Sashe 92
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ni fa daman tun Asali ke na fara so banma san ya akayi na koma kanta ba abin kamar tayi mun Asiri kuma daya karye na rabu da ita kawai naji tsoron idan na dawo miki bazaki karbeni ba saboda Aminiyarki ce shi yasa na haqura daku gaba daya" Khalil ya sake sakin wani dialogue din ganin ta sakawa guri daya ido tana faman doka murmushi ai kuwa tayi saurin kallonsa ya kashe mata ido daya ya sake cewa
"Eh mana kema ai kina sona ko tunda gashi kin kasa haqura kina so ki kwatoni daga gurin Hadiza ta qarfin tuwo" yayi maganar cikin sigar tsokana yana kallonta ya rausayar dakai irin taji kunyar nan har sannan batayi magana ba sedai murmushi dan haka ya sake cewa
"Kinyi shiru baki ce komai ba ko baki son nawa ne? Kinyi shiru kiyi magana" ya sake fada yana leqa fuskarta data sunkuyar qasa, seta dago tana hade fuskarta daga murmushin da takeyi tace
"Ina sonka mana kaima ka sani kuma ni daman saboda na sameka ya saka nayi abinda nayi. Amma dukda haka bazan yarda da dadin bakin ka ba dan jiyan nan na gama jin kana gaya mata zaka kaini gurin DSS waya sani ko yanzun ma kayi report?
To dai koma yayane na gaya maka kuma zan maimaita idan ka saka an kamani kamar ka qarawa wuta fetur ne dan na raba copys na hotunan nan dama wasu da baku san dasu ga ga Qawayena da abokanaina. Ko yanzu da zan taho seda na gaya musu inda zanje kuma dakai zan hadu idan wani abu ya sameni karsu jira komai su sake su a Internet".
'Dum' qirjinsa ya buga a zuciyarsa yace
"An yanka ta tashi" amma afili qoqari yayi ya daidaita nutsuwarsa yace
"Haba dai kina wata magana kuma ko jiyan da kikaji na fada mata haka nayi ne dan na kwantar mata da hankali bawai dagaske nakeyi ba dan haka ki kwantar da hankalinki infact ni koda ace kin fitar da hotunan da kike fada babu abinda ze shafeni saboda ni namiji ne kin sani me hausawa suke cewa ai duk abinda mukayi Ado ne kawai dai ita nake jin tausayi a matsayinta na Mace"
"Oh haka ma kace baka tsoron Abokanan huldarka su gani ko yan uwanka? Bama wannan ba matarka da take da bala'in kishi idan ta gani me kake tunanin ze faru?" Khausar ta fada fuskarta ta kasa boye mamakin jin yace wai babu abinda ze dame shi ita duk kanta ya kulle ma. Jiya fa ya rikice a waya amma yanzu ya ringa nuna abin be dame shi ba kuma har kan fuskarsa bata ga alamar qarya a abinda yake fada ba, maganar sace ta katse mata tunani yace
"A ina kika san Matata da har kika san tana da Kishi?"
Seta harareshi qasa qasa kafin ta danna wayarta ta nemo number Umaimah data kwafa ranar daya nuna musu hotunanta a waya ta juya masa wayar tana cewa
"Ko ba wannan ce Number taba? Na tabbata idan taga hotunan nan seka gwammace kida da karatu dan kaida kwanciyar hankali har abada".
Dariyar da shikansa ya rasa ta mecece yayi kafin cikin tsananin dauriya daga rudun ganin number Umaimah a wayarta yace
"Toh ko zaki gwada aika mata yanzu ko gani? Kinga naga alamar bazamu daidaita ni abinda nake miki magana akai daban ke kuma kina wani shirme daban, kina zaton zakiyi blackmailing dina ne kiringa mun barazana da wata Matata ko wani abu to bari kiji ki koma ki sake shiri dan wannan bazeyi aiki ba, maganar soyayyar ma kuma na fasa tunda naga ba ita bace a gabanki na barki kije kici gaba da shirmen da kike ganin dabara ce a gurinki" ya fada yana miqewa tsaye zuciyarsa na wani tsalle akan fargabar abinda ze biyo bayan hargagin nasa amma ga mamakinsa se yaga itama ta miqe tsaye tana kallonsa tace
"Ta yaya zan yarda gaskiya kake fada mun ba yaudarata kakeyi ba?"
Ajiyar zuciya ya sauke a boye kafin shima ya kalleta yace
"Kibi abinda zuciyarki tafi yarda akai".
Seta koma ta zauna ganin haka shima yaja kujerarsa ya zauna yana Addu'a a zuciyarsa, shiru sukayi na wani lokaci kafin ta bude baki tace
"Ni ba soyayya ko bata lokaci nake so muyi ba Sonka nakeyi da aure dan haka idan ka shirya belin kanka a shirye nake ko a gobe ka tura a nema maka aurena ni kuma nayi maka Alqawarin zan goge duk wani hoto da video na gurina da gurin wadanda na bawa Ajiya"
"Well, ni idan zan aureki zan aureki ne a ra'ayin qashin kaina badan wata barazanarki ba, sannan idan dan wannan nema ai kin rigada kin lalata abin tunda har kin turawa wasu a matsayin Ajiya ko? Ta yaya zan yarda suma basu nunawa wasu ba kinga kenan idan ina gudun fitarsu ne magana ta qare kin rigada kin fitar dasu tunda bake kadai kika mallake su ba" Khalil ya fada yana tsareta da ido, shikansa yayi mamakin yanda ya iya dakewa yake magana ba tareda ta gano shi ba.
Duburburcewa tayi cikin in ina tace
"Toh ai toh nasan wadanda na bawan zasu boye ba zasu nunawa kowa ba, kuma ma ni da kaina na boye su kansu basu san menene a ciki ba"
"Amma dazu fa kikace kin gaya musu zaki hadu dani idan wani abu ya sameki nine kinga kenan sun san abinda yake faruwa ko?" Ya sake jefa mata wata tambayar yana kallonta kamar wani Jami'in tsaro seta hade rai ta miqe tana cewa
"Saboda kaga na tsaya muna magana shine har kake nema ka titsiyeni ka raina mun hankali ko? Toh shikenan kaje zakaga abinda ze biyo baya, zakazo kana dana sani da bashida amfani tunda har ka kasa amfani da damar dana baka. Kuma wallahi kaci sa'a ina sonka ne amma a yanda na quduri daidaita rayuwar Hadiza dan saboda kaine na rangwanta mata abin ya tsaya iya haka amma tunda bakaga abinda nayi maka ba, zaka gwammaci kida da karatu" ta dauki jakarta da wayarta dake ajiye zata juya shima ya miqe yana cewa
"Na gaya miki ni bana tsoron ki yada koma menene amma ki sani kin dabawa kanki wuqa kuma ita ramuwar gayya akace tafi ta gayya zafi. Idan kin sabayiwa mutane haka kina cin banza ki tabbatar wannan karon kin tabo tsuliyar Dodo dan Khausar idan bakiyi wasa ba seba batar dake" yana gama gaya mata haka ya juya ya wuceta fuuu kamar iska ya barta tsaye tana binsa da kallo daidai sannan.
Khausar
Sosai tsoron yanayin da Khalil din yayi magana ya kamata daman kuma ta fuskanci kamar ya gano duk wani shirinta amma yanzu yaya zatayi? Batar da ita fa yace zeyi ta tabbatar da kuma ze iya tunda komai kudi ne yake aiki a yanzu.
Komawa tayi ta zauna ta dauki wayarta dake ajiye ta shiga kiran qawarta Shema wadda da ita suka qulla duk wani shiri ita ce ma ta hada ta da wanda yayi mata hotunan da Video
"Ke kamarfa gayen nan ya gama gane shiri na gaba daya fa ya nuna baya jin tsoron ma na saki hotunan ba kamar jiya da nake gaya miki ba" Khausar ta fada bayan da Shema ta daga wayar, tsaki Sheman tayi tace
"Kefa banzace daman ai dole ze nuna miki be damu ba saboda ki karaya ki fasa abinda zakiyi Allah sa dai bake ce ma kikaje kikayi abinda ya gano ki ba"
"Ko daya wallahi nuna mun yayi shi be damu ba ko jiyan ma saboda Hadiza ne kuma ma ashe basa tare yanzu harfa yana maganar daman yana sona kuma ze aureni to fa daga na tambayeshi ya zaayi na gane ba yaudarata yake so yayi ba shine kuma yayi fushi har yana cewa Ze iya batar dani" Khausar ta sake fada se Shema ta buga tsaki me qarfi tace
"Ai daman ke banza ce wai wa ma yace ki hadu dashi daga fara abu jiya har zaki bari ku hadu yau dole ma ya gane bada gaske kike ba, yanzu ya turo miki da kudin da kika nema jiya ne? Seda nace miki idan be turo ba kaitsaye ki aikawa da Matarsa shine ze tabbatar bada wasa kike na amma jiki na rawa daga yace kizo kuyi magana kinje seki shirya tarar abinda ze biyo baya tunda daman idan baka iya kama barawo ba ai shi se ya kamaka"
"Toh yanzu ya zanyi Shema, ni fa batarwar nan daya ce ta daga mun hankali ke kika bani labarin qawarki da haka ta fau da ita fa" Khausar ta sake fada kamar zatayi kuka daga can bangaren Shema tace
"Minal ba shekara biyu kenan babu labarinta se tashin zancen, iyayenta ma da suka gaji da nema Addu'a kawai aka mata sun saddaqar ta mutu amma ita ai babban mutum tayiwa, daman a lokacin seda muka hanata wata qawarta tace mata babu komai itama ta tabayi ta samu kudi sasai dan daman su badan a aure su bane kawai Kudi suke karba a gurin mutanen, aiko randa ta tura masa da Video washe gari ta fita aka dauketa a hanya shikenan qila se a lahira".
Cikin Khausar ne ya bada qarara quuu jin wai a hanya aka dauketa tace
"Karfa nima yanzu kiji babu ni ko kuma yasa a tareni a kwace mun waya kin san komai yana ciki kawai bari in jira kizo mu tafi tare ne kinji dan Allah"
"Ai seda nace ki tura a wayata saboda tsaro ke ga me wayo kika ce Aa, Ai se ki zauna barazana yayi miki kuma kin rufta Allah yasa ma ba labewa yayi yaga yanda zakiyi ba kinga kuwa idan haka ne kina ruwa wallahi ya gano lagonki, ina yaga kudinda ze biya a batar dake banda ma ke sauna ce da har zaki wani tashi hankalinki? Dallah ki kamo hanya ki taho musan yanda zamu gyara shirmen da kikayi" tana gama fada ta kashe wayar.
"Eh mana kema ai kina sona ko tunda gashi kin kasa haqura kina so ki kwatoni daga gurin Hadiza ta qarfin tuwo" yayi maganar cikin sigar tsokana yana kallonta ya rausayar dakai irin taji kunyar nan har sannan batayi magana ba sedai murmushi dan haka ya sake cewa
"Kinyi shiru baki ce komai ba ko baki son nawa ne? Kinyi shiru kiyi magana" ya sake fada yana leqa fuskarta data sunkuyar qasa, seta dago tana hade fuskarta daga murmushin da takeyi tace
"Ina sonka mana kaima ka sani kuma ni daman saboda na sameka ya saka nayi abinda nayi. Amma dukda haka bazan yarda da dadin bakin ka ba dan jiyan nan na gama jin kana gaya mata zaka kaini gurin DSS waya sani ko yanzun ma kayi report?
To dai koma yayane na gaya maka kuma zan maimaita idan ka saka an kamani kamar ka qarawa wuta fetur ne dan na raba copys na hotunan nan dama wasu da baku san dasu ga ga Qawayena da abokanaina. Ko yanzu da zan taho seda na gaya musu inda zanje kuma dakai zan hadu idan wani abu ya sameni karsu jira komai su sake su a Internet".
'Dum' qirjinsa ya buga a zuciyarsa yace
"An yanka ta tashi" amma afili qoqari yayi ya daidaita nutsuwarsa yace
"Haba dai kina wata magana kuma ko jiyan da kikaji na fada mata haka nayi ne dan na kwantar mata da hankali bawai dagaske nakeyi ba dan haka ki kwantar da hankalinki infact ni koda ace kin fitar da hotunan da kike fada babu abinda ze shafeni saboda ni namiji ne kin sani me hausawa suke cewa ai duk abinda mukayi Ado ne kawai dai ita nake jin tausayi a matsayinta na Mace"
"Oh haka ma kace baka tsoron Abokanan huldarka su gani ko yan uwanka? Bama wannan ba matarka da take da bala'in kishi idan ta gani me kake tunanin ze faru?" Khausar ta fada fuskarta ta kasa boye mamakin jin yace wai babu abinda ze dame shi ita duk kanta ya kulle ma. Jiya fa ya rikice a waya amma yanzu ya ringa nuna abin be dame shi ba kuma har kan fuskarsa bata ga alamar qarya a abinda yake fada ba, maganar sace ta katse mata tunani yace
"A ina kika san Matata da har kika san tana da Kishi?"
Seta harareshi qasa qasa kafin ta danna wayarta ta nemo number Umaimah data kwafa ranar daya nuna musu hotunanta a waya ta juya masa wayar tana cewa
"Ko ba wannan ce Number taba? Na tabbata idan taga hotunan nan seka gwammace kida da karatu dan kaida kwanciyar hankali har abada".
Dariyar da shikansa ya rasa ta mecece yayi kafin cikin tsananin dauriya daga rudun ganin number Umaimah a wayarta yace
"Toh ko zaki gwada aika mata yanzu ko gani? Kinga naga alamar bazamu daidaita ni abinda nake miki magana akai daban ke kuma kina wani shirme daban, kina zaton zakiyi blackmailing dina ne kiringa mun barazana da wata Matata ko wani abu to bari kiji ki koma ki sake shiri dan wannan bazeyi aiki ba, maganar soyayyar ma kuma na fasa tunda naga ba ita bace a gabanki na barki kije kici gaba da shirmen da kike ganin dabara ce a gurinki" ya fada yana miqewa tsaye zuciyarsa na wani tsalle akan fargabar abinda ze biyo bayan hargagin nasa amma ga mamakinsa se yaga itama ta miqe tsaye tana kallonsa tace
"Ta yaya zan yarda gaskiya kake fada mun ba yaudarata kakeyi ba?"
Ajiyar zuciya ya sauke a boye kafin shima ya kalleta yace
"Kibi abinda zuciyarki tafi yarda akai".
Seta koma ta zauna ganin haka shima yaja kujerarsa ya zauna yana Addu'a a zuciyarsa, shiru sukayi na wani lokaci kafin ta bude baki tace
"Ni ba soyayya ko bata lokaci nake so muyi ba Sonka nakeyi da aure dan haka idan ka shirya belin kanka a shirye nake ko a gobe ka tura a nema maka aurena ni kuma nayi maka Alqawarin zan goge duk wani hoto da video na gurina da gurin wadanda na bawa Ajiya"
"Well, ni idan zan aureki zan aureki ne a ra'ayin qashin kaina badan wata barazanarki ba, sannan idan dan wannan nema ai kin rigada kin lalata abin tunda har kin turawa wasu a matsayin Ajiya ko? Ta yaya zan yarda suma basu nunawa wasu ba kinga kenan idan ina gudun fitarsu ne magana ta qare kin rigada kin fitar dasu tunda bake kadai kika mallake su ba" Khalil ya fada yana tsareta da ido, shikansa yayi mamakin yanda ya iya dakewa yake magana ba tareda ta gano shi ba.
Duburburcewa tayi cikin in ina tace
"Toh ai toh nasan wadanda na bawan zasu boye ba zasu nunawa kowa ba, kuma ma ni da kaina na boye su kansu basu san menene a ciki ba"
"Amma dazu fa kikace kin gaya musu zaki hadu dani idan wani abu ya sameki nine kinga kenan sun san abinda yake faruwa ko?" Ya sake jefa mata wata tambayar yana kallonta kamar wani Jami'in tsaro seta hade rai ta miqe tana cewa
"Saboda kaga na tsaya muna magana shine har kake nema ka titsiyeni ka raina mun hankali ko? Toh shikenan kaje zakaga abinda ze biyo baya, zakazo kana dana sani da bashida amfani tunda har ka kasa amfani da damar dana baka. Kuma wallahi kaci sa'a ina sonka ne amma a yanda na quduri daidaita rayuwar Hadiza dan saboda kaine na rangwanta mata abin ya tsaya iya haka amma tunda bakaga abinda nayi maka ba, zaka gwammaci kida da karatu" ta dauki jakarta da wayarta dake ajiye zata juya shima ya miqe yana cewa
"Na gaya miki ni bana tsoron ki yada koma menene amma ki sani kin dabawa kanki wuqa kuma ita ramuwar gayya akace tafi ta gayya zafi. Idan kin sabayiwa mutane haka kina cin banza ki tabbatar wannan karon kin tabo tsuliyar Dodo dan Khausar idan bakiyi wasa ba seba batar dake" yana gama gaya mata haka ya juya ya wuceta fuuu kamar iska ya barta tsaye tana binsa da kallo daidai sannan.
Khausar
Sosai tsoron yanayin da Khalil din yayi magana ya kamata daman kuma ta fuskanci kamar ya gano duk wani shirinta amma yanzu yaya zatayi? Batar da ita fa yace zeyi ta tabbatar da kuma ze iya tunda komai kudi ne yake aiki a yanzu.
Komawa tayi ta zauna ta dauki wayarta dake ajiye ta shiga kiran qawarta Shema wadda da ita suka qulla duk wani shiri ita ce ma ta hada ta da wanda yayi mata hotunan da Video
"Ke kamarfa gayen nan ya gama gane shiri na gaba daya fa ya nuna baya jin tsoron ma na saki hotunan ba kamar jiya da nake gaya miki ba" Khausar ta fada bayan da Shema ta daga wayar, tsaki Sheman tayi tace
"Kefa banzace daman ai dole ze nuna miki be damu ba saboda ki karaya ki fasa abinda zakiyi Allah sa dai bake ce ma kikaje kikayi abinda ya gano ki ba"
"Ko daya wallahi nuna mun yayi shi be damu ba ko jiyan ma saboda Hadiza ne kuma ma ashe basa tare yanzu harfa yana maganar daman yana sona kuma ze aureni to fa daga na tambayeshi ya zaayi na gane ba yaudarata yake so yayi ba shine kuma yayi fushi har yana cewa Ze iya batar dani" Khausar ta sake fada se Shema ta buga tsaki me qarfi tace
"Ai daman ke banza ce wai wa ma yace ki hadu dashi daga fara abu jiya har zaki bari ku hadu yau dole ma ya gane bada gaske kike ba, yanzu ya turo miki da kudin da kika nema jiya ne? Seda nace miki idan be turo ba kaitsaye ki aikawa da Matarsa shine ze tabbatar bada wasa kike na amma jiki na rawa daga yace kizo kuyi magana kinje seki shirya tarar abinda ze biyo baya tunda daman idan baka iya kama barawo ba ai shi se ya kamaka"
"Toh yanzu ya zanyi Shema, ni fa batarwar nan daya ce ta daga mun hankali ke kika bani labarin qawarki da haka ta fau da ita fa" Khausar ta sake fada kamar zatayi kuka daga can bangaren Shema tace
"Minal ba shekara biyu kenan babu labarinta se tashin zancen, iyayenta ma da suka gaji da nema Addu'a kawai aka mata sun saddaqar ta mutu amma ita ai babban mutum tayiwa, daman a lokacin seda muka hanata wata qawarta tace mata babu komai itama ta tabayi ta samu kudi sasai dan daman su badan a aure su bane kawai Kudi suke karba a gurin mutanen, aiko randa ta tura masa da Video washe gari ta fita aka dauketa a hanya shikenan qila se a lahira".
Cikin Khausar ne ya bada qarara quuu jin wai a hanya aka dauketa tace
"Karfa nima yanzu kiji babu ni ko kuma yasa a tareni a kwace mun waya kin san komai yana ciki kawai bari in jira kizo mu tafi tare ne kinji dan Allah"
"Ai seda nace ki tura a wayata saboda tsaro ke ga me wayo kika ce Aa, Ai se ki zauna barazana yayi miki kuma kin rufta Allah yasa ma ba labewa yayi yaga yanda zakiyi ba kinga kuwa idan haka ne kina ruwa wallahi ya gano lagonki, ina yaga kudinda ze biya a batar dake banda ma ke sauna ce da har zaki wani tashi hankalinki? Dallah ki kamo hanya ki taho musan yanda zamu gyara shirmen da kikayi" tana gama fada ta kashe wayar.