Sashe 202
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Na gaya maka duk ranar daka kuskura ka hada soyayyata data wata sena kashe ka na kasheta sannan na kashe kaina baka ji ba yau zan nuna maka da gaske nakeyi wallahi Khalil sena kashe ka da dai ka hadani da wata mace gara na rasaka har abada" ta fada tana binsa da wuqa tsirara hankalin su Hajiya ya qara tashi gaba daya suka rude suna kiran sunanta amma ina bata ji se bin Khalil take tana kuka shi kuma yana gudu hankali tashe dan babu yanda za'ayi ya tsaya be san me zata aikata masa ba.
Get ya nufa da gudu ta bishi, yana qoqarin bude qofar aka turo ya saki ajiyar zuciya ganin Mama cikin tashin hankali Salman na bayanta da AbdulBasit dan Yayanta jikinsa sanye da Uniform dinsa na police da alama daga gurin aiki yake, ko a jikin Umaimah babu abinda ta fasa saboda ganinsu kai tsaye ta sake durfafar Khalil daya maqale jikin Get yana raba ido dake da qeya, Qafa AbdulBasit din ya saka mata ta tafi kamar zata fadi kafinta kai qasa ta tareta wuqar hannunta ta fadi Salman ya dauki yayi waje da sauri.
"Ka sakeni, ku bani wuqata in kashe shi wlh sena kashe shi ai na gaya masa amma beji ba ku rabu dani" Umaimah ta fada tamkar me maye lokaci daya numfashinta yana sarqewa idanunta suka qaqqafe kafin suyi wani yunquri jikinta ya saki gaba daya Abdilbasit ya gyara ruqon da yayi mata yana cewa Khalil
"Kama munita mu sakata a mota akaita Asibiti ta suma" se Khalil din yayi gaba ya dawo baya saboda yanda gaba daya tunaninsa ya rimice ga wani mugun ciwo da kansa yake masa sakamon dukan datayiwa qeyarsa. Su Hajiya suka qarasa bakin Get din Jamila ce tayi qarfin Halin matsawa ta kama masa Umaiman tana cewa
"Baze iya ba, shima ba a hayyacinsa yake ba abu ta buga masa akai"
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allahumma ajirni fi musibati wa'aklifni khairan minha" Mama ta fada gaba daya ta rikice ta rasa abinyi, haka suka taru suka ciccibata aka sakata a motar dasu Maman suka zo su kuma suka shiga motar Khalil banda Jalila da tace babu inda zataje, Asibiti suka nufa.
Emergency aka karbi Umaiman, suna dorata akan Gado ta farka da wani mugun qarfi ta zabura zata sauka Nurses uku suka hadu suka danneta, tana bige bige tana zaginsu maganganu takeyi marasa kan gado da su basu fahimci abinda take magana akai ba abu daya suke iya fahimta kalmar seta kashe da take ta nanawata a haka Likitan yayi mata allurar bacci wadda seda akayi da gaske kafin ta dauketa.
A can reception kuwa gaba daya sukayi cirko cirko banda Khalil daya zauna a qasa ya dafe kansa da yake ji kamar ana girki a ciki tsabar zafin da yayi masa, Abba da Mama ta kira tun suna hanya ya qaraso Asibitin tareda Anty hankalinsu a mutuqar tashe, a taqaice suka gaya masa abinda ya faru suna nan tsaye suna jajantawa Wata Nurse ta fito da gudu daga ward din da aka kwantar da Umaimah tana kiran Dr,
"Wannan patient din da aka kawo Dr inaga tana da tabin hankali gata can ko 29 mins ba'ayi dayi mata allura ba ta farka tana ta buga kanta a bango tana kuka mun rasa ya zamuyi da ita" Nurse ta fada jikinta na rawa dan tunda take a Asibiti bata taba cin karo da psychiatric patient ba se yau kuma shahararre da haukansa yayi nisa irin na Umaimah.
A fusace Abba yabi bayan Dr zuwa dakin, Umaimah na tsaye tana zugawa Nurses din zagi na tsamar nama akan su bude mata qofa ta fita sunqi Dr ya bude ta waje suka shiga tana ganinsa ta yunqura da niyyar fita Abba dake bayanaa ya zabga mata marin daya sa tayi gefe ta tsaya babu shiri
"Ki nutsu ki shiga hankalinki wlh tun kafin kija nayi miki abinda zanzo ina nadama daga baya. Ke wace irin kafaffiyar yarinya ce da baki san Annabi ya faku ba? A rayuwarki baki san komai se tashin hankali da bala'i ke baki zauna lafiya ba mu baki barmu munsamu nutsuwa ba kashe mu kike so kiyi kome Umaimah?"
"Ni babu ruwanku dani Abba babu wanda nace ya shiga sabgata baku ga abinda akayi mun ba Aure fa Khalil yayi Abba ya munafunceni ban sani ba se yau sannan kuma ku hanani hukuntashi wannan ai ba adalci bane nidai tunda babu me qaunata duk ba zaku iya kwatarmun haqqina ba se ku barni daman nasan ba sona kuke yi ba na sani ma da hadin bakinku yayi shi yasa Mma dasu Anty Hafsa suka ringa zuwa suna fadamun maganganu ashe kunsan abinda kuka shirya nidai Allah ya isa kuma an cuceni Allah yana kallo bazan yafe ba duk wanda yake sa hadin baki a maganar nan Allah ya bi mun haqqina" Umaiman ta fada cikin matsanancin kuka Abba da baqin ciki ya qumeshi ya sake niyyar kai mata Mari ta goce yayi taga taga ze fadi saboda jirin daya taho masa Likita ya riqeshi yana cewa
"Yi a hankali Alhaji karka fadi kayi haquri ka kwantar da hankalinka".
Cikin bacin rai ya kalli Umaimah da har sannan take kuka yace
"Kaiconki Umaimah kaicon zuciya irin taki, ashe ke ba zaki taba yarda da cewar duk abinda ya samu bawa daga Allah bane? Ba zaki iya haquri da duk jarabawar data sameki a rayuwa ba?
Iya wannan auran idan kinada hankali ya isheki ishara amma a maimakon ki dauki darashi ki nutsu sema sake bude babin hauka kikayi ko to kiji da kunnenki karki fasa duk abinda kika yi niyya zan kuma sake jaddada miki Khalil yayi aure babu kuma abinda ya isa ya tada wannan aure se ikon Allah kuma ko kinso ko baki so ba a yau ba se gobe ba ze tare da Matarsa a cikin gidanki a dakinki tunda kin Lalata abinda iyayenta suka saka mata idan yaso baqin ciki yasa ko hadiyi zuciya ki mutu kowa ya huta yar banza me zuciya irinta kafiranfarko" yana gama fadar haka ya sa kai ya fice daga dakin zuciyarsa na wani irin tuquqi, badan karya butulcewa Allah ba daya yi nadamar kasancewar Umaimah jininsa.
Cak ta tsaya da kukan kalamansa sukayi mata dirar Mikiya wai Abba ne yake gaya mata Khalil ze tare da wata mace yau a dakinta akan Gadonta? Seta miqe da wani irin sauri a take kuma kamar wadda aka mayar ta fadi yaraf a gurin kamar me farfadiya tana jijjiga Likitan yayi kanta da sauri Nurses suka rufa masa baya, seda suka mayar da ita kan gadon kafin suka shiga bata taimakon gaggawa sun kwashe sama da minti talatin akanta kafin jijjigar ta tsaya jikinta ya saki gaba daya numfashinta kansa se a hankali dole suka saka mata oxygen bayan Likitan ya mata duk abinda ya kamata yayi suka fita daga dakin aka barta da Nurse guda daya.
Reception din ya koma yana dafe kansa da jarabar Umaimah tasa ya fara maaa ciwo, suna zaune kamar ana zaman makoki sabanin da yanzu su Nuratu sun qaru da wasu daga bangaren Hajiyar dan tuni Lubna ta dake maqale a daki tunda tasha matsa ta kai labari Family group dinsu. Suna ganin Likitan Hajiya da Anty sukamiqe da sauri suna tambayarsa jikinta cikeda qosawa yace musu
"Da sauqi amma kuyi haquri yanzu ku barta kar wanda ya shiga inda take saboda tana da buqatar hutu sosai"
"Toh likita cikin jikinta fa, daman ba kunce gobe zaku mata aiki ba meze hana ayi yanzu saboda gudun kar wani abu ya same shi" Hajiya ta fada se likitan ya girgiza kai yace
"Baze yuwu ba Hajiya, maganar gaskiya a yanzu haka ta sake Suma sannan jininta ya hau har ya wuce qa'ida baze yuwu muyi mata Allurar Anesthesia ba saboda idan abun yazo da tsautsayi zata iya zarcewa dole se mun jira ta farka sannan jininta ya daidaita kafin koma menene ya biyo baya, nidai roqon da zanyi muku ku barta ta huta dan Allah zuciyarta da kwakwalwarta su samu hutu sosai, Ina Mijinta ya biyo ni ina son magana dashi" daga haka ya wuce office ya barsu nan a tsaye.
Khalil ya fito daga wani office dayaga likita shima ya auna BP sa ya rubuta masa magani yace yasha ya samu yayi bacci ciwon kan nasa ze sauka, seda yaje gurin likitan daya duba Umaimah ya sake masa bayanin daya musu kafin ya fito yaje pharmacy ya siyi maganin da aka rubuta masa a gurin ya sha ya sake dawowa reception din ya tarar dasu, Abbane ya kirashi suka fita tare. Duk su biyun idan ka kallesu kasan babu me nutsuwa a cikinsu, can gurin wata bishiya suka tsaya Abban ya kalli Khalil da shi kuma yake kallon qasa yace
"Ibrahim kayi haquri ka qara akan wanda kakeyi dukda dai Allah ya sani ban rufeka ba tun kafin na baka auran Umaimah seda na zaunar dakai na gaya maka wacece ita kuma a hakan kace kaji ka gani kana sonta na tabbata a sannan baka san cewar Jidalinta ya kai har haka ba, bamu tara sani da ikon Allah kuma ita qaddarar mutum baya kauce mata badan da qila yanzu kana gudanar da rayuwarka cikin kwanciyar hankali da nutsuwa. A taqaice abinda nake so na gaya maka shine karka dauki wannan abun da tayi a matsayin wani abu da ze tsorata ka kota dakatar dakai daga yin duk abinda kayi niyya. Naji ance ta lalatawa Amarya dakinta kuma gobe ya kamata ta tare ko?"
Khalil ya gyada kai kawai se Abban yaci gaba da cewa
"Shikenan amma hakan baze canza komai ba, ka dauki dakinta da take ciki da komai ka bawa Amaryar ita kuma idan ta warke ta shere inda ta lalata ta koma ciki ban kuma yarda naji ka ce ba haka na Umarni na baka idan har ka daukeni a matsayin Uba sannan kamar yanda aka tsara tarewar Amarya a gobe idan Allah ya kaimu zan kira Kawunka nida shi zamu dakko Maka Amaryarka mu kawo maka ita idan Allah ya yarda".
Get ya nufa da gudu ta bishi, yana qoqarin bude qofar aka turo ya saki ajiyar zuciya ganin Mama cikin tashin hankali Salman na bayanta da AbdulBasit dan Yayanta jikinsa sanye da Uniform dinsa na police da alama daga gurin aiki yake, ko a jikin Umaimah babu abinda ta fasa saboda ganinsu kai tsaye ta sake durfafar Khalil daya maqale jikin Get yana raba ido dake da qeya, Qafa AbdulBasit din ya saka mata ta tafi kamar zata fadi kafinta kai qasa ta tareta wuqar hannunta ta fadi Salman ya dauki yayi waje da sauri.
"Ka sakeni, ku bani wuqata in kashe shi wlh sena kashe shi ai na gaya masa amma beji ba ku rabu dani" Umaimah ta fada tamkar me maye lokaci daya numfashinta yana sarqewa idanunta suka qaqqafe kafin suyi wani yunquri jikinta ya saki gaba daya Abdilbasit ya gyara ruqon da yayi mata yana cewa Khalil
"Kama munita mu sakata a mota akaita Asibiti ta suma" se Khalil din yayi gaba ya dawo baya saboda yanda gaba daya tunaninsa ya rimice ga wani mugun ciwo da kansa yake masa sakamon dukan datayiwa qeyarsa. Su Hajiya suka qarasa bakin Get din Jamila ce tayi qarfin Halin matsawa ta kama masa Umaiman tana cewa
"Baze iya ba, shima ba a hayyacinsa yake ba abu ta buga masa akai"
"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Allahumma ajirni fi musibati wa'aklifni khairan minha" Mama ta fada gaba daya ta rikice ta rasa abinyi, haka suka taru suka ciccibata aka sakata a motar dasu Maman suka zo su kuma suka shiga motar Khalil banda Jalila da tace babu inda zataje, Asibiti suka nufa.
Emergency aka karbi Umaiman, suna dorata akan Gado ta farka da wani mugun qarfi ta zabura zata sauka Nurses uku suka hadu suka danneta, tana bige bige tana zaginsu maganganu takeyi marasa kan gado da su basu fahimci abinda take magana akai ba abu daya suke iya fahimta kalmar seta kashe da take ta nanawata a haka Likitan yayi mata allurar bacci wadda seda akayi da gaske kafin ta dauketa.
A can reception kuwa gaba daya sukayi cirko cirko banda Khalil daya zauna a qasa ya dafe kansa da yake ji kamar ana girki a ciki tsabar zafin da yayi masa, Abba da Mama ta kira tun suna hanya ya qaraso Asibitin tareda Anty hankalinsu a mutuqar tashe, a taqaice suka gaya masa abinda ya faru suna nan tsaye suna jajantawa Wata Nurse ta fito da gudu daga ward din da aka kwantar da Umaimah tana kiran Dr,
"Wannan patient din da aka kawo Dr inaga tana da tabin hankali gata can ko 29 mins ba'ayi dayi mata allura ba ta farka tana ta buga kanta a bango tana kuka mun rasa ya zamuyi da ita" Nurse ta fada jikinta na rawa dan tunda take a Asibiti bata taba cin karo da psychiatric patient ba se yau kuma shahararre da haukansa yayi nisa irin na Umaimah.
A fusace Abba yabi bayan Dr zuwa dakin, Umaimah na tsaye tana zugawa Nurses din zagi na tsamar nama akan su bude mata qofa ta fita sunqi Dr ya bude ta waje suka shiga tana ganinsa ta yunqura da niyyar fita Abba dake bayanaa ya zabga mata marin daya sa tayi gefe ta tsaya babu shiri
"Ki nutsu ki shiga hankalinki wlh tun kafin kija nayi miki abinda zanzo ina nadama daga baya. Ke wace irin kafaffiyar yarinya ce da baki san Annabi ya faku ba? A rayuwarki baki san komai se tashin hankali da bala'i ke baki zauna lafiya ba mu baki barmu munsamu nutsuwa ba kashe mu kike so kiyi kome Umaimah?"
"Ni babu ruwanku dani Abba babu wanda nace ya shiga sabgata baku ga abinda akayi mun ba Aure fa Khalil yayi Abba ya munafunceni ban sani ba se yau sannan kuma ku hanani hukuntashi wannan ai ba adalci bane nidai tunda babu me qaunata duk ba zaku iya kwatarmun haqqina ba se ku barni daman nasan ba sona kuke yi ba na sani ma da hadin bakinku yayi shi yasa Mma dasu Anty Hafsa suka ringa zuwa suna fadamun maganganu ashe kunsan abinda kuka shirya nidai Allah ya isa kuma an cuceni Allah yana kallo bazan yafe ba duk wanda yake sa hadin baki a maganar nan Allah ya bi mun haqqina" Umaiman ta fada cikin matsanancin kuka Abba da baqin ciki ya qumeshi ya sake niyyar kai mata Mari ta goce yayi taga taga ze fadi saboda jirin daya taho masa Likita ya riqeshi yana cewa
"Yi a hankali Alhaji karka fadi kayi haquri ka kwantar da hankalinka".
Cikin bacin rai ya kalli Umaimah da har sannan take kuka yace
"Kaiconki Umaimah kaicon zuciya irin taki, ashe ke ba zaki taba yarda da cewar duk abinda ya samu bawa daga Allah bane? Ba zaki iya haquri da duk jarabawar data sameki a rayuwa ba?
Iya wannan auran idan kinada hankali ya isheki ishara amma a maimakon ki dauki darashi ki nutsu sema sake bude babin hauka kikayi ko to kiji da kunnenki karki fasa duk abinda kika yi niyya zan kuma sake jaddada miki Khalil yayi aure babu kuma abinda ya isa ya tada wannan aure se ikon Allah kuma ko kinso ko baki so ba a yau ba se gobe ba ze tare da Matarsa a cikin gidanki a dakinki tunda kin Lalata abinda iyayenta suka saka mata idan yaso baqin ciki yasa ko hadiyi zuciya ki mutu kowa ya huta yar banza me zuciya irinta kafiranfarko" yana gama fadar haka ya sa kai ya fice daga dakin zuciyarsa na wani irin tuquqi, badan karya butulcewa Allah ba daya yi nadamar kasancewar Umaimah jininsa.
Cak ta tsaya da kukan kalamansa sukayi mata dirar Mikiya wai Abba ne yake gaya mata Khalil ze tare da wata mace yau a dakinta akan Gadonta? Seta miqe da wani irin sauri a take kuma kamar wadda aka mayar ta fadi yaraf a gurin kamar me farfadiya tana jijjiga Likitan yayi kanta da sauri Nurses suka rufa masa baya, seda suka mayar da ita kan gadon kafin suka shiga bata taimakon gaggawa sun kwashe sama da minti talatin akanta kafin jijjigar ta tsaya jikinta ya saki gaba daya numfashinta kansa se a hankali dole suka saka mata oxygen bayan Likitan ya mata duk abinda ya kamata yayi suka fita daga dakin aka barta da Nurse guda daya.
Reception din ya koma yana dafe kansa da jarabar Umaimah tasa ya fara maaa ciwo, suna zaune kamar ana zaman makoki sabanin da yanzu su Nuratu sun qaru da wasu daga bangaren Hajiyar dan tuni Lubna ta dake maqale a daki tunda tasha matsa ta kai labari Family group dinsu. Suna ganin Likitan Hajiya da Anty sukamiqe da sauri suna tambayarsa jikinta cikeda qosawa yace musu
"Da sauqi amma kuyi haquri yanzu ku barta kar wanda ya shiga inda take saboda tana da buqatar hutu sosai"
"Toh likita cikin jikinta fa, daman ba kunce gobe zaku mata aiki ba meze hana ayi yanzu saboda gudun kar wani abu ya same shi" Hajiya ta fada se likitan ya girgiza kai yace
"Baze yuwu ba Hajiya, maganar gaskiya a yanzu haka ta sake Suma sannan jininta ya hau har ya wuce qa'ida baze yuwu muyi mata Allurar Anesthesia ba saboda idan abun yazo da tsautsayi zata iya zarcewa dole se mun jira ta farka sannan jininta ya daidaita kafin koma menene ya biyo baya, nidai roqon da zanyi muku ku barta ta huta dan Allah zuciyarta da kwakwalwarta su samu hutu sosai, Ina Mijinta ya biyo ni ina son magana dashi" daga haka ya wuce office ya barsu nan a tsaye.
Khalil ya fito daga wani office dayaga likita shima ya auna BP sa ya rubuta masa magani yace yasha ya samu yayi bacci ciwon kan nasa ze sauka, seda yaje gurin likitan daya duba Umaimah ya sake masa bayanin daya musu kafin ya fito yaje pharmacy ya siyi maganin da aka rubuta masa a gurin ya sha ya sake dawowa reception din ya tarar dasu, Abbane ya kirashi suka fita tare. Duk su biyun idan ka kallesu kasan babu me nutsuwa a cikinsu, can gurin wata bishiya suka tsaya Abban ya kalli Khalil da shi kuma yake kallon qasa yace
"Ibrahim kayi haquri ka qara akan wanda kakeyi dukda dai Allah ya sani ban rufeka ba tun kafin na baka auran Umaimah seda na zaunar dakai na gaya maka wacece ita kuma a hakan kace kaji ka gani kana sonta na tabbata a sannan baka san cewar Jidalinta ya kai har haka ba, bamu tara sani da ikon Allah kuma ita qaddarar mutum baya kauce mata badan da qila yanzu kana gudanar da rayuwarka cikin kwanciyar hankali da nutsuwa. A taqaice abinda nake so na gaya maka shine karka dauki wannan abun da tayi a matsayin wani abu da ze tsorata ka kota dakatar dakai daga yin duk abinda kayi niyya. Naji ance ta lalatawa Amarya dakinta kuma gobe ya kamata ta tare ko?"
Khalil ya gyada kai kawai se Abban yaci gaba da cewa
"Shikenan amma hakan baze canza komai ba, ka dauki dakinta da take ciki da komai ka bawa Amaryar ita kuma idan ta warke ta shere inda ta lalata ta koma ciki ban kuma yarda naji ka ce ba haka na Umarni na baka idan har ka daukeni a matsayin Uba sannan kamar yanda aka tsara tarewar Amarya a gobe idan Allah ya kaimu zan kira Kawunka nida shi zamu dakko Maka Amaryarka mu kawo maka ita idan Allah ya yarda".