Sashe 223
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru Maman tayi kamar ba zata ce mata komai ba se kuma ta numfasa tace
"Idan ruwan ya tafasa kizo ki gaya ki debi kwai ki dafa a saka a cikin Alalan" daga haka taci gaba da jan carbinta Umaimah ta ja qafafunta ta wuce Kitchen din. Waken ta fara dubawa ta sauke ajiyar zuciya ganin gyararrene har ya juqu ma dan haka ta wanke shi ta dubo Attaruhu da Albasa ta zuba cikin takatsan tsan, sedata hada markadan tsaf kafin ta wuce qofar dakin Anty ta kwankwasa dan babu wanda ya fito a yaran Lahadi ce kuma an musu hutun Tahfiz ga garin yanayin sanyi ya fara shigowa tasan suna nade a bargo se ita da uwarta bata sonta ce take gararanba a tsakar gida da farar safiya. Tafi Minti biyar tana bugu kafin Antyn ta bude fuska babu yabo babu fallasa tana kallonta, kamar karta gaisheta saboda qin roqar mata da Abba da batayi ba jiya amma ta dake tace mata ina kwana.
"Mama ce tace Yasir yazo ya kai markaden Alala" ta fada a cukule itama Antyn murya babu walwala tace
"Yasir ya tashi da Zazzabi sedai ko Sharifa dan Firdausi ma tabi Fatima jiya". Jin cewar se Sharifa yasa ta juya ba tareda ta cewa Antyn komai ba dan indai yar iskar yarinyar nan ce qarshe seta jawo mata wani laifin ace bata gama da wuri ba sawunta a likafa ta wuce ta kunna wuta danma itacen busashshene tana yi tana hawaye wai ita Umaimah ce ta sake dawowa girkin itace? Seda ta hada wutar ta dora ruwan kunu kafin ta leqa waje ta samo Almajiri ya kai mata markaden a ranta tana Mamakin duk Almajiran da suke musu hidima a gidan suna ina tunda satin ya kama ta dena ganinsu ko saboda an shirya maida ita boyi boyi yasa aka sallamesu.
Ta kalli tsakar gidan ta tabbatar kuma ita din ce dai me sharewa duk dan saboda a jance zancen cin shinkafa ta tattara kwanukan da aka fito dasu na wanke wanke a gefe ta hau shara, kafin ta gama bayanta ya riqe dakyar ta iya miqewa saboda Azabar ciwon daya dauka ta wuce dakin Mama tana kuka kamar yarinya dan ruwan ya tafasa Mama ta kalleta kawai bata ce komai ba, ganin Almajirin ya kawo markaden ta kama hada Alalan tana yi tana diga musu Hawayen daya kasa tsayar mata a ciki Mama dai ta dama kununta tafi ki mutu bata ce mata ba se sanann Anty ta fito suka gaisa ta kawo Flask din da ake saka musu Kunun Maman ta zubawa kowa nasa ta koma dakinta. Umaimah na zaune tana jiran Alalal ta dafu tana aikin kuka kamar matar Mamaci har yayi ta kwashe ta hada kwanukan ta hau wanke wanke. Tana kallo kowa ya debi abin karinsa yaci kamar kwayar idonta zata fita saboda kuka yanzu duk ta gama wahalar nan ba zataci ba kenan ake nufi haka ta wuce daki ta kwanta dakyar saboda ciwon jiki tana kuka data ci shinkafar nan ta gwammace yunwa ta kasheta kawai kowa ma ya huta tunda an tsaneta. Sha biyun rana Mama ta kwala mata kira, ta yunqura dakyar ta fita jikinta kamar wadda ta fado daga kan bishiya saboda ciwo ta tsaya tana kallon Zogalen dake jibge a qasa ba'a tsinke shi ba ta kalli Mama dake cewa
"Gashi nan Dambu zakiyi tsakin kwano biyu zaki auna dan za'a kai nan baya gidan Malam Bala anyi Rasuwa dazu ga Madambaci nan nasa a aro na gidan su Harira shi babbane sosai in kika hada da wannan zaki fi sauri".
"Dambu" ta maimaita tamkar bata san kalmar ba, ta waiwaya jin Yaro yayi sallama da wani uban rafkeken madambaci ya ajiye take ta tuno da zuwansu gidan Qawarta Abu Maman Nihal a irinsa suka tarar da ita tana dambu shikenan ta shiga ukun ta ta lalace. Cikin kuka tace
"Wlh yunwa nakeji Mama bazan iya aikin dambu yanzu ba"
"Ga shinkafarki can ai ki diba ki dumama kici kuma ki hanzarta ki dora da wuri dan Abbanku yana gida kin san kuma Azahar nayi ze nemi Abinci" Maman ta bata amsa cikin ko in kula kafin ta zura Hijabin dake hannunta tana cewa
"Idan kin gama bamu dawowa ba ga Kwano nan(ta nuna mata wata fanteka) indai kinyi awon daidai ragowar ze cika wannan bayan ki debar mana na gida se bawa Ko Salman ne ya miqa gidan rasuwar se Mundawo" tana gama fada tayi gaba sega Anty ta fito da fitsararriyar yarta inji Umaimah a bayanta da alama tare zasu tafi suka rankaya suka barta a tsaye ta rasa abinyi se hawaye takeyi.*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 77
UMAIMAH
Daren Ranar bata iya bacci ba seda Anty ta kira wani me Chemist ya dubata yayi mata allurar rage zugi tasha magani sannan, washe gari da safe ta tashi da wani sabon tashin hankalin. Qarfe goma gaba daya yan gidan manya da yara suka hallara bisa umarnin kiran da Abban yayi musu tun daren jiya. Bata san kiran me ya musu ba tadai ga sun shige can bangarensa kuma sun dade suna magana dan har se gurin sha biyu sannan Salman yazo yayi kiranta.
Dakyar take tafiya saboda yanda jikinta yayi tsami, badan kar ta sake yin wani laifin ba daman da bazataje kiran ba. Irin yanda gaba daya suka dauke kai tamkar babu wanda yasan da tsiron halittarta a gurin ya mata ciwo daman tunda ta dawo gidan in ka cire Anty babu me shiga sabgarta Mama kuwa in zasu hadu sau dubu ta gaidata bazata amsa ba daman tun randa tadawo tayi mata iyaka da shiga dakinta tace bata buqatar ganinta a ciki. Tana zama kamar wata Mujiya a cikinsu suka fara darewa daya da daya duk suka fice daga dakin kowanne yazo giftata seya bugamata tsaki sannan su harareta, seda suka fice gaba daya kafin Mama ta kalleta rai babu dadi tace
"Matso ciki".
Gaba kadan ta muskuta amma bata yarda tayi kusa dasu da yawa ba cikin rawar Murya ta shiga gaishe su ta kalli Abba dake Kishingide da gani bashida lafiya, babu wanda ya amsa gaisuwar Tata har Antyn yau tana daga gefe idonta yayi jajir alamar Kuka tayi se Umaimah ta sunkuyar da kanta qasa, muryar Abban taji cikin dakiya yana cewa
"Ina so ku zama shaida tsakanina da Umaimah zan kafa mata sharudda da har idan tana neman zaman lafiya a cikin gidan nan dole ta bisu. Ban yarda Umaimah ta taka ko nan da qofar gida ba tareda izinina ba haka zalika banyarda wani yazo gidannan gurinta ba, sannan zata bani wayarta" Abban ya fada yana kallon Umaimah data sunkuyar da kanta qasa tana hawaye, takaicin yanda gaba daya kowa ya tsaneta ya kamata, babu wanda ya dubi halin da ta tsinci kanta a ciki ita ta rasa Khalil a maimakon su tausaya mata suyi qoqarin kwato mata haqqinta se suka bige da tsanarta kamar ta aikata musu wani mugun laifi.
Tana jin Abban ya gama maganarsa, zancen ba zata fita ba ko ba za'a zo gunta ba be dameta ba kamar na karbe mata waya. Idan ya rabata da wayarta ta ina zata samu damar magana da Khalil harsu daidaita ta koma dakinta? Tsawar da Mama ta daka mata ceta sakata miqewa da sauri dan dakko wayar, tana hawaye kamar yarinya ta bashi wayar tata ya karba a gabanta ya zare layin ya ballashi biyu kafin ya sake kallonta yace
"Abu na gaba
daga yau duk wani aiki na cikin gidan nan ya dawo hannunki, ina nufin daga kan shara girki wanke wanke da duk wasu sauran ayyukan tsakar gida ke zaki cigaba da yinsu har wankin kayanku idan kuna da buqata ku bata tayi muku dan ba zan ringa ciyar da ke a banza ba tunda kinqi zaman aure kiyi na Farilla ki samu lada zakiyi Mustahabi anan. Idan har na kamaki da laifin saba daya daga cikin sharuddan nan ina me tabbatar miki da cewar sekin gane kuskurenki tabbas".
Da sauri ta daga kai ta kalli Abban bakinta na rawa alamar son yin magana amma mugun kallon da Mama ta aika mata dashi yasa ta kasa cewa komai ta maida kanta qasa hawaye suka sake balle mata kamar famfo.
"Rayuwar da kika zabarwa kanki kenan zaman gida ba gaki ga gidannan se kici uwar da kika ajiye a ciki. Kinsan dai ba zamu zauna muna goga kafada dake a cikin gidan nan ba mu dafa mu baki kici ki ajiye kwano mu share guri ki zauna na iya lokacin da aka miki ma Allah ya bamu lada dan haka dolenki kiyi aiki in har kina son zaman lafiya damu koda yake ma bata bakina nakeyi saboda na manta da kin rigada kin zama yar kanki kiyi duk yanda yayi miki Umaimah babu wanda zesake tilasta ki akan kiyi daidai amma kin sani matuqar kika qi ji ba zaki qi gani ba kuma kinji abinda Mahaifinki duk ya fada se ki zaba zama lafiya kibi abinda yace ko ki fara neman wani gidan uban da zakije kici gaba da yanda kika ga dama" Mama ta fada cikin fushi ita dai Umaimah kanta na qasa in banda hawaye babu abinda takeyi.
"Idan ruwan ya tafasa kizo ki gaya ki debi kwai ki dafa a saka a cikin Alalan" daga haka taci gaba da jan carbinta Umaimah ta ja qafafunta ta wuce Kitchen din. Waken ta fara dubawa ta sauke ajiyar zuciya ganin gyararrene har ya juqu ma dan haka ta wanke shi ta dubo Attaruhu da Albasa ta zuba cikin takatsan tsan, sedata hada markadan tsaf kafin ta wuce qofar dakin Anty ta kwankwasa dan babu wanda ya fito a yaran Lahadi ce kuma an musu hutun Tahfiz ga garin yanayin sanyi ya fara shigowa tasan suna nade a bargo se ita da uwarta bata sonta ce take gararanba a tsakar gida da farar safiya. Tafi Minti biyar tana bugu kafin Antyn ta bude fuska babu yabo babu fallasa tana kallonta, kamar karta gaisheta saboda qin roqar mata da Abba da batayi ba jiya amma ta dake tace mata ina kwana.
"Mama ce tace Yasir yazo ya kai markaden Alala" ta fada a cukule itama Antyn murya babu walwala tace
"Yasir ya tashi da Zazzabi sedai ko Sharifa dan Firdausi ma tabi Fatima jiya". Jin cewar se Sharifa yasa ta juya ba tareda ta cewa Antyn komai ba dan indai yar iskar yarinyar nan ce qarshe seta jawo mata wani laifin ace bata gama da wuri ba sawunta a likafa ta wuce ta kunna wuta danma itacen busashshene tana yi tana hawaye wai ita Umaimah ce ta sake dawowa girkin itace? Seda ta hada wutar ta dora ruwan kunu kafin ta leqa waje ta samo Almajiri ya kai mata markaden a ranta tana Mamakin duk Almajiran da suke musu hidima a gidan suna ina tunda satin ya kama ta dena ganinsu ko saboda an shirya maida ita boyi boyi yasa aka sallamesu.
Ta kalli tsakar gidan ta tabbatar kuma ita din ce dai me sharewa duk dan saboda a jance zancen cin shinkafa ta tattara kwanukan da aka fito dasu na wanke wanke a gefe ta hau shara, kafin ta gama bayanta ya riqe dakyar ta iya miqewa saboda Azabar ciwon daya dauka ta wuce dakin Mama tana kuka kamar yarinya dan ruwan ya tafasa Mama ta kalleta kawai bata ce komai ba, ganin Almajirin ya kawo markaden ta kama hada Alalan tana yi tana diga musu Hawayen daya kasa tsayar mata a ciki Mama dai ta dama kununta tafi ki mutu bata ce mata ba se sanann Anty ta fito suka gaisa ta kawo Flask din da ake saka musu Kunun Maman ta zubawa kowa nasa ta koma dakinta. Umaimah na zaune tana jiran Alalal ta dafu tana aikin kuka kamar matar Mamaci har yayi ta kwashe ta hada kwanukan ta hau wanke wanke. Tana kallo kowa ya debi abin karinsa yaci kamar kwayar idonta zata fita saboda kuka yanzu duk ta gama wahalar nan ba zataci ba kenan ake nufi haka ta wuce daki ta kwanta dakyar saboda ciwon jiki tana kuka data ci shinkafar nan ta gwammace yunwa ta kasheta kawai kowa ma ya huta tunda an tsaneta. Sha biyun rana Mama ta kwala mata kira, ta yunqura dakyar ta fita jikinta kamar wadda ta fado daga kan bishiya saboda ciwo ta tsaya tana kallon Zogalen dake jibge a qasa ba'a tsinke shi ba ta kalli Mama dake cewa
"Gashi nan Dambu zakiyi tsakin kwano biyu zaki auna dan za'a kai nan baya gidan Malam Bala anyi Rasuwa dazu ga Madambaci nan nasa a aro na gidan su Harira shi babbane sosai in kika hada da wannan zaki fi sauri".
"Dambu" ta maimaita tamkar bata san kalmar ba, ta waiwaya jin Yaro yayi sallama da wani uban rafkeken madambaci ya ajiye take ta tuno da zuwansu gidan Qawarta Abu Maman Nihal a irinsa suka tarar da ita tana dambu shikenan ta shiga ukun ta ta lalace. Cikin kuka tace
"Wlh yunwa nakeji Mama bazan iya aikin dambu yanzu ba"
"Ga shinkafarki can ai ki diba ki dumama kici kuma ki hanzarta ki dora da wuri dan Abbanku yana gida kin san kuma Azahar nayi ze nemi Abinci" Maman ta bata amsa cikin ko in kula kafin ta zura Hijabin dake hannunta tana cewa
"Idan kin gama bamu dawowa ba ga Kwano nan(ta nuna mata wata fanteka) indai kinyi awon daidai ragowar ze cika wannan bayan ki debar mana na gida se bawa Ko Salman ne ya miqa gidan rasuwar se Mundawo" tana gama fada tayi gaba sega Anty ta fito da fitsararriyar yarta inji Umaimah a bayanta da alama tare zasu tafi suka rankaya suka barta a tsaye ta rasa abinyi se hawaye takeyi.*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 77
UMAIMAH
Daren Ranar bata iya bacci ba seda Anty ta kira wani me Chemist ya dubata yayi mata allurar rage zugi tasha magani sannan, washe gari da safe ta tashi da wani sabon tashin hankalin. Qarfe goma gaba daya yan gidan manya da yara suka hallara bisa umarnin kiran da Abban yayi musu tun daren jiya. Bata san kiran me ya musu ba tadai ga sun shige can bangarensa kuma sun dade suna magana dan har se gurin sha biyu sannan Salman yazo yayi kiranta.
Dakyar take tafiya saboda yanda jikinta yayi tsami, badan kar ta sake yin wani laifin ba daman da bazataje kiran ba. Irin yanda gaba daya suka dauke kai tamkar babu wanda yasan da tsiron halittarta a gurin ya mata ciwo daman tunda ta dawo gidan in ka cire Anty babu me shiga sabgarta Mama kuwa in zasu hadu sau dubu ta gaidata bazata amsa ba daman tun randa tadawo tayi mata iyaka da shiga dakinta tace bata buqatar ganinta a ciki. Tana zama kamar wata Mujiya a cikinsu suka fara darewa daya da daya duk suka fice daga dakin kowanne yazo giftata seya bugamata tsaki sannan su harareta, seda suka fice gaba daya kafin Mama ta kalleta rai babu dadi tace
"Matso ciki".
Gaba kadan ta muskuta amma bata yarda tayi kusa dasu da yawa ba cikin rawar Murya ta shiga gaishe su ta kalli Abba dake Kishingide da gani bashida lafiya, babu wanda ya amsa gaisuwar Tata har Antyn yau tana daga gefe idonta yayi jajir alamar Kuka tayi se Umaimah ta sunkuyar da kanta qasa, muryar Abban taji cikin dakiya yana cewa
"Ina so ku zama shaida tsakanina da Umaimah zan kafa mata sharudda da har idan tana neman zaman lafiya a cikin gidan nan dole ta bisu. Ban yarda Umaimah ta taka ko nan da qofar gida ba tareda izinina ba haka zalika banyarda wani yazo gidannan gurinta ba, sannan zata bani wayarta" Abban ya fada yana kallon Umaimah data sunkuyar da kanta qasa tana hawaye, takaicin yanda gaba daya kowa ya tsaneta ya kamata, babu wanda ya dubi halin da ta tsinci kanta a ciki ita ta rasa Khalil a maimakon su tausaya mata suyi qoqarin kwato mata haqqinta se suka bige da tsanarta kamar ta aikata musu wani mugun laifi.
Tana jin Abban ya gama maganarsa, zancen ba zata fita ba ko ba za'a zo gunta ba be dameta ba kamar na karbe mata waya. Idan ya rabata da wayarta ta ina zata samu damar magana da Khalil harsu daidaita ta koma dakinta? Tsawar da Mama ta daka mata ceta sakata miqewa da sauri dan dakko wayar, tana hawaye kamar yarinya ta bashi wayar tata ya karba a gabanta ya zare layin ya ballashi biyu kafin ya sake kallonta yace
"Abu na gaba
daga yau duk wani aiki na cikin gidan nan ya dawo hannunki, ina nufin daga kan shara girki wanke wanke da duk wasu sauran ayyukan tsakar gida ke zaki cigaba da yinsu har wankin kayanku idan kuna da buqata ku bata tayi muku dan ba zan ringa ciyar da ke a banza ba tunda kinqi zaman aure kiyi na Farilla ki samu lada zakiyi Mustahabi anan. Idan har na kamaki da laifin saba daya daga cikin sharuddan nan ina me tabbatar miki da cewar sekin gane kuskurenki tabbas".
Da sauri ta daga kai ta kalli Abban bakinta na rawa alamar son yin magana amma mugun kallon da Mama ta aika mata dashi yasa ta kasa cewa komai ta maida kanta qasa hawaye suka sake balle mata kamar famfo.
"Rayuwar da kika zabarwa kanki kenan zaman gida ba gaki ga gidannan se kici uwar da kika ajiye a ciki. Kinsan dai ba zamu zauna muna goga kafada dake a cikin gidan nan ba mu dafa mu baki kici ki ajiye kwano mu share guri ki zauna na iya lokacin da aka miki ma Allah ya bamu lada dan haka dolenki kiyi aiki in har kina son zaman lafiya damu koda yake ma bata bakina nakeyi saboda na manta da kin rigada kin zama yar kanki kiyi duk yanda yayi miki Umaimah babu wanda zesake tilasta ki akan kiyi daidai amma kin sani matuqar kika qi ji ba zaki qi gani ba kuma kinji abinda Mahaifinki duk ya fada se ki zaba zama lafiya kibi abinda yace ko ki fara neman wani gidan uban da zakije kici gaba da yanda kika ga dama" Mama ta fada cikin fushi ita dai Umaimah kanta na qasa in banda hawaye babu abinda takeyi.