita yana mamakinta. Jiyan nan dubu talatin ya bata wai zata siyi kayan gyara, sannan duk satin duniya se ya bata dubu biyu ta zubin gidauniya data ce banda idan ya samu kudi haka kawai ma bata yakeyi ko idan zata fita unguwa duk suna ina da seya bata kudin wata barka ai bashi ya aiketa ba.
Da dai Umaimah bazatace ya bata kudi ba duk abinda yaga dama ya bata zata karba tayi godiya wani lokacin har tace ya rage saboda tana tausayinsa amma yanzu ta zama yar fashi daga zaune. Bill ne take masa harda na banza, ana zaune lafiya zata qirqiro abu tace tana so idan yaqiyi kuma ta ringa fushi da baqin rai kenan da mita har se ya mata abinda take so yanzu a ritsin nan Iphone 13 ta saka seda ya siya mata shi yana fama da X tun kafin auransu be chanza ba ita kuwa 12 take riqewa rana daya tace duk qawayenta 13 ce dasu dole ya karbi ta hannunta ya cika aka bata wata.
Umaimah kuwa harara ta rakashi da ita babu arziqin a dawo lafiya tunda ya hanata kudin barka. Shifa yace dan ita yake nema a da tausaya masa takeyi ganin yana da dawainiya dayawa akan sa amma tunda Rufaida ta wayar mata dakai ta dena. Ita ta koya mata dabarun karbar kudi a hannunsa dukda kota karba ba wata tsiyar take dasu ba sedai rantawa qawaye da zubin Adashi se siyi banza siyi wofi abin kirki kadai da zata ce tana siya shine kayan gyaran jiki wannan ko bata wasa dasu dan da jikin take yaqarsa tayi iskancinta son rai kuma taci riba.
Kiran wayarta ne ya dakatar da ita ta janyota, Rufaida ce tana dagawa tace
"Madam kin shirya mu shiga gidan sunan kuwa?"
"Na dauka seda yamma ai" Umaimah ta bata amsa se tace mata
"Aa zamu shiga yanzu mana muga koda abinda zamu kama musu"