← Book details Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 142 OF 267

Sashe 142

Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Ingantaccen haɗin sabaya😍* Haɗin sabayarmu duniya ne ƴar'uwa. Baza muyi miki ƙaryar nonuwanki za su taso su tsaitsaya kamar na budurwa ba, amma fa za su cicciko, suyi kyau, su dinga sheƙi, sannan duk wata rama da take jikinki za ta cicciko, ni'ima bazai yanke miki ba saboda amfani da haɗin sabayarmu.

*Muna da maganin wankin nono ga masu ciki da shayarwa.* Duk ɗauri ɗaya 500.

*Sunana Fareeda Abdallah, a kaduna nake da zama. Amma muna aikawa da magungunanmu ko ina tsakanin Nigeria da Nijer, sai dai duk inda mai siyan magani take ita za ta biya kuɗin mota ko na delivery zuwa gidanta. A tuntuɓeni ta whatsapp ko a kira ni akan lambobin wayata 07039080978, 09077591726. Sai kun zo😍😍😍*

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼

Page 54

Gadan gadan ya nufi Umaimah dake take jin tamkar numfashi ta ze dauke saboda Azabar tsoron yanayin data ga Khalil din a ciki, Hajiya da ita kanta jikinta rawa yake ta shiga tsakiyarsu, cikin muryar da bata taba jinsa da ita ba yace
"Hajiya ki matsa, ki matsa karkisa nayi Abinda Allah zeyi fushi dani"

"Khalil saurara tsaya Khalil ka tsaya nace maka" Hajiya ta fada a rude tana tokare qirjinsa da hannayenta ganin yana neman zagayeta ya isa ga Umaimah data durqushe a jikin bango tana jiran jin sauakar Aradu
"Wallahi Hajiya sena illata yarinyar nan yau sena illata Umaimah" ya fada cikin qaraji kafin Hajiya ta ce wani abu ya isa gaban Umaimah cikin qasa da second biyu ya dagota tsaye da hannu daya kafin ya sharara mata mari da daya hannun ya shaqe mata wuya duk a lokaci daya.

Kuka Hajiya ta fashe dashi ta shiga qoqarin kwatarta amma ina Ran Maza ya baci jikinsa rawa yake kamar Mazari ya zurawa Umaiman idanunsa da suka koma Ja yana kallon yanda nata idon suka firfito tana kokawa da Numfashi.
"Laure ze kashe ta kira su Sammani" Hajiya ta fada cikin kuka sanda Anty laure ta shigo dakin ta kuwa kwasa da gudu tayi waje tana kururuwar azo a taimakawa Umaiman.

Khalil kuwa seda yaji jijiyar wuyan Umaimah daya matse ta dena bugawa kafin ya saketa kamar kayan wanki a qasa ya juya a zuciye ya bar dakin. A palour ya tsaya daidai sanda yan agajin da Anty Laure ta kwaso suka shigo ya watsa musu wani kallo daya sa babu shiri suka juya kamar muna fukai suka bar gurin se ya juya yabi bayansu dan be gamsu da abinda yayi mata ba idan yaci gaba da zama a gidan tabbas ze koma ya qarasata.

Tsakanin Hajiya da Anty Laure rasa me rarrashin wani akayi sanda suka kai Umaimah data Suma Asibiti. Hankalinsu be dan kwanta ba seda Likita ya tabbatar musu da tana lafiya sunyi mata Allura dan ta danyi bacci ta samu sauqin firgicin da ta shiga. Se a sannan Anty Laure ta iya kiran Mama tana kuka tace
"Malika ashe mahaukaci kuka aurawa Umaimah? To ki taho idan kinada rabo ku gana da yarki dan ya dandana mata qamshin mutuwa gamu a Asibiti babu tabbacin ta mutu ko tana raye".

MAMA
Salati ta saka tana kallon Abba dake shan shayi jin salatinta ya sakashi kallonta shima.
"Laure ce, ban fahimci abinda take fada ba tadai ce muzo Asibiti Umaimah bata da lafiya" Maman tayi qarfin halin gaya masa se Abban ya miqe yana cewa
"Subhanallahi jikin ne ya tashi? Muje to daman na gama se mu ganota".

Seda suka shiga mota sannan ta lura da dan mayafin Abaya ne ta yafa akanta daman doguwar riga ta saka budaddiya, bata da nutsuwar da zata koma sako Hijabi haka suka tafi Abban na cewa
"Ikon Allah wannan cikin dai ya zowa Umaimah da sammatsi Allah ya rabasu lafiya"
Mama dai bata iya cewa komai ba dan tunaninta gaba daya yana can, Allah Allah takeyi su isa taga Umaiman da Laure tace tazo idan suna da rabon ganawa wane mugun abu Khalil yayi mata har haka?

Sun isa Asibitin a Reception suka tarar da Hajiya da Anty Laure kowa da inda take kallo dan bala'in haushin Hajiyar Laure takeji shiyasa tunda ta gama wayarta ta juya mata qeya tana sharar hawayen tausayin Umaiman. Tana ganin su Mama ta miqe da sauri tana sake rushewa da kuka gaban Mama ya fadi data kalli fuskokinsu, shi kansa Abban hankalin sa tashi yayi nan take suka qarasa cikin kuka Anty Laure take cewa
"Shaqeta yayi, haka muka kawota bata numfashi. Daman tunda muka koma nake lura dashi sam basa jituwa da alama wancan ciwon ma dukanta yayi shine yanzu kuma yake neman daukar ranta"

"Subhanallahi wace irin magana ce haka kikeyi Laure? Yanzu dai ina likitan naji abinda ake ciki Hajiya kiyi haquri ki dena kuka haka" Abba ya fada yana kallon Hajiya dake sharbar Hawaye har sannan jikin baiwar Allah be dena bari ba saboda yanda ta tsorata da yanayin Khalil. Gurin likitan Abba ya wuce, kamar yanda ya gayawa su Hajiya haka ya sake maimaita masa cewar babu wata matsala bacci kawai takeyi data farka komai ze daidaita. A Asibitin ya bar Mama ya wuce kasuwa haka suka zauna su ukun babu me cewa wani qala se Anty Laure ce take ta maimaita Khalil mahaukaci ne kuma idan wani abu ya samu Umaimah se sunyi qararsa.

Guraren La'asar Umaimah ta farka a firgice, Nurse ta shiga cire mata ruwan daya qare ta farka yanda taga tana zare ido ya sakata kama hannunta tana cewa
"Is ok you are in a safe hand". Umaimah ta qarewa inda take kallo ta sake maida kallonta kan Nurse din kafin a hankali cikin muryarta data dashe saboda Azabat shaqa tace
"Khalil, is he here?"
Nurse din ta girgiza mata kai alamar Aa kafin tace
"But your Mum and Aunties are outside, let me call them for you" ta dafa kafadarta cikin son kwantar mata da hankali kafin ta juya ta fita. A tare su ukun suka shiga, Umaimah na ganin Mama ta fashe da kuka Maman kanta zaro ido tayi ganin yanda gefen fuskarta ya kumbure idon ya shige ciki ga wuyanta nan inda ya shaqeta shima yayi baqi.

"Na shiga uku Hajiya me Khalil yayiwa yarinyar nan?" maman ta fada tana qarasawa kusada Umaiman, tana zuwa kuwa ta riqeta tareda qarawa kukanta qarfi tace
"Mama ki tafi dani wallahi kasheni Khalil zeyi idan na koma" ta sake fashewa da wani kuka tana tuna qanshin mutuwar dataji. Shaqar daya mata tasa sam bata ji zafin marin ba har yanzu maqogaronta a cushe yake wani mugun tsoronsa ya darsu a ranta dan ko a mafarki bata taba zaton Khalil ze aikata mata haka ba.

Rarrashinta Mama ta shigayi Hajiya da gaba daya jikinta yayi sanyi tace zataje gida ta dawo. Tana fita Anty Laure ta kalli mama tace
"Kingani ko Malika, duk lokacin da aka debo rigima se a dorawa yarinyar nan laifi gashi yanzu a gaban ido na na gani ashe cutar ta yakeyi yanzu wannan shaqar da yayi mata yau da da qarar kwana ai mu ze bari da Jimami shi bashi da asara ga mata nan birjik yana kulawa kullum da wacce zakiji shi suna waya yana qyalqyala dariya se ya shigo gurinmu ya ringa daure fuska ai wallahi ya bani mamaki".

Daga Maman Har Umaimah ido suka zuba mata, qirjij Umaimah ya shiga lugude wato ba Zahra kadai yake kulawa ba she sunada yawa? Ta tambayi kanta Mama kuwa duk ta rasa inda zata ajiye maganganu su. Ita dai tasan sedai idan Khalil shaye shaye ya fara shine kawai zeyiwa Umaimah irin wannan abun in kuwa ba haka ba toh wani mugun abun tayi masa da har ta kaishi bango wanda kadan ne daga aikinta, ita ta haifi abarta ta kusan me zatayi. Numfashi taja ta kalli Umaiman tace
"Ke me kikayi masa da har ya shaqe ki?"
"Me kuwa zatayi masa? Bafa ya nan ya tafi Zamfara yau kwana uku, ni na fita da safen naj dubo Inna ai na gaya miki shigowar da zanyi na ganshi ya sakko daga sama kamar wanda Aljanu suka koro. Ze jin kururuwar uwar sa nayi tana a kawo musu dauki da alama daman ya zaba ita take zuwa ceto ko shiyasa yau din tun kafin ya fara ta shigo" Anty Laure ta ceci Umaimah dake zare ido dan bata san me zata cewa Maman ba Kallonta Maman tayi take ta karanto zallar rashin gaskiya ko daga yanda take sunkuyar dakai kasan da wata a qasa dan haka bata qara magana ba taja bakinta tayi shiru.

Sallamar Anty ce ta katse mata shirun suka shigo tareda Salman daya ruqo kwandon Abinci, cikin jimami ta qarasa gadon tana kallon Umaiamah. Suka gaisa da Anty Laure shigowarta baby dadewa sega Nurse tace su fito likita ze dubata suka fita gaba daya Anty Laure na mayar mata da yanda akayi.

Bayan Dr ya gama dubata ya rubuta magunguna tareda Sallama ya basu. Salman ne yaje Pharmacy ya karbo ya tambayesu kudin sukace yaje kawai an saka a bill ya karbo ya dawo suka tattara suka wuce gidansu suna Hanya Hajiya ta kira Mama akan ta dawo Asibiti ance an basu sallama tace mata eh sun wuce gida. Jiki a sanyaye Hajiya tayi mata fatan samun sauqi suka kashe wayar, Anty Laure ta mere baki tace
"Da so take a mayar musu da ita su qarasa kashe mana ita ko to baze yuwu ba auren babu dole se a haqura, daman an fada ai yawancin matan da suke a qaton gidan nan in ka tona zaman da suke se kasha Mamaki amma dai yaron nan ya shammaceni yanda nake masa kallon mutumin arziqi ban zaymta haka yake ba".

Babu Wanda ya tankata har suka isa. A dakin Mama Umaimah ta kwanta bayan tayi wanka tasha kunu dan ta kasa hadiyar Abinci, maganin ma dakyar ta iya sha daga nan bacci yayi awon gaba da ita.
Chapter 142 · 0% Book details