Sashe 169
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonsa Hajiya ta ringayi har ya kai qarshe kafin ta sauke ajiyar zuciya tace
"Babana dagask dai kake da maganar aurannan, ni da zaka bi ta tawa da ka haqura da matarka ita kadai yanzu kuna zamanku lafiya so kakeyi ka dakko wata da zata zo ta jawo maka tashin hankali da damuwa...."
"Hajiya" ya kira sunanta cikin marairaicewa abinda yasa ta dakata da maganar da takeyi kafin yaci gaba da cewa
"Dan Allah Hajiya na roqeki da ko saka albarka a abun nan ki dena yi mun fatan tashin hankali ko damuwa. Hajiya ni nake zaune da Umaimah ni nasan dadinta ko akasin haka tunda har nazo miki da buqatar ina son qari ki barni dan Allah".
"Shikenan Allah ubangiji ya tabbatar da Alkhairi yasa ayi a sa'a, amma ina so kafin a kai ga yin magana ka fara sanar da matarka tukunna, idan ta karbi abun ta fuskar limana shikenan idan kuma ba haka ba dole a qara lokaci zuwa sanda abubuwa zasu qara sauqaqa kaga ita ma kafin nan yarinyar ta qara girma se ayi komai cikin dadin rai da kwanciyar hankali" Hajiyan ta sak fada, ajiyar zuciya yayi yana kallon qasa yace mata
"In sha Allahu babu abinda zero faru is Alkhairi, yanzu dai ki sanarwa da Baba Abun duk abunda suka yanke shikenan" ya sak jaddada mata dan gaba daya kalaman na Hajiya yau jinsu yakeyi akwai son kai a ciki, yanda kasan Umaimah ta haifa ba shi ba yanzu tana nufin kenan seda Amincewar Umaimah zeyi aure idan ba haka ba sedai a fasa kenan.
Sallama yayi mata ya wuce bangarensu, a falon qasan ya tarar da Umaimah tana kwance a qasa tana danna waya. Ba yabo ba fallasa ta amsa sallamarsa tareda yi masa sannu da zuwa, daga kwancen ta nuna masa Dining inda abincinsa yake ya wuce ya zauna yana duba abinda suka dafa. Gurasa ce da gasashshan nama se kunun Aya ga Qaramin flask na Tea dinsa an ajiye ya zuba abinda ze iya ci yayi bismillah ya fara lokaci lokaci yana kallon Umaiman dake kwance har sannan a zuciyarsa yana ayyana ta yanda ze sanar mata da zancen auran har ya gama ya tashi daga gurin. Kusada ita ya koma ya zauan ya dauki remote ya chanza tasha zuwa labarai ya tsurawa Tv ido badan yana fuskantar abinda ake cewa a ciki ba yana nan zaune se ji yayi tana masa sallama zata shige daki, miqewa tsaye yayi shima gaba daya bakinsa ya masa nauyi yana nan tunanin me zece mata harta shige ta kullo qofarta seya sauke ajiyar zuciya ya kashe Tv ya haye sama shima dan tuni Ruqayya ta kwashe kayan abincin daya gama.
A daren kasa bacci yayi, kwana yayi yana saqa da warwarar yanda ze gayawa Umaimah zancen auran nasa daga qarshe ya yanke shawarar komawa ya sake samun Hajiya ya lallabata ita ta gaya mata dan gaskiya yana shakkar kallon idonta yazo mata da wannan zance be san a yanda zata dauki al'amarin ba yasan idan Hajiyar ce zata fi fahimtarta akansa.
UMAIMAH
Tun bayan da taje tayi tijara a gidansu Humairah ta kwantar da hankalinta dan gani takeyi barazanar da tayi musu ta isa ta saka a fasa auran musamman da Khalil beyi mata maganar ba kenan sunji tsoro basu gaya masa ba qila dai an rusa maganar to koma dai menene ita dai tayi abinda tayi cansu gane ba matsalarta bace koda Rufaida ta dawo kamar yanda tayi alqawari taje gidan se kawai tace mata babu komai, daman abu ne ya taso mata kuma ta rigada tayi daman bata sake bi takan Safinah ba dan ita shawararta a gunta ba mafita bace.
Lafiya lau take ci gaba da zuba mulkinta, yanda Khalil din yake ta tata yana tarairayarta ya sake tabbatar mata da cewar babu waccen magana ta rusata dan haka ta saki ranta take sabgoginta. Hajiya ce dai ta dauke mata wuta ba kamar yanda suke a da ba tunda ta fahimci da hadin bakinta aka so ayi mata qullalliya shikenan ta qullaceta shigar da takeyi part dinta ta dena sau daya take leqawa ta gaisheta ba kuma ta zama suyi hira kamar yanda suka saba zata koma bangarenta su kansu yaran yanzu janye su takeyi da sun dawo daga makaranta suka shiga bazata barsu su koma part din Hajiyar ba se kwanciya bacci shima din saboda ba zata iya zirga zirgar tashi sakasu fitsari ba ne amma ta qudurce a ranta data haihu zata tattaro yaranta gaba daya su dawo gurinta tunda itama fuska biyu ce da Hajiyan toh su zuba su gani.
A bangaren Hajiya ma kwana tayi tana juya maganganun Khalil din, har ga Allah ita dai bata son qarin auran nan daya dakko ba kuma dan komai ba se dan gudun tashin hankalin da ze iya faruwa a gidan. Iya abubuwan da suka faru a baya sun isa ishara a sannan ma hasashene ya saka Umaiman aikata abinda tayi ballantana a yanzu da zancen auran na gaske ke shirin qulluwa, ita duk ba wannan ba yarinyar daya dakko yake son auran kanta abar tausayice bata yi kwarin da za'a hadata kishi da mace kamar Umaimah ba banda ma abu irin na Namiji idan auran yake so meze hana yaj ya nemo babbar Mace amma ya dage se wannanyar yarinyar. Haka ta ringa juye tana saqa yanda abubuwan zasu kasance, a yanda ya bude baki har yake mata magana ta tabbatar da har zuci yake son auran nan kuma idan tace zatayi amfani da qarfinta na Uwa ta tauye shi batayi masa Adalci ba dan haka dole ta haqura ta barshi yayi, amma badai ya auri wanann yarinyar ba sedai yaje can ya samo wadda zata iya gogawa da Umaiman dan idan ta bari akayi wannan hadin tamkar daukar Alhaki ne. Ita kanta Hajiya Hauwan tayi mamaki data yarda da wannan hadi amma zuwa da safe zata kiraya suyi magana ta fahimta ta yanda su da kansu zasu fasa bashi auran ta haka komai zero warware ba tareda yayi zargin ita ta hana ba. Da wannan shawara tayi Na'am ta kiran Hajiya Hauwa amma kafin nan zata tara sauran yaranta mata dan taji shawarar su akan wannan al'amari kafin ta yanke hukunci.
Washe gari kuwa da safe ta kira Amina ta shaida mata tana son ganinsu gaba daya yau, babu bata lokaci kuwa Aminan ta kira Jamila da Jalilah ta gaya musu daman Habiba na gida dan haka kafin qarfe tara na safe gaba daya sun hallara a gidan saboda amsa kiran Hajiyar kowacce zuciyarta cike da son jin ba'asin wannan kiran gaggawa haka.
A taqaice Hajiyar tayi musu bayanin dalilin kiran nasu da tayi, Jalilah taja kabbara harda daga hannaye tace
"Alhamdulillahi Allah na gode maka daka nuna mun wannan rana da raina ban mutu ba, ai wallahi na dade da wannan qudurin kuma koda ace Khalil be nemo aure ba ni da kaina zan nemo masa to gashi yayiwa kansa tunani me kyau kai wallahi naji dadi, Allah ya tabbatar da Alkhairi ya nuna mana lokaci"
Jamila da tayi tagumi ce ta janye tana cewa
"Toni abin ne na rasa me zanyi, murna ce ko kuma fargaba? Yin auran abu ne me kyau amma ni tashin hankalin da matarsa zatayi shi nake tsoro wallahi"
"Kamar kin shiga raina Jamila ni kaina abinda kawai nake hasasowa kenan, gashi Hajiua tace yarinya ce qarama idan da ace ma wata babbace da zasu iya gogawa da sauqi amma yanzu ya auro yarinyar mutane tayita azabtar da ita ai anyi ba ayi ba kenan" Anty Amina ta goyi da bayan Jamilan, Hajiya na shirin magana Jalilah ta taresu da cewa
"Oh saboda ana gudun Jidalinta shikenan shikenan se yayita zama yana tauye kansa shi bazeji dadin aure ba to ko jaririya ya nemo haka ze aurota kuma babu abinda ta isa tayi mata da ikon Allah taci zamaninta yanzu kuwa sedai ta zama yar kallo a gidan Khalil. Ni bari na kirashi ma yazo muji yanda za'ayi da batun hada lefe gara ayi komai da wuri bana son bata lokaci".
Duk ta yanda suka so kawo suka akan lamarin auran seda tabi ta kanainaye musamman da Khalifa ya shigo shima ya mara mata baya seda suka san yanda suka ja ra'ayin Jamila da Aminan suka Aminta da zancen auran dukda daman su bawai basa so yayin bane, Aa Jidalin Umaimah suke tunani da kuma tausayin ita wadda akace yana so ze aura din suna ganin tayi qanqanta a hadata kishi da Umaimah. Hajiya da tunda suka fara bata ce musu komai ba tayi ajiyar numfashi tace
"Yanzu meye matsayarku akan maganar nan? Nidai har ga zuciyata bawai bana son auran nan ba Aa tunanin abinda zeje ya dawo nakeyi, bana son tashin hankali musamman a matsayin da yarinyar nan take ciki gata da taohon ciki kuma daman tun samuwar cikin ake ta turka turka daga wannan se wannan bana son abinda ze zo ya taba lafiyarta ko ta abinda yake cikinta amma kuma bazan so na zama me son kai ba shima Babana na tauyeshi, dan haka mecece shawararku ta qarshe akan abinda ya kamata muyi?"
Anty Amina ce tayi magana tace
"Nidai Hajiya ina ganin tunda har Khalil ya furta yana so yayi aure ki barshi yayi ki kuma bishi da Addu'a Allah yasa hakan ya zama Alkhairi ya kuma bashi ikon yin Adalci a tsakaninsu. Amma yanzu yayi haquri ya dakata da maganar auran har zuwa Umaimah ta haihu saboda kowa yasan halinta, bazata dubi halin da take ciki ba tsaf zata illata kanta ta illata abinda ke cikinta a banza saboda haukan kishi dan haka yaci gaba da naman auransa a hankali har zuwa sanda Allah ze tabbatar".
Jalilah da Jamila sunyi Na'am da maganarta amma seda Jalilan ta qara da cewa
"Amma kamar yanda yace iyayenta sunce ya tura idan da gaske yake to ya kamata ayi hakan kinga shine shaidar yana nema manya su shiga cikin magana, daga nan za'a iya jan lokaci ta fara makaranta ma zuwa sannan ta qara wayo da sanin yanda duniya take kafin azo ga batun aure ko ba haka ba?"
"Babana dagask dai kake da maganar aurannan, ni da zaka bi ta tawa da ka haqura da matarka ita kadai yanzu kuna zamanku lafiya so kakeyi ka dakko wata da zata zo ta jawo maka tashin hankali da damuwa...."
"Hajiya" ya kira sunanta cikin marairaicewa abinda yasa ta dakata da maganar da takeyi kafin yaci gaba da cewa
"Dan Allah Hajiya na roqeki da ko saka albarka a abun nan ki dena yi mun fatan tashin hankali ko damuwa. Hajiya ni nake zaune da Umaimah ni nasan dadinta ko akasin haka tunda har nazo miki da buqatar ina son qari ki barni dan Allah".
"Shikenan Allah ubangiji ya tabbatar da Alkhairi yasa ayi a sa'a, amma ina so kafin a kai ga yin magana ka fara sanar da matarka tukunna, idan ta karbi abun ta fuskar limana shikenan idan kuma ba haka ba dole a qara lokaci zuwa sanda abubuwa zasu qara sauqaqa kaga ita ma kafin nan yarinyar ta qara girma se ayi komai cikin dadin rai da kwanciyar hankali" Hajiyan ta sak fada, ajiyar zuciya yayi yana kallon qasa yace mata
"In sha Allahu babu abinda zero faru is Alkhairi, yanzu dai ki sanarwa da Baba Abun duk abunda suka yanke shikenan" ya sak jaddada mata dan gaba daya kalaman na Hajiya yau jinsu yakeyi akwai son kai a ciki, yanda kasan Umaimah ta haifa ba shi ba yanzu tana nufin kenan seda Amincewar Umaimah zeyi aure idan ba haka ba sedai a fasa kenan.
Sallama yayi mata ya wuce bangarensu, a falon qasan ya tarar da Umaimah tana kwance a qasa tana danna waya. Ba yabo ba fallasa ta amsa sallamarsa tareda yi masa sannu da zuwa, daga kwancen ta nuna masa Dining inda abincinsa yake ya wuce ya zauna yana duba abinda suka dafa. Gurasa ce da gasashshan nama se kunun Aya ga Qaramin flask na Tea dinsa an ajiye ya zuba abinda ze iya ci yayi bismillah ya fara lokaci lokaci yana kallon Umaiman dake kwance har sannan a zuciyarsa yana ayyana ta yanda ze sanar mata da zancen auran har ya gama ya tashi daga gurin. Kusada ita ya koma ya zauan ya dauki remote ya chanza tasha zuwa labarai ya tsurawa Tv ido badan yana fuskantar abinda ake cewa a ciki ba yana nan zaune se ji yayi tana masa sallama zata shige daki, miqewa tsaye yayi shima gaba daya bakinsa ya masa nauyi yana nan tunanin me zece mata harta shige ta kullo qofarta seya sauke ajiyar zuciya ya kashe Tv ya haye sama shima dan tuni Ruqayya ta kwashe kayan abincin daya gama.
A daren kasa bacci yayi, kwana yayi yana saqa da warwarar yanda ze gayawa Umaimah zancen auran nasa daga qarshe ya yanke shawarar komawa ya sake samun Hajiya ya lallabata ita ta gaya mata dan gaskiya yana shakkar kallon idonta yazo mata da wannan zance be san a yanda zata dauki al'amarin ba yasan idan Hajiyar ce zata fi fahimtarta akansa.
UMAIMAH
Tun bayan da taje tayi tijara a gidansu Humairah ta kwantar da hankalinta dan gani takeyi barazanar da tayi musu ta isa ta saka a fasa auran musamman da Khalil beyi mata maganar ba kenan sunji tsoro basu gaya masa ba qila dai an rusa maganar to koma dai menene ita dai tayi abinda tayi cansu gane ba matsalarta bace koda Rufaida ta dawo kamar yanda tayi alqawari taje gidan se kawai tace mata babu komai, daman abu ne ya taso mata kuma ta rigada tayi daman bata sake bi takan Safinah ba dan ita shawararta a gunta ba mafita bace.
Lafiya lau take ci gaba da zuba mulkinta, yanda Khalil din yake ta tata yana tarairayarta ya sake tabbatar mata da cewar babu waccen magana ta rusata dan haka ta saki ranta take sabgoginta. Hajiya ce dai ta dauke mata wuta ba kamar yanda suke a da ba tunda ta fahimci da hadin bakinta aka so ayi mata qullalliya shikenan ta qullaceta shigar da takeyi part dinta ta dena sau daya take leqawa ta gaisheta ba kuma ta zama suyi hira kamar yanda suka saba zata koma bangarenta su kansu yaran yanzu janye su takeyi da sun dawo daga makaranta suka shiga bazata barsu su koma part din Hajiyar ba se kwanciya bacci shima din saboda ba zata iya zirga zirgar tashi sakasu fitsari ba ne amma ta qudurce a ranta data haihu zata tattaro yaranta gaba daya su dawo gurinta tunda itama fuska biyu ce da Hajiyan toh su zuba su gani.
A bangaren Hajiya ma kwana tayi tana juya maganganun Khalil din, har ga Allah ita dai bata son qarin auran nan daya dakko ba kuma dan komai ba se dan gudun tashin hankalin da ze iya faruwa a gidan. Iya abubuwan da suka faru a baya sun isa ishara a sannan ma hasashene ya saka Umaiman aikata abinda tayi ballantana a yanzu da zancen auran na gaske ke shirin qulluwa, ita duk ba wannan ba yarinyar daya dakko yake son auran kanta abar tausayice bata yi kwarin da za'a hadata kishi da mace kamar Umaimah ba banda ma abu irin na Namiji idan auran yake so meze hana yaj ya nemo babbar Mace amma ya dage se wannanyar yarinyar. Haka ta ringa juye tana saqa yanda abubuwan zasu kasance, a yanda ya bude baki har yake mata magana ta tabbatar da har zuci yake son auran nan kuma idan tace zatayi amfani da qarfinta na Uwa ta tauye shi batayi masa Adalci ba dan haka dole ta haqura ta barshi yayi, amma badai ya auri wanann yarinyar ba sedai yaje can ya samo wadda zata iya gogawa da Umaiman dan idan ta bari akayi wannan hadin tamkar daukar Alhaki ne. Ita kanta Hajiya Hauwan tayi mamaki data yarda da wannan hadi amma zuwa da safe zata kiraya suyi magana ta fahimta ta yanda su da kansu zasu fasa bashi auran ta haka komai zero warware ba tareda yayi zargin ita ta hana ba. Da wannan shawara tayi Na'am ta kiran Hajiya Hauwa amma kafin nan zata tara sauran yaranta mata dan taji shawarar su akan wannan al'amari kafin ta yanke hukunci.
Washe gari kuwa da safe ta kira Amina ta shaida mata tana son ganinsu gaba daya yau, babu bata lokaci kuwa Aminan ta kira Jamila da Jalilah ta gaya musu daman Habiba na gida dan haka kafin qarfe tara na safe gaba daya sun hallara a gidan saboda amsa kiran Hajiyar kowacce zuciyarta cike da son jin ba'asin wannan kiran gaggawa haka.
A taqaice Hajiyar tayi musu bayanin dalilin kiran nasu da tayi, Jalilah taja kabbara harda daga hannaye tace
"Alhamdulillahi Allah na gode maka daka nuna mun wannan rana da raina ban mutu ba, ai wallahi na dade da wannan qudurin kuma koda ace Khalil be nemo aure ba ni da kaina zan nemo masa to gashi yayiwa kansa tunani me kyau kai wallahi naji dadi, Allah ya tabbatar da Alkhairi ya nuna mana lokaci"
Jamila da tayi tagumi ce ta janye tana cewa
"Toni abin ne na rasa me zanyi, murna ce ko kuma fargaba? Yin auran abu ne me kyau amma ni tashin hankalin da matarsa zatayi shi nake tsoro wallahi"
"Kamar kin shiga raina Jamila ni kaina abinda kawai nake hasasowa kenan, gashi Hajiua tace yarinya ce qarama idan da ace ma wata babbace da zasu iya gogawa da sauqi amma yanzu ya auro yarinyar mutane tayita azabtar da ita ai anyi ba ayi ba kenan" Anty Amina ta goyi da bayan Jamilan, Hajiya na shirin magana Jalilah ta taresu da cewa
"Oh saboda ana gudun Jidalinta shikenan shikenan se yayita zama yana tauye kansa shi bazeji dadin aure ba to ko jaririya ya nemo haka ze aurota kuma babu abinda ta isa tayi mata da ikon Allah taci zamaninta yanzu kuwa sedai ta zama yar kallo a gidan Khalil. Ni bari na kirashi ma yazo muji yanda za'ayi da batun hada lefe gara ayi komai da wuri bana son bata lokaci".
Duk ta yanda suka so kawo suka akan lamarin auran seda tabi ta kanainaye musamman da Khalifa ya shigo shima ya mara mata baya seda suka san yanda suka ja ra'ayin Jamila da Aminan suka Aminta da zancen auran dukda daman su bawai basa so yayin bane, Aa Jidalin Umaimah suke tunani da kuma tausayin ita wadda akace yana so ze aura din suna ganin tayi qanqanta a hadata kishi da Umaimah. Hajiya da tunda suka fara bata ce musu komai ba tayi ajiyar numfashi tace
"Yanzu meye matsayarku akan maganar nan? Nidai har ga zuciyata bawai bana son auran nan ba Aa tunanin abinda zeje ya dawo nakeyi, bana son tashin hankali musamman a matsayin da yarinyar nan take ciki gata da taohon ciki kuma daman tun samuwar cikin ake ta turka turka daga wannan se wannan bana son abinda ze zo ya taba lafiyarta ko ta abinda yake cikinta amma kuma bazan so na zama me son kai ba shima Babana na tauyeshi, dan haka mecece shawararku ta qarshe akan abinda ya kamata muyi?"
Anty Amina ce tayi magana tace
"Nidai Hajiya ina ganin tunda har Khalil ya furta yana so yayi aure ki barshi yayi ki kuma bishi da Addu'a Allah yasa hakan ya zama Alkhairi ya kuma bashi ikon yin Adalci a tsakaninsu. Amma yanzu yayi haquri ya dakata da maganar auran har zuwa Umaimah ta haihu saboda kowa yasan halinta, bazata dubi halin da take ciki ba tsaf zata illata kanta ta illata abinda ke cikinta a banza saboda haukan kishi dan haka yaci gaba da naman auransa a hankali har zuwa sanda Allah ze tabbatar".
Jalilah da Jamila sunyi Na'am da maganarta amma seda Jalilan ta qara da cewa
"Amma kamar yanda yace iyayenta sunce ya tura idan da gaske yake to ya kamata ayi hakan kinga shine shaidar yana nema manya su shiga cikin magana, daga nan za'a iya jan lokaci ta fara makaranta ma zuwa sannan ta qara wayo da sanin yanda duniya take kafin azo ga batun aure ko ba haka ba?"