Sashe 87
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Gaskiya sedai kije ni se zuwa yamma bana jin dadi kaina yana ciwo" Umaiman ta sake fada cikin jimami Rufaidan ta mata sannu tareda cewa bari ta shigo toh. Basufi minti goma da waya ba taji bugun qofa taje ta bude mata ta shigo ta zumbulo Hijabi da gani ko wanka ba tayi ba, seda suka zauna take tambayarta
"megidan baya nan naga babu motarsa".
Baki Umaimah ta tabe tace
"Ya tafi gidan Anty Jalila"
"Kice yau seta Allah ko ba ita ce tazo kwanaki da qanwar Mijinta ba?" Rufaida ta fada tana gyara zama Umaimah ta girgiza kai alamar Aa kafin tace
"Ba ita ba wannan Yan biyunsa ce ba Anty Amina ba ita ce babbarsu"
"Au wai yan biyune, toh Allah ya fishsheki dan kinsan idan ka hadu da yayyen Miji mata se a hankali musamman keda ake ganin kina ciki daula yanzu se kiji zantuka kala kala".
"Uhm" kawai Umaimah tace tayi shiru, hudubar Rufaida ta rigada ta gama tasiri a zuciyarta ita ta nuna mata tunda yayyen Khalil matane bazasu sota tsakani da Allah ba zasu ringa kishi da ita suna ganin Dan uwansu na bauta mata yana mata abinda su basa samu a gidan auransu dalilin da ya saka taja baya dasu dukda ko kallon banza babu wadda ta tabayi mata a cikinsu, yanzu hatta da Habiba da take yar gidanta ta rage kiranta tazo gidan acewar Rufaida zata ringa kwashe sirrinta tana kaiwa gida ita kuma taga hakan ze yuwu.
Nan suka zauna basu shiga gidan sunan ba se bayan la'asar Rufaida ta koma tayo wanka itama ta shirya bayan Hauwa ta dauki Mu'ayyad ta tafi dashi gidansu seda aka yi Isha'i suka baro gidan sunan ta shiga gida har sannan kuma Khalil be dawo ba.
Khalil
Seda ya fara biyawa gidan Abokinsa Mukhtar da yake shirin angwancewa nan da sati uku, fenti akeyi, ya duba masa aikin suka dan taba hira kafin ya wuce gidan Jalila.
Cikin murna ta tareshi dan ya dade rabonsa da gidan nata, ita kadai ya tarar se Almajirinta yana mata wanki a tsakar gida suka shiga ciki ta kawo masa ruwan Lipton da Dumamen tuwo miyar Kuka yaji man shanu.
"Kai amma Allah ya tsundumaki a Aljanna kamar kinsan na kwana biyu banci tuwo ba" ya fada sanda ya bude kwanon.
"Ai tun da kace mun yau da safe zakazo, banyi niyyar tuwo ba jiya saboda kai nayi nace dan qanina nasan ba lallai Maman Mu'ayyad nayin tuwo ba balle ka samu dumame".
Hannunsa ya wanko a Kitchen ya saka tuwon a bowl hade yake da miyar ta dumama irin yanda yake so yayi bismillah ya fara ci ita kuma ta tsiyaya masa baqin shayin daya sha kayan qamshi a kofi.
Seda ya cinye tas yasha shayin yayi hamdala, shi ya kai mata kwanukan kitchen ta rigada tayi wanke wanke dan haka ya dauraye wanda ya bata ya kife mata su a kwandon daya gani cikin sink ya futo da gorar ruwa a hannunsa.
"Ashe dai har yanzu kana aikin gida" ta fada cikin tsokana ya zauna yana murmushi yace
"Nasan mitarki idan na ajiye ban wanke ba har na tafi kina mun surutu"
"Kasan haka muke da Abbansu tun be iya wanke wanke har seda ya saba yanzu da sun bata kwanuka zece a wanke se kaji Zee tana ayi wanke wanke kafin Mama ta fara mita" suka saka dariya gaba daya.
"Ina yaran nema naji gidan shiru" ya tambayeta bayan daya zauna tace
"Kamal da Asiya sun tafi Tahfiz, Nuradden kuma yana Jalingo kasan Hajiya da Didi kuma qanwarsa ta kai su gidan kitso jiya wai sunyi dare suka kwana a gidanta inaga se anjima zata dawo dasu"
"Wai har yanzu Nuraddeen be dawo ku haqura da yaron nan kawai ku bar musu shi mana" Khalil ya fada tayi murmushi tace
"nima haka nace jiya da yake zancen ze kira Hajiyar ya gaya mata an dade da komawa makaranta nace ai sun sani ka barshi kawai yayi zamansa nan da can ai duk daya ne toh kasan shi da qulafucin Yaya bedai ce komai ba kuma be kirata ba yana dai mitar wai Nura nada wasa baya sonkaratu idan ba an takura masa ba acan in ya samu sake sangarcewa zeyi"
"Haka dai ze haqura ya barshi da ya samu kakannin ma masu so su riqe jikan, nan Hajiya data dauko Inteen kina ganin yanda suka qare" Khalil ya fada suka fashe da dariya gaba daya. Seda suka lafa Jalila ta kalle shi tace
"Toh ya ake ciki ranar mun fara magana a waya?"
Tattara hankalinsa yayi akanta yace
"Wato wata yarinya ce muka hadu da ita kin gane, harga Allah tana burgeni kuma ina sonta amma kuma ni banyi tunanin nan kusa zata kawo maganar muyi aure ko wani abu ba kuma ita bala'in sona takeyi, nidai in taqaice miki magana yanzu kinsan dai matsayin da nake ciki a yanzu bazance zanyi aure ba saboda kowa seya tambayeni dalili idan kika duba aurena shekara biyu kwata kwata ni kuma bani da wani dalili me qarfi dazance gashi ya saka zanyi aure".
Shiru Jalila tayi tana kallonsa har ya kai aya kafin taja numfashi tace
"Ita yarinyar yaushe kuka hadu, kuma tsahon wane lokaci kuke tare?"
"Bamu wani dade ba wata uku zuwa hudu kenan da haduwarmu lokacin da naje aiki Lagos din nan, dukda dai mun taba haduwa a nan Kano amma dai Officially mu fara magana da ita yanzu za'ayi 3 months" Khalil ya bata amsa tayi shiru tana kallonsa, so takeyi tace masa lokacin da Umaimah taqi binsa Lagos kenan kuma ta tambayeshi wace irin alaqa ce tsakaninsu dukda bata zargin qanin nata amma tasan abinda Umaiman tayi masa yana iya sakawa shedan ya zugashi ya fada abinda ba halinsa ba. Itama ta samu labarin ne a bakin Khalifa kuma ya roqeta akan dan Allah karta gayawa Kowa dan Yaya Khalil yaja masa kunne kawai ya kasa hadiye maganar ne yasa ya gaya mata dan ita ana sirri da ita ba irin su Yaya Jamila faransai bace.
"Kinyi shiru kina kallona kamar wanda nayi miki qarya" Khalil ya fada se tayi murmushi tace
"So nake na auna soyayyar da kakeyi mata da irin wadda na gani a idonka sanda kake gaya mun ka hadu da Umaimah"
"Babu hadi Jalila babu macen da zata kamo qafar Umaimah a zuciyata" Khalil yayi saurin tareta a zuciyarta tace
"Ta gano lagon ka shiyasa take garaka kamar kwallo a fili kuwa seta gyara zamanta tace
"Toh tanada wannan matsayin ya akayi har idonka ya iya hange hange ka samo wata ka fara so, kuma a yanda kake jaddada soyayyar nan tata ace a ayan shekarun nan zaka mata kishiya Khalil?
Idan har da gaske ka daukeni yar uwar da zamu kashe mu rufe ka gaya mun gaskiyar meye damuwarka, meye dalilinka na son qara aure? Ni kuma zanyi maka hukunci bisa adalci in sha Allah dan bazan so ka tauye kanka ba haka itama Umaimah bazan bi bayanka kayi mata rashin Adalci idan har ya zamana son ranka ne kawai".
Shiru Khalil yayi yana nanawa maganarta a zuciyarsa, yanada yaqinin Jalila zata riqe masa sirri idan ya gaya mata amma yana tsoron ta farayiwa Umaimah wani kallo na daban a matsayin me musgunawa dan uwanta, yasan zata qullaceta dan Jalilan nason duk abinda yake so tana kuma qin abinda yake bata masa.
"Kayi shiru dan qanina ko da akwai matsala ne" ta fada cikin tsokana ya dago ya harareta tayi dariya tace
"Sarkin son girma duk tsiyarka dai minti biyar ba wasa bace" dole yayi murmushin shima ta sake cewa
"Yawwa ina jinka kayi magana mu samu mu san ta inda zamu kamo bakin zaren maganar nan"
"Kina ji Jalila ina son Umaimah kuma bani da wata matsala da ita, damuwata guda daya ce kawai yanayin aikina da bana zama guri daya a koda yaushe ana turani garuruwa nayi ayyuka kuma ina yin kwanaki wani lokacin ma satittika ni kuma ina da sha'awar duk ina zani na tafi da Matata, matsalar anan ita kuma Umaimah bata son tafiya.
Duk sanda wata tafiya ta taso se rayukan mu sun baci kafin ta bini, kinga last tafiyar da nayi Lagos har na gama zamana na dawo bataje ba acan nema na hadu da Hadiza dan a lokacin fushin da nake ciki na yanke shawarar aure kawai zan qara na auro wadda ko bangon duniya nace zanje zata bini"
Yaci gaba da bata labarin yanda ya hadu da Hadiza da irin soyayyar fa sukayi har zuwa matsayin da suke yanzu akai na zancen turowa da tayi masa. Ya rufe da cewa
"Banaso haqqinta ya kamani dan dagaske yarinyar tana so na ni kuma bansan ya zanyi ba yanzu.
Tun bayan dawowata na tuntubi Hajiya da maganar dan naji ta bakinta tayi futufutu tace babu wannan maganar ba yanzu ba har gaba babu ita.
Toh ni maganar Hajiya ma da sauqi nasan idan na lallabata tana iya yarda, Umaimah nada bala'in kishi irin wanda bakiyi tunani ba, idan zancen auran nan ya fito na tabbata babu sauran zaman lafiya tsakanin mu".
"Hmmmm" Jalila taja dogon numfashi tareda sauke taguminda tayi tana kallon Khalil tace
"Ni har na rasa ta ina zanfara ma, idan na fahimceka abinda yasa ka fara kula Sabuwarka saboda rashin Umaimah a kusa ne bari na fara da wannan bangaren in har kana ganin cewar Umaimah bazata haqura ta ringa binka duk inda zakaje ba kana da hujjar da zaka qara aure kuma duk wanda ka gayawa dalilinka baze hanaka ba kodan gudun fadawa halaka.
Amma idan shawara kake nema se nace maka qarin aure ba shine mafita ba ka zauna da ita kuyi magana ta fahimta ka nuna mata buqatarka da abinda bijirewa hakan ze iya janyowa idan har bata gyara ba daga nan kana iya daukar mataki na gaba sannan ita wannan Hadiza kace kowa sunanta ba son ta kakeyi ba, Umaimah ta riga ta siye filin a ganina ka saurareta ne kawai a lokacin saboda fushin Umaimah inda dagaske ka gantan kake sonta zuciyarka bazata kawo maka wani tunani ba balle har kaji shayin tunkarar kowa da maganar auranta.
"megidan baya nan naga babu motarsa".
Baki Umaimah ta tabe tace
"Ya tafi gidan Anty Jalila"
"Kice yau seta Allah ko ba ita ce tazo kwanaki da qanwar Mijinta ba?" Rufaida ta fada tana gyara zama Umaimah ta girgiza kai alamar Aa kafin tace
"Ba ita ba wannan Yan biyunsa ce ba Anty Amina ba ita ce babbarsu"
"Au wai yan biyune, toh Allah ya fishsheki dan kinsan idan ka hadu da yayyen Miji mata se a hankali musamman keda ake ganin kina ciki daula yanzu se kiji zantuka kala kala".
"Uhm" kawai Umaimah tace tayi shiru, hudubar Rufaida ta rigada ta gama tasiri a zuciyarta ita ta nuna mata tunda yayyen Khalil matane bazasu sota tsakani da Allah ba zasu ringa kishi da ita suna ganin Dan uwansu na bauta mata yana mata abinda su basa samu a gidan auransu dalilin da ya saka taja baya dasu dukda ko kallon banza babu wadda ta tabayi mata a cikinsu, yanzu hatta da Habiba da take yar gidanta ta rage kiranta tazo gidan acewar Rufaida zata ringa kwashe sirrinta tana kaiwa gida ita kuma taga hakan ze yuwu.
Nan suka zauna basu shiga gidan sunan ba se bayan la'asar Rufaida ta koma tayo wanka itama ta shirya bayan Hauwa ta dauki Mu'ayyad ta tafi dashi gidansu seda aka yi Isha'i suka baro gidan sunan ta shiga gida har sannan kuma Khalil be dawo ba.
Khalil
Seda ya fara biyawa gidan Abokinsa Mukhtar da yake shirin angwancewa nan da sati uku, fenti akeyi, ya duba masa aikin suka dan taba hira kafin ya wuce gidan Jalila.
Cikin murna ta tareshi dan ya dade rabonsa da gidan nata, ita kadai ya tarar se Almajirinta yana mata wanki a tsakar gida suka shiga ciki ta kawo masa ruwan Lipton da Dumamen tuwo miyar Kuka yaji man shanu.
"Kai amma Allah ya tsundumaki a Aljanna kamar kinsan na kwana biyu banci tuwo ba" ya fada sanda ya bude kwanon.
"Ai tun da kace mun yau da safe zakazo, banyi niyyar tuwo ba jiya saboda kai nayi nace dan qanina nasan ba lallai Maman Mu'ayyad nayin tuwo ba balle ka samu dumame".
Hannunsa ya wanko a Kitchen ya saka tuwon a bowl hade yake da miyar ta dumama irin yanda yake so yayi bismillah ya fara ci ita kuma ta tsiyaya masa baqin shayin daya sha kayan qamshi a kofi.
Seda ya cinye tas yasha shayin yayi hamdala, shi ya kai mata kwanukan kitchen ta rigada tayi wanke wanke dan haka ya dauraye wanda ya bata ya kife mata su a kwandon daya gani cikin sink ya futo da gorar ruwa a hannunsa.
"Ashe dai har yanzu kana aikin gida" ta fada cikin tsokana ya zauna yana murmushi yace
"Nasan mitarki idan na ajiye ban wanke ba har na tafi kina mun surutu"
"Kasan haka muke da Abbansu tun be iya wanke wanke har seda ya saba yanzu da sun bata kwanuka zece a wanke se kaji Zee tana ayi wanke wanke kafin Mama ta fara mita" suka saka dariya gaba daya.
"Ina yaran nema naji gidan shiru" ya tambayeta bayan daya zauna tace
"Kamal da Asiya sun tafi Tahfiz, Nuradden kuma yana Jalingo kasan Hajiya da Didi kuma qanwarsa ta kai su gidan kitso jiya wai sunyi dare suka kwana a gidanta inaga se anjima zata dawo dasu"
"Wai har yanzu Nuraddeen be dawo ku haqura da yaron nan kawai ku bar musu shi mana" Khalil ya fada tayi murmushi tace
"nima haka nace jiya da yake zancen ze kira Hajiyar ya gaya mata an dade da komawa makaranta nace ai sun sani ka barshi kawai yayi zamansa nan da can ai duk daya ne toh kasan shi da qulafucin Yaya bedai ce komai ba kuma be kirata ba yana dai mitar wai Nura nada wasa baya sonkaratu idan ba an takura masa ba acan in ya samu sake sangarcewa zeyi"
"Haka dai ze haqura ya barshi da ya samu kakannin ma masu so su riqe jikan, nan Hajiya data dauko Inteen kina ganin yanda suka qare" Khalil ya fada suka fashe da dariya gaba daya. Seda suka lafa Jalila ta kalle shi tace
"Toh ya ake ciki ranar mun fara magana a waya?"
Tattara hankalinsa yayi akanta yace
"Wato wata yarinya ce muka hadu da ita kin gane, harga Allah tana burgeni kuma ina sonta amma kuma ni banyi tunanin nan kusa zata kawo maganar muyi aure ko wani abu ba kuma ita bala'in sona takeyi, nidai in taqaice miki magana yanzu kinsan dai matsayin da nake ciki a yanzu bazance zanyi aure ba saboda kowa seya tambayeni dalili idan kika duba aurena shekara biyu kwata kwata ni kuma bani da wani dalili me qarfi dazance gashi ya saka zanyi aure".
Shiru Jalila tayi tana kallonsa har ya kai aya kafin taja numfashi tace
"Ita yarinyar yaushe kuka hadu, kuma tsahon wane lokaci kuke tare?"
"Bamu wani dade ba wata uku zuwa hudu kenan da haduwarmu lokacin da naje aiki Lagos din nan, dukda dai mun taba haduwa a nan Kano amma dai Officially mu fara magana da ita yanzu za'ayi 3 months" Khalil ya bata amsa tayi shiru tana kallonsa, so takeyi tace masa lokacin da Umaimah taqi binsa Lagos kenan kuma ta tambayeshi wace irin alaqa ce tsakaninsu dukda bata zargin qanin nata amma tasan abinda Umaiman tayi masa yana iya sakawa shedan ya zugashi ya fada abinda ba halinsa ba. Itama ta samu labarin ne a bakin Khalifa kuma ya roqeta akan dan Allah karta gayawa Kowa dan Yaya Khalil yaja masa kunne kawai ya kasa hadiye maganar ne yasa ya gaya mata dan ita ana sirri da ita ba irin su Yaya Jamila faransai bace.
"Kinyi shiru kina kallona kamar wanda nayi miki qarya" Khalil ya fada se tayi murmushi tace
"So nake na auna soyayyar da kakeyi mata da irin wadda na gani a idonka sanda kake gaya mun ka hadu da Umaimah"
"Babu hadi Jalila babu macen da zata kamo qafar Umaimah a zuciyata" Khalil yayi saurin tareta a zuciyarta tace
"Ta gano lagon ka shiyasa take garaka kamar kwallo a fili kuwa seta gyara zamanta tace
"Toh tanada wannan matsayin ya akayi har idonka ya iya hange hange ka samo wata ka fara so, kuma a yanda kake jaddada soyayyar nan tata ace a ayan shekarun nan zaka mata kishiya Khalil?
Idan har da gaske ka daukeni yar uwar da zamu kashe mu rufe ka gaya mun gaskiyar meye damuwarka, meye dalilinka na son qara aure? Ni kuma zanyi maka hukunci bisa adalci in sha Allah dan bazan so ka tauye kanka ba haka itama Umaimah bazan bi bayanka kayi mata rashin Adalci idan har ya zamana son ranka ne kawai".
Shiru Khalil yayi yana nanawa maganarta a zuciyarsa, yanada yaqinin Jalila zata riqe masa sirri idan ya gaya mata amma yana tsoron ta farayiwa Umaimah wani kallo na daban a matsayin me musgunawa dan uwanta, yasan zata qullaceta dan Jalilan nason duk abinda yake so tana kuma qin abinda yake bata masa.
"Kayi shiru dan qanina ko da akwai matsala ne" ta fada cikin tsokana ya dago ya harareta tayi dariya tace
"Sarkin son girma duk tsiyarka dai minti biyar ba wasa bace" dole yayi murmushin shima ta sake cewa
"Yawwa ina jinka kayi magana mu samu mu san ta inda zamu kamo bakin zaren maganar nan"
"Kina ji Jalila ina son Umaimah kuma bani da wata matsala da ita, damuwata guda daya ce kawai yanayin aikina da bana zama guri daya a koda yaushe ana turani garuruwa nayi ayyuka kuma ina yin kwanaki wani lokacin ma satittika ni kuma ina da sha'awar duk ina zani na tafi da Matata, matsalar anan ita kuma Umaimah bata son tafiya.
Duk sanda wata tafiya ta taso se rayukan mu sun baci kafin ta bini, kinga last tafiyar da nayi Lagos har na gama zamana na dawo bataje ba acan nema na hadu da Hadiza dan a lokacin fushin da nake ciki na yanke shawarar aure kawai zan qara na auro wadda ko bangon duniya nace zanje zata bini"
Yaci gaba da bata labarin yanda ya hadu da Hadiza da irin soyayyar fa sukayi har zuwa matsayin da suke yanzu akai na zancen turowa da tayi masa. Ya rufe da cewa
"Banaso haqqinta ya kamani dan dagaske yarinyar tana so na ni kuma bansan ya zanyi ba yanzu.
Tun bayan dawowata na tuntubi Hajiya da maganar dan naji ta bakinta tayi futufutu tace babu wannan maganar ba yanzu ba har gaba babu ita.
Toh ni maganar Hajiya ma da sauqi nasan idan na lallabata tana iya yarda, Umaimah nada bala'in kishi irin wanda bakiyi tunani ba, idan zancen auran nan ya fito na tabbata babu sauran zaman lafiya tsakanin mu".
"Hmmmm" Jalila taja dogon numfashi tareda sauke taguminda tayi tana kallon Khalil tace
"Ni har na rasa ta ina zanfara ma, idan na fahimceka abinda yasa ka fara kula Sabuwarka saboda rashin Umaimah a kusa ne bari na fara da wannan bangaren in har kana ganin cewar Umaimah bazata haqura ta ringa binka duk inda zakaje ba kana da hujjar da zaka qara aure kuma duk wanda ka gayawa dalilinka baze hanaka ba kodan gudun fadawa halaka.
Amma idan shawara kake nema se nace maka qarin aure ba shine mafita ba ka zauna da ita kuyi magana ta fahimta ka nuna mata buqatarka da abinda bijirewa hakan ze iya janyowa idan har bata gyara ba daga nan kana iya daukar mataki na gaba sannan ita wannan Hadiza kace kowa sunanta ba son ta kakeyi ba, Umaimah ta riga ta siye filin a ganina ka saurareta ne kawai a lokacin saboda fushin Umaimah inda dagaske ka gantan kake sonta zuciyarka bazata kawo maka wani tunani ba balle har kaji shayin tunkarar kowa da maganar auranta.