Sashe 108
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Isma'il dake kallon qasa ya dago kai ya dube shi, Barr ya daga masa kai cikin tabbatarwa yace
"Kwarai hakan ne kadai zesaka farat daya ka yarda da duk abinda aka ce ta aikata idan daman kasan akan haka ta ginu amma babu yanda za'ayi rana daya azo ace mutum yayi abu dukda ba'a shaidar mutum amma Akwai abinda idan an gaya maka akan wani seka tirza ka ciza ko kuma kaga kwakwkwarar shedar da babu wanda ze qaryata sannan kuwa amma kai ka kafa hujja da hotunan da nida kai munsan basu isa su tabbatar da zargin da akeyi ba.
Kasan girman laifin da ake zargin qanwar ka dashi kuwa? Dani dakai duk musulmaine mun kuma san menene Madigo da hukunci da makomar me aimatashi a duniya da lahira.
Yanzu idan kotun musulinci akaje se an samu Shaidun gani da iso guda uku wanda suka ganta tana aikatawa sannan ne katu zata karbi shaidarsu ta yanke mata hukunci ko kana zaton akwai alqalin da ze saurari wadannan shirman hotunan da ake yawo dasu ana mata qazafi akan su.
Na tabbatar a cikin wayarka yanzu idanan duba se an samu wadanda suka fisu muni idan ba'ayi wasa ba. Nidakai mun sani ba wani abu bane a gurin yammatan yanzu daukar hotuna su bayyanar da sassan jikinsu su turawa samari kaima na tabbatar ba zaka rasa wadda take tura maka ba Nida kai munsan komai babu abinda zaka boye mun idan kuma qarya nakeyi ka kawo wayarka na kawo tawa a gani idan baza'a samu ba".
Yanda kasan qasa ta bude Isma'il ya shiga haka yaji, se yake ganin kamar Barr yasan abinda yake cikin wayar tasa ne dan gaskiya ya fada Yammatan da suke tura masa da hotunan da videos dinsu na tsiraici bazasu irgu ba wasu ma bashi yake tambayarsu ba. Wata ma daga sama baka san wacece ba zata kawo maka tallan kanta kuma da yawa idan ka gansu seka rantse bazasu aikata hakan ba shi yasa yake kasa musawa idan Aka ce Hadizan ta aikata abu tunda yaga wadanda suka fita fuskar Salahai ma suna aikatawa.
"Kayi shiru ko ba haka bane?" Barr ya katse masa tunani seya daga kai alamar haka ne ba tareda yayi magana ba.
"Toh ka gani ba, dukda bani da wata doguwar Mu'amala da ita banyi mata sani na sosai ba amma kai tsaye ina ganin abin nace qarya ne. Akwai wanda idan an fadi abu akansa koda ba gaskiya bane kai tsaye za'a gasgata shi amma akwai kuma wanda se kayi dagaske zaka yarda yayi abu koda kuwa a gabanka ya aikata se kaji shakkun anya kuwa shidinne.
Kuma irin wannan abin ba wai yanzu aka fara shi ba haka kawai mutane zasu samu hoto suyi ta yadawa da sharri kala kala qarshe idan zaka kamasu basu san ma mutumin dake jikin hoton ba ba kuma a san daga inda labarin ya faro ba dalilin da ya saka muke so mu daqile irin abubuwan nan kenan kuma zamu zurfafa bincike, duk wani wanda yake da saka hannu a ciki zamu gano shi sannan mu miqasu gaban shari'a tayi musu hukuncin daya dace dasu dan haka nanemeka, ina so kayi tunani ko akwai wani da kuke zargi da ze iya aikata mata hakan dukda na fada maka mun samu bayanan wadda ta wallafa abin a Facebook, amma bazamu dogara da ita kadai ba dan zata yuwu itama ta samo ne tayi karambanin dorawa a nan din".
"Toh nidai a iya hasashena bazan iya cewa ga wani abokin fada da Hadiza take dashi ba da har ze iya yi mata wannan abin, hasalima ita ko qawaye bata dasu qawarta kwaya daya ce Khausar kuma itace wadda take fada mana daman duk irin rashin jin da takeyi a boye tunda ita koda yaushe suna tare a gida ko a gurin aiki kuma ko yanzun kafin na yarda da maganar seda na titsiyeta ta gaya mun gaskiya kuma ta tabbatar mun da haka din ne abinda Hadizan take aikatawa kenan" Isma'il ya fada a sanyaye dan gaba daya maganganun Barr sun sake dulmiya masa tunani sun kuma fara maido dashi kan hanyar daya kaucewa. Allah ya sani ba wai ya yarda da cewar tanayin bane sedan bashida hujjar qaryata hakan.
Maganar Barr tace ta sakashi dagowa da sauri ya kalleshi jin yana cewa
"Wannan ce Khausar din da kake magana ko" ya fada yana miqa masa screen din wayarsa daya kunna Video seya karba bakinsa yaqi rufuwa saboda tsabar mamakin abinda yake gani Khausar ce zaune a tsakiyar qartin maza sun kai biyar ta kwanta jikin daya daga ciki hannunta riqe da dogon pipe na shisha tana zuqa. Shigar dake jikinta tayi muninda kai tsaye ze iya cewa ba ita bace amma hasken gurin daya haska fuskarta tarwai ga sunanta da wanda yakeyin video ya ambata akan ta dago fuskarta yayi mata video ta kuwa dago tana wani shegen fari da ido besan lokacin daya fara maimaita Innalillahi a fili ba.
Barr ya zare wayar daga hannunsa yana cewa
"Se kayiwa kanka Alqalanci ka kuma dora maganganun da take gaya muku akan sikeli, abu na qarshe da zan gaya maka kaje ka taushi yar uwarka Ubangiji kadai yasan halin da take ciki kuma yanzu ne take da buqatar kulawarku da qarfafa guiwa, koda ace abinda akw yawo dashi akanta gaskiya ne a halin yanzu tana cike da nadamar abinda ta aikata kuma tana buqatar wanda ze tallafa mata yajata a jiki ya taimaketa ta bar abinda takeyi ballantana ita da akayiwa Sharri".
Isma'il yayi shiru ya kasa cewa komai gaba daya kunyar kansa ce ta dabaibayeshu, ya akayi ya kasayiwa Tilon yar uwarsa uzuri koda na minti daya yaji ta bakinta? Tunda ake kawo musu magana akanta daga shi har Mama babu wanda ya taba bata damar da zata kare kanta sun kasa yarda da ita duk da daga shi har Maman idanza'a tsire su basu da shaidar da zata tabbatar da gaskiyar abinda suke zarginta dashi ko ake fada akanta suna yarda kawai zallar Son zuciyarsu ne yasa suke gasgata maganar wasu can daban sun kasa yarda da tarbiyyar dasuka bata, Allah sarki Alhajinsu ya tabbatar yau da yana raye baze taba juyawa Hadiza baya ba komai girman abinda ta aikata kuwa dan kamar yanda yake gaya musu a koda yaushe ba'a gyara laifi da laifi. Idan mutum ya aikata kuskure ana gyara masa ne ta hanyar janyo shi jiki a kyautata masa har shi dakansa ya fahimci kuskurensa kuma ya gyara amma sam su basu taba kwatanta hakan ba.
"Karka ji haushin kanka saboda ko wanne dan Adam a rayuwa da yanda yake iya tunkarar damuwa. Wani yakan saka nutsuwa da tunani gurin warware damuwarsa wani kuma yanayi mata gaggawa, dan haka yanzu ka tashi kaje gida ka huta zuwa gobe in Allah ya kaimu, duk wani ci gaba da muka samu akan binciken zan sanar maka. Sannan ka lallabi yar uwarka ina sake jaddada maka ka bata qwarin guiwa akan duk abinda ze fuskantota a gaba, ta qaddara cewar wannan abin da ya faru jarabawa ce daga ubangiki idan tayi haquri ta cinyeta se ta zame mata sikar takawani matakine na Nasara da batayi tsammani ba" Barr ya sake fada kafin suka miqe gaba daya. Har bakin Get ya rakashi yana sake jaddada masa daya je ya taushi hadiza ya kuma bata haquri da kwarin guiwa.
A hanya tunani Isma'il ya ringayi har seda kwallar tausayin Hadizan ta shiga zubo masa. Sam wani abu me kama da tausayinta be zo masa ba se a yanzu, a sanda abin ya faru wani mugun baqin ciki da tsanarta yaji sunyi masa dirar mikiya saboda yasan ta rusa masa shirin daya kwashe tsahon shekaru yanayinsa seda Mafarkinsa yazo dabda cika ya samu Tikitin tsayawa takarar Dan Majalisar Jaha wanda dakyar da roqon Allah damar ta samu se gashi wannan abun ya bullo wanda take Yan Adawa suka samu nayi suka fara sukar sa tun kafin bayyanuwar takarar tasa kowa yasanda ita. Zafin wannan ne ya sake ingiza shi yayi mata dukan da beqi ace ta mutu ba ko ya ji sauqin wani kaso na baqin cikin data qunsa musu.
Gidan Mama ya wuce, ya tarar da Bilkisu ta tafi saboda dare ta baro yara su kadai se Hajiya Zuwaira da Wata Asabe itama maqociyarsu ce Hajiya Zuwairan ta kirata akan tazo ta taya Maman kwana kafin gobe su Mama Innani su iso tuni ma har tasha magungunanta ma bacci ya dauketa se su biyun suna zaune suna ta mayar da yanda akayi.
Be zauna ba yayi musu sallama dan yana buqatar yaje gida ya harhada tunanin da suka tarar masa akai ko ze samu amsar abinda yake gabansa. Harya fita ya dawo, daga bakin qofa ya tsaya kamar baya son magana yana kallon Hajiya Zuwaira yace
"Momy wane Asibiti aka kwantar da Hadizan ne?"
Karkata kai Hajiya Zuwaira tayi tana kallonsa tace "Se yanzu zaka tambayi halin da yar uwarka take ciki Sama'ila? Ai wallahi banyi tsammanin haka daga gareka ba ko kusa ko alama kuwa. Idan hankali ya gushe ai nutsuwa ce take nemoshi fisabilillahi idan baka zama bango majinginarta ba wa kake so ta dafa tayi kuka a rayuwarta? Ka dagawa Mahaifiyarku hankali a maimakon ka kwantar mata sannan ka kama baiwar Allah da duka idan da abin yazo da Ajali ai yanzu ai wani zancen ake ba wannan ba shikenan saboda kaji abu da Allah kadai yasan Al'amari seka nemi Ran baiwar Allah nan duk da mukaje ceto babu wanda be fita da tabon ka ba akan meye eye? To wallahi kayiwa kanka fada kuma ka nemi yafiyarta, mugun bakin da ka saka uwarku ta ringayi mata idan baka saka ta gogesu qaiqayine ze koma kan masheqiya danbata da haqqinku daga kai Har Karimatun".
"Kwarai hakan ne kadai zesaka farat daya ka yarda da duk abinda aka ce ta aikata idan daman kasan akan haka ta ginu amma babu yanda za'ayi rana daya azo ace mutum yayi abu dukda ba'a shaidar mutum amma Akwai abinda idan an gaya maka akan wani seka tirza ka ciza ko kuma kaga kwakwkwarar shedar da babu wanda ze qaryata sannan kuwa amma kai ka kafa hujja da hotunan da nida kai munsan basu isa su tabbatar da zargin da akeyi ba.
Kasan girman laifin da ake zargin qanwar ka dashi kuwa? Dani dakai duk musulmaine mun kuma san menene Madigo da hukunci da makomar me aimatashi a duniya da lahira.
Yanzu idan kotun musulinci akaje se an samu Shaidun gani da iso guda uku wanda suka ganta tana aikatawa sannan ne katu zata karbi shaidarsu ta yanke mata hukunci ko kana zaton akwai alqalin da ze saurari wadannan shirman hotunan da ake yawo dasu ana mata qazafi akan su.
Na tabbatar a cikin wayarka yanzu idanan duba se an samu wadanda suka fisu muni idan ba'ayi wasa ba. Nidakai mun sani ba wani abu bane a gurin yammatan yanzu daukar hotuna su bayyanar da sassan jikinsu su turawa samari kaima na tabbatar ba zaka rasa wadda take tura maka ba Nida kai munsan komai babu abinda zaka boye mun idan kuma qarya nakeyi ka kawo wayarka na kawo tawa a gani idan baza'a samu ba".
Yanda kasan qasa ta bude Isma'il ya shiga haka yaji, se yake ganin kamar Barr yasan abinda yake cikin wayar tasa ne dan gaskiya ya fada Yammatan da suke tura masa da hotunan da videos dinsu na tsiraici bazasu irgu ba wasu ma bashi yake tambayarsu ba. Wata ma daga sama baka san wacece ba zata kawo maka tallan kanta kuma da yawa idan ka gansu seka rantse bazasu aikata hakan ba shi yasa yake kasa musawa idan Aka ce Hadizan ta aikata abu tunda yaga wadanda suka fita fuskar Salahai ma suna aikatawa.
"Kayi shiru ko ba haka bane?" Barr ya katse masa tunani seya daga kai alamar haka ne ba tareda yayi magana ba.
"Toh ka gani ba, dukda bani da wata doguwar Mu'amala da ita banyi mata sani na sosai ba amma kai tsaye ina ganin abin nace qarya ne. Akwai wanda idan an fadi abu akansa koda ba gaskiya bane kai tsaye za'a gasgata shi amma akwai kuma wanda se kayi dagaske zaka yarda yayi abu koda kuwa a gabanka ya aikata se kaji shakkun anya kuwa shidinne.
Kuma irin wannan abin ba wai yanzu aka fara shi ba haka kawai mutane zasu samu hoto suyi ta yadawa da sharri kala kala qarshe idan zaka kamasu basu san ma mutumin dake jikin hoton ba ba kuma a san daga inda labarin ya faro ba dalilin da ya saka muke so mu daqile irin abubuwan nan kenan kuma zamu zurfafa bincike, duk wani wanda yake da saka hannu a ciki zamu gano shi sannan mu miqasu gaban shari'a tayi musu hukuncin daya dace dasu dan haka nanemeka, ina so kayi tunani ko akwai wani da kuke zargi da ze iya aikata mata hakan dukda na fada maka mun samu bayanan wadda ta wallafa abin a Facebook, amma bazamu dogara da ita kadai ba dan zata yuwu itama ta samo ne tayi karambanin dorawa a nan din".
"Toh nidai a iya hasashena bazan iya cewa ga wani abokin fada da Hadiza take dashi ba da har ze iya yi mata wannan abin, hasalima ita ko qawaye bata dasu qawarta kwaya daya ce Khausar kuma itace wadda take fada mana daman duk irin rashin jin da takeyi a boye tunda ita koda yaushe suna tare a gida ko a gurin aiki kuma ko yanzun kafin na yarda da maganar seda na titsiyeta ta gaya mun gaskiya kuma ta tabbatar mun da haka din ne abinda Hadizan take aikatawa kenan" Isma'il ya fada a sanyaye dan gaba daya maganganun Barr sun sake dulmiya masa tunani sun kuma fara maido dashi kan hanyar daya kaucewa. Allah ya sani ba wai ya yarda da cewar tanayin bane sedan bashida hujjar qaryata hakan.
Maganar Barr tace ta sakashi dagowa da sauri ya kalleshi jin yana cewa
"Wannan ce Khausar din da kake magana ko" ya fada yana miqa masa screen din wayarsa daya kunna Video seya karba bakinsa yaqi rufuwa saboda tsabar mamakin abinda yake gani Khausar ce zaune a tsakiyar qartin maza sun kai biyar ta kwanta jikin daya daga ciki hannunta riqe da dogon pipe na shisha tana zuqa. Shigar dake jikinta tayi muninda kai tsaye ze iya cewa ba ita bace amma hasken gurin daya haska fuskarta tarwai ga sunanta da wanda yakeyin video ya ambata akan ta dago fuskarta yayi mata video ta kuwa dago tana wani shegen fari da ido besan lokacin daya fara maimaita Innalillahi a fili ba.
Barr ya zare wayar daga hannunsa yana cewa
"Se kayiwa kanka Alqalanci ka kuma dora maganganun da take gaya muku akan sikeli, abu na qarshe da zan gaya maka kaje ka taushi yar uwarka Ubangiji kadai yasan halin da take ciki kuma yanzu ne take da buqatar kulawarku da qarfafa guiwa, koda ace abinda akw yawo dashi akanta gaskiya ne a halin yanzu tana cike da nadamar abinda ta aikata kuma tana buqatar wanda ze tallafa mata yajata a jiki ya taimaketa ta bar abinda takeyi ballantana ita da akayiwa Sharri".
Isma'il yayi shiru ya kasa cewa komai gaba daya kunyar kansa ce ta dabaibayeshu, ya akayi ya kasayiwa Tilon yar uwarsa uzuri koda na minti daya yaji ta bakinta? Tunda ake kawo musu magana akanta daga shi har Mama babu wanda ya taba bata damar da zata kare kanta sun kasa yarda da ita duk da daga shi har Maman idanza'a tsire su basu da shaidar da zata tabbatar da gaskiyar abinda suke zarginta dashi ko ake fada akanta suna yarda kawai zallar Son zuciyarsu ne yasa suke gasgata maganar wasu can daban sun kasa yarda da tarbiyyar dasuka bata, Allah sarki Alhajinsu ya tabbatar yau da yana raye baze taba juyawa Hadiza baya ba komai girman abinda ta aikata kuwa dan kamar yanda yake gaya musu a koda yaushe ba'a gyara laifi da laifi. Idan mutum ya aikata kuskure ana gyara masa ne ta hanyar janyo shi jiki a kyautata masa har shi dakansa ya fahimci kuskurensa kuma ya gyara amma sam su basu taba kwatanta hakan ba.
"Karka ji haushin kanka saboda ko wanne dan Adam a rayuwa da yanda yake iya tunkarar damuwa. Wani yakan saka nutsuwa da tunani gurin warware damuwarsa wani kuma yanayi mata gaggawa, dan haka yanzu ka tashi kaje gida ka huta zuwa gobe in Allah ya kaimu, duk wani ci gaba da muka samu akan binciken zan sanar maka. Sannan ka lallabi yar uwarka ina sake jaddada maka ka bata qwarin guiwa akan duk abinda ze fuskantota a gaba, ta qaddara cewar wannan abin da ya faru jarabawa ce daga ubangiki idan tayi haquri ta cinyeta se ta zame mata sikar takawani matakine na Nasara da batayi tsammani ba" Barr ya sake fada kafin suka miqe gaba daya. Har bakin Get ya rakashi yana sake jaddada masa daya je ya taushi hadiza ya kuma bata haquri da kwarin guiwa.
A hanya tunani Isma'il ya ringayi har seda kwallar tausayin Hadizan ta shiga zubo masa. Sam wani abu me kama da tausayinta be zo masa ba se a yanzu, a sanda abin ya faru wani mugun baqin ciki da tsanarta yaji sunyi masa dirar mikiya saboda yasan ta rusa masa shirin daya kwashe tsahon shekaru yanayinsa seda Mafarkinsa yazo dabda cika ya samu Tikitin tsayawa takarar Dan Majalisar Jaha wanda dakyar da roqon Allah damar ta samu se gashi wannan abun ya bullo wanda take Yan Adawa suka samu nayi suka fara sukar sa tun kafin bayyanuwar takarar tasa kowa yasanda ita. Zafin wannan ne ya sake ingiza shi yayi mata dukan da beqi ace ta mutu ba ko ya ji sauqin wani kaso na baqin cikin data qunsa musu.
Gidan Mama ya wuce, ya tarar da Bilkisu ta tafi saboda dare ta baro yara su kadai se Hajiya Zuwaira da Wata Asabe itama maqociyarsu ce Hajiya Zuwairan ta kirata akan tazo ta taya Maman kwana kafin gobe su Mama Innani su iso tuni ma har tasha magungunanta ma bacci ya dauketa se su biyun suna zaune suna ta mayar da yanda akayi.
Be zauna ba yayi musu sallama dan yana buqatar yaje gida ya harhada tunanin da suka tarar masa akai ko ze samu amsar abinda yake gabansa. Harya fita ya dawo, daga bakin qofa ya tsaya kamar baya son magana yana kallon Hajiya Zuwaira yace
"Momy wane Asibiti aka kwantar da Hadizan ne?"
Karkata kai Hajiya Zuwaira tayi tana kallonsa tace "Se yanzu zaka tambayi halin da yar uwarka take ciki Sama'ila? Ai wallahi banyi tsammanin haka daga gareka ba ko kusa ko alama kuwa. Idan hankali ya gushe ai nutsuwa ce take nemoshi fisabilillahi idan baka zama bango majinginarta ba wa kake so ta dafa tayi kuka a rayuwarta? Ka dagawa Mahaifiyarku hankali a maimakon ka kwantar mata sannan ka kama baiwar Allah da duka idan da abin yazo da Ajali ai yanzu ai wani zancen ake ba wannan ba shikenan saboda kaji abu da Allah kadai yasan Al'amari seka nemi Ran baiwar Allah nan duk da mukaje ceto babu wanda be fita da tabon ka ba akan meye eye? To wallahi kayiwa kanka fada kuma ka nemi yafiyarta, mugun bakin da ka saka uwarku ta ringayi mata idan baka saka ta gogesu qaiqayine ze koma kan masheqiya danbata da haqqinku daga kai Har Karimatun".