Sashe 230
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Momy" taji an kira ta se tayi saurin saka hannu ta share hawayen fuskarta ta juya Bibi na tsaye a bakin qofar ta tafi da gudu ta fada jikin Umaimah ga mamakinta se kawai yarinyar ta fashe da kuka tana cewa
"Momy dama kina nan gidan kullum na tambayi Dady ina kike se yace mun kinyi tafiya zaki dawo".
Rungume yarinyar tayi a jikinta wani irin kewarsu na sake shigarta a hankali tana shafa kanta tace
"To kukan menene kuma ba gani yanzu kin ganni ba" se yarinyar ta dago tana shafa fuskar Umaiman tace
"Momy kin rame baki da lafiya?" Se tayi saurin janye fuskarta saboda wani kuka daya sake taho mata dai dai nan mu'ayyad da Iman suka shiga shima da gudu ya fada jikinta yana cewa
"I miss you Momy ina kika tafi kika barmu kullum se Dady yace mana kinyi tafiya kinqi ki dawo?"
Ta kalli Iman data tsaya a bakin qofa wata sahihiyar qaunarta da bata tsaya ta tantance ba sanda ta haifeta ta shiga zuciyarta, seta miqa mata hannu alamar itana ta taho yar gasken ta maqe kafada ba zataje ba, Mu'ayyad ya tashi ya janyota yana cewa
"Kizo gurin Momy" kai tsaye ta fizge hannunta cikin muryarta da bata gama iya magana ba tace
"Ni ba Momy na bace, Mamah na tana gida da Aryaan".
Yanda kasan dukan guduma haka taji maganar har ranta, ta zubawa yarinyar ido yanda ta dauke kai ta cuna baki a dole ba zataje gurinta ba zuciyarta ta qara karaya, babu tantama haqqin banzatar da ita da tayi ne ya fara bibiyarta Mamanta da tace tana gida ta tabbata Matar Khalil take nufi tunda ita ta bude ido ta gani a matsayin mahaifiyarta batayi laifi dan tace ita ba Momynta bace.
Wunin ranar sir da yaranta tayi shi wani irin dadi mara misaltuwa ta ringaji suka ringa bata labarai na Hajiya Dadynsu, Mamah da Aryaan da ta kas gane wanene shi kp wata daga cikin su Jalilah ta sake haihuwa ne? A bakinsu taji cewar Habiba tayi aure harta haihu tun tuni sunanr Yarinyar Hajar. Har Magriba suna gidan suna kuma maqale da Momynsu dan da Abba ya dawo ma sukaje gurinsa basu dade ba suka gudo gurinta, Mu'ayyad da Bibi na lafe a jikinta Iman ce take ja baya da alama dan yan uwanta na gurin Umaiman nema yasa ta zauna da bazata tsaya ba su kuwa kewarta ce tasa suka kasa barin inda take dukda motsi kadan se sun tambayeta bata da lafiya ta rame se tace musu eh kawai se kuma suka kafa tambayar yaushe zata koma gidansu haka kawai taji bakinta ya furta
"Ku tambayi Dady, duk sanda yace na dawo zan dawo".
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 79
Seda akayi sallar Magriba akazo daukarsu dan daman sun fada musu ba kwana zasuyi ba. Wata Farar mace kyakykyawa ajin farko tayi sallama riqe da yaro kalarta Umaiman na tsaye bakin qofar shigowa tana jiran yaron data aika ya siyowa Mu'ayyad Awara wai zeci matar ta shigo qamshinta me sanyi da Aji ya kai mata ziyara ta shaqa tana ware ido akanta saboda akwai hasken nefa a gurin ta ga fuskarta tar seta zuba mata ido tana so ta gano inda ta santa. Humaira ta fadada murmushin ta cikin ladabin data ke gaida duk wanda ya girmeta ta dan rankwafawa Umaiman tana cewa
"Ina wuni"
"Lafiya lau" ta amsa ba tareda ta gano inda ta santa din ba seta raya qila baquwar Anty ce dan da ta bangarensu ce zata santa. Qara gyara tsayuwa Humaira tayi tana kallon Umaiman tace
"Mama fa tana ciki?" Seta nuna mata qofar Maman kawai ba tareda ta sake cewa komai ba dan haka siddan taji tsanar matar ta dirar mata dukda bata da tabbacin wani abu ya taba hada, murmushi ta sakeyi mata kafin ta shige cikin gidan Umaimah ta bita da wani siririn tsaki daidai nan yaron data aika ya dawo ta karba ta wuce dakinta inda yaran suke jiranta.
A plate ta juye musu sun fara ci kenan ta Mama ta kwala mata kira seta miqe bayan ta mayar da Hijabinta ta fita. Tare ta tarar dasu da matar dazun tana zaune a qasa yaronta na kan cinyar Mama se wani sunne kai takeyi Umaimah ta tabe baki qila cikin surukanta ne yaran yan uwanta tunda anyi bukunkuna da yawa a shekarun duk bata je ba tana zaune kamar Prisoner Mama ta nuna mata Humaira tana cewa
"Mamansu ce tazo daukarsu" set kalli Maman kafin tace
"Maman suwa?"
"Su Malika, su fito su tafi kar su bata mata lokaci dare yanayi" Maman ta bata amsa tana harararta Umaimah kuwa daskarewa tayi a inda take kamar wadda ta samu cutar mantau kusan minti biyar kafin ta dawo hayyacinta sanadin tsawar da Maman tayi mata akan ta wuce ta turo yaran ta tsaya musu aka kamar wata kurma seta juya jiki a matuqar sabule tana jefa qafafunta kawai badan tasan ina ta nufa ba, a qofar dakin ta kifa kanta ta fashe da kukan data kasa riqewa wanda ta rasa ma na menene, ta tabbata dai waccen Matar ana nufinitace Matar da Khalil ya aura wadda tayi sanadin barinta dakinta ta rabata da yaranta har Iman take fadin ita ba Mamanta bace to idan haka ne shi kuma yaron hannu ta na waye dandai tafi kowa sanin cewar Khalil ya rasa lafiyar da ze iya yiwa Mace ciki ta haihu?
Kuka takr haiqan, Mu'ayyad daya fito da plate ya ganta yayi saurin ajiyewa ya matsa kusa da ita fusakarsa ta nuna damuwa yace
"Momy me akayi miki kike kuka?" Se a sannan ta tuna a inda take tayi saurin daga kanta ta shiga share hawayen amma sun gagara tsayawa se ta juya tana tafiya tace masa
"Anzo daukarku kira qannenka ku tafi" tayi can hanyar tsofaffin dakunan su na baya da se ana wani sha'ani ake amfani dasu. Guri ta samu ta cigada da rera kukanta da takeyi tundaga can qasan zuciyarta. Kishin matar da ke amsa sunan ta Khalil a yanzu ya cikata, yanzu duk wata soyayya da tarairaya da yakeyi mata ita take samunta kenan, Khalil ya iya mallakawa wata mace bayanta kansa abinda bata taba tsammatar ze iya faruwa ba. A zatonta irin tarin qaunar da Khalil yake mata ko a Aljanna da da hali ze iya haqura da Kyautar Hurul ayni ya zauna da ita kadai suci gaba da cin soyayyarsu amma se gashi tun a duniya tana raye ya manta da ita ya juya mata baya ya sadaukarwa da wata kansa ba tareda ya dubi halin da take ciki ba wanda shine sila shiya jefata shiya janyo ta aikata koma menene Soyayyar sa ce sila.
Tana nan zaune tana kukan suka fito Mama ta rakosu har bakin qofa tana musu Addu'a ga qatuwar leda a hannun Mu'ayyad da bata san ko menene a ciki ba haka suka fice daga gidan tana jin Bibi na cewa
"Ina momy? Bamuyi sallama da ita ba fa" tayi maganar cikin son fasa musu kukan rigima ta jiyo tashin muryar Humairan dukda bata ji abinda take fada ba amma tasan lallashin tayi suka tafi seta sske kecewa da wani kukan dana sani da nadamar ayyukanta suka ringa taso mata, me yasa ta biyewa zuciya ta gazayin aiki da kwakwalwarta? Me yasa bata saurari yanuwa da abokan arziqi da suka ringa qoqarin nusar da ita ha ya ta kwarai ba a lokacin bata yi tunanin makomarta ba ta biyewa hudubar shaidar da son zuciyarta kawai gashi Khalil din da tayi danshi ya barta harya samu lafiyarsa yaci gaba da mu'amalantar watanta tubda ga shaida ta gani da idonta wanda kadai ya isa ya tabbatar mata da cewar yayi gaba a rayuwarsa ba kuma zai waiwayeta ba.
Bata san lokacin data bata a gurin tana kuka da dana sani mara amfani ba kafin daga qarshe ta haqura ta tashi daga gurin tana jin kanta tamkar ya tsage saboda ciwo. Ragowar awarar da suka bari taci ta kwanta kawai amma bacci ya qauracewa idonta, duk inta motsa Khalil take gani a idonta da Humairan yana gwada mata kalar soyayyarsa me tsayawa a zuciya ta dora pillow akanta ta fasa qara kamar zata tsaga dakin, a fusace Mama ta shiga ta saiti bayanta ta watsa mata Carbin dake hannunta Umaiman ta zabura ta sake zuba mata shi yanda ta bude baki ta fara kuka me hade da ihu ya sake tunzura Maman ta ringa caula mata carbi ta ko ina seda ya tsinke kafin ta rabu da ita tana haki tace
"Ke dan ubanki baki san ki ambaci Allah ba a duk sanda kike cikin tsanani se ihu da kwaroroto kamar diyar Arna? Ihun ne ze miki maganin damuwarki ko me, se yaushe zakiyi hankali Umaimah ki maida Al'amuranki zuwa ga Allah sannan ki ringa neman agajinsa akan duk abinda ya dameki? Kullum cikin yi miki tunatarwa nake akan duk a abinda ya sameki ki nemi taimakon Allah ki lazumci karanta Hasbunallahu wani'imal wakeel da sannu Allah ze kawo miki rangwame da salama cikin lamuranki, sannan ki riqe 'La'ilaha illah anta subhanaka inni kuntu minazzalimin' duk tsanani da yardar Allah zaki samu mafita amma inase ihu da kururuwa kadai kika sani babu Istigfari babu hailala babu salatin Annabi babu karatun Alqur'ani se Kuka da tagumi kika qulla aure dasu tayaya zakiga daidai a sha'ani ki Umaimah? Tun lokaci be qure miki ba ki gyara badan wani ba sedan ke a karan kanki kodan kiji dadin sauran rayuwar data rage miki Umaimah ki kama Allah" daga haka ta juya ta bar mata dakin Umaimah da tayi luqus jikinta gaba daya radadin dukan carbin data sha yakeyi amma maganganun Maman tabbas sun shigeta matuqa.
"Momy dama kina nan gidan kullum na tambayi Dady ina kike se yace mun kinyi tafiya zaki dawo".
Rungume yarinyar tayi a jikinta wani irin kewarsu na sake shigarta a hankali tana shafa kanta tace
"To kukan menene kuma ba gani yanzu kin ganni ba" se yarinyar ta dago tana shafa fuskar Umaiman tace
"Momy kin rame baki da lafiya?" Se tayi saurin janye fuskarta saboda wani kuka daya sake taho mata dai dai nan mu'ayyad da Iman suka shiga shima da gudu ya fada jikinta yana cewa
"I miss you Momy ina kika tafi kika barmu kullum se Dady yace mana kinyi tafiya kinqi ki dawo?"
Ta kalli Iman data tsaya a bakin qofa wata sahihiyar qaunarta da bata tsaya ta tantance ba sanda ta haifeta ta shiga zuciyarta, seta miqa mata hannu alamar itana ta taho yar gasken ta maqe kafada ba zataje ba, Mu'ayyad ya tashi ya janyota yana cewa
"Kizo gurin Momy" kai tsaye ta fizge hannunta cikin muryarta da bata gama iya magana ba tace
"Ni ba Momy na bace, Mamah na tana gida da Aryaan".
Yanda kasan dukan guduma haka taji maganar har ranta, ta zubawa yarinyar ido yanda ta dauke kai ta cuna baki a dole ba zataje gurinta ba zuciyarta ta qara karaya, babu tantama haqqin banzatar da ita da tayi ne ya fara bibiyarta Mamanta da tace tana gida ta tabbata Matar Khalil take nufi tunda ita ta bude ido ta gani a matsayin mahaifiyarta batayi laifi dan tace ita ba Momynta bace.
Wunin ranar sir da yaranta tayi shi wani irin dadi mara misaltuwa ta ringaji suka ringa bata labarai na Hajiya Dadynsu, Mamah da Aryaan da ta kas gane wanene shi kp wata daga cikin su Jalilah ta sake haihuwa ne? A bakinsu taji cewar Habiba tayi aure harta haihu tun tuni sunanr Yarinyar Hajar. Har Magriba suna gidan suna kuma maqale da Momynsu dan da Abba ya dawo ma sukaje gurinsa basu dade ba suka gudo gurinta, Mu'ayyad da Bibi na lafe a jikinta Iman ce take ja baya da alama dan yan uwanta na gurin Umaiman nema yasa ta zauna da bazata tsaya ba su kuwa kewarta ce tasa suka kasa barin inda take dukda motsi kadan se sun tambayeta bata da lafiya ta rame se tace musu eh kawai se kuma suka kafa tambayar yaushe zata koma gidansu haka kawai taji bakinta ya furta
"Ku tambayi Dady, duk sanda yace na dawo zan dawo".
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 79
Seda akayi sallar Magriba akazo daukarsu dan daman sun fada musu ba kwana zasuyi ba. Wata Farar mace kyakykyawa ajin farko tayi sallama riqe da yaro kalarta Umaiman na tsaye bakin qofar shigowa tana jiran yaron data aika ya siyowa Mu'ayyad Awara wai zeci matar ta shigo qamshinta me sanyi da Aji ya kai mata ziyara ta shaqa tana ware ido akanta saboda akwai hasken nefa a gurin ta ga fuskarta tar seta zuba mata ido tana so ta gano inda ta santa. Humaira ta fadada murmushin ta cikin ladabin data ke gaida duk wanda ya girmeta ta dan rankwafawa Umaiman tana cewa
"Ina wuni"
"Lafiya lau" ta amsa ba tareda ta gano inda ta santa din ba seta raya qila baquwar Anty ce dan da ta bangarensu ce zata santa. Qara gyara tsayuwa Humaira tayi tana kallon Umaiman tace
"Mama fa tana ciki?" Seta nuna mata qofar Maman kawai ba tareda ta sake cewa komai ba dan haka siddan taji tsanar matar ta dirar mata dukda bata da tabbacin wani abu ya taba hada, murmushi ta sakeyi mata kafin ta shige cikin gidan Umaimah ta bita da wani siririn tsaki daidai nan yaron data aika ya dawo ta karba ta wuce dakinta inda yaran suke jiranta.
A plate ta juye musu sun fara ci kenan ta Mama ta kwala mata kira seta miqe bayan ta mayar da Hijabinta ta fita. Tare ta tarar dasu da matar dazun tana zaune a qasa yaronta na kan cinyar Mama se wani sunne kai takeyi Umaimah ta tabe baki qila cikin surukanta ne yaran yan uwanta tunda anyi bukunkuna da yawa a shekarun duk bata je ba tana zaune kamar Prisoner Mama ta nuna mata Humaira tana cewa
"Mamansu ce tazo daukarsu" set kalli Maman kafin tace
"Maman suwa?"
"Su Malika, su fito su tafi kar su bata mata lokaci dare yanayi" Maman ta bata amsa tana harararta Umaimah kuwa daskarewa tayi a inda take kamar wadda ta samu cutar mantau kusan minti biyar kafin ta dawo hayyacinta sanadin tsawar da Maman tayi mata akan ta wuce ta turo yaran ta tsaya musu aka kamar wata kurma seta juya jiki a matuqar sabule tana jefa qafafunta kawai badan tasan ina ta nufa ba, a qofar dakin ta kifa kanta ta fashe da kukan data kasa riqewa wanda ta rasa ma na menene, ta tabbata dai waccen Matar ana nufinitace Matar da Khalil ya aura wadda tayi sanadin barinta dakinta ta rabata da yaranta har Iman take fadin ita ba Mamanta bace to idan haka ne shi kuma yaron hannu ta na waye dandai tafi kowa sanin cewar Khalil ya rasa lafiyar da ze iya yiwa Mace ciki ta haihu?
Kuka takr haiqan, Mu'ayyad daya fito da plate ya ganta yayi saurin ajiyewa ya matsa kusa da ita fusakarsa ta nuna damuwa yace
"Momy me akayi miki kike kuka?" Se a sannan ta tuna a inda take tayi saurin daga kanta ta shiga share hawayen amma sun gagara tsayawa se ta juya tana tafiya tace masa
"Anzo daukarku kira qannenka ku tafi" tayi can hanyar tsofaffin dakunan su na baya da se ana wani sha'ani ake amfani dasu. Guri ta samu ta cigada da rera kukanta da takeyi tundaga can qasan zuciyarta. Kishin matar da ke amsa sunan ta Khalil a yanzu ya cikata, yanzu duk wata soyayya da tarairaya da yakeyi mata ita take samunta kenan, Khalil ya iya mallakawa wata mace bayanta kansa abinda bata taba tsammatar ze iya faruwa ba. A zatonta irin tarin qaunar da Khalil yake mata ko a Aljanna da da hali ze iya haqura da Kyautar Hurul ayni ya zauna da ita kadai suci gaba da cin soyayyarsu amma se gashi tun a duniya tana raye ya manta da ita ya juya mata baya ya sadaukarwa da wata kansa ba tareda ya dubi halin da take ciki ba wanda shine sila shiya jefata shiya janyo ta aikata koma menene Soyayyar sa ce sila.
Tana nan zaune tana kukan suka fito Mama ta rakosu har bakin qofa tana musu Addu'a ga qatuwar leda a hannun Mu'ayyad da bata san ko menene a ciki ba haka suka fice daga gidan tana jin Bibi na cewa
"Ina momy? Bamuyi sallama da ita ba fa" tayi maganar cikin son fasa musu kukan rigima ta jiyo tashin muryar Humairan dukda bata ji abinda take fada ba amma tasan lallashin tayi suka tafi seta sske kecewa da wani kukan dana sani da nadamar ayyukanta suka ringa taso mata, me yasa ta biyewa zuciya ta gazayin aiki da kwakwalwarta? Me yasa bata saurari yanuwa da abokan arziqi da suka ringa qoqarin nusar da ita ha ya ta kwarai ba a lokacin bata yi tunanin makomarta ba ta biyewa hudubar shaidar da son zuciyarta kawai gashi Khalil din da tayi danshi ya barta harya samu lafiyarsa yaci gaba da mu'amalantar watanta tubda ga shaida ta gani da idonta wanda kadai ya isa ya tabbatar mata da cewar yayi gaba a rayuwarsa ba kuma zai waiwayeta ba.
Bata san lokacin data bata a gurin tana kuka da dana sani mara amfani ba kafin daga qarshe ta haqura ta tashi daga gurin tana jin kanta tamkar ya tsage saboda ciwo. Ragowar awarar da suka bari taci ta kwanta kawai amma bacci ya qauracewa idonta, duk inta motsa Khalil take gani a idonta da Humairan yana gwada mata kalar soyayyarsa me tsayawa a zuciya ta dora pillow akanta ta fasa qara kamar zata tsaga dakin, a fusace Mama ta shiga ta saiti bayanta ta watsa mata Carbin dake hannunta Umaiman ta zabura ta sake zuba mata shi yanda ta bude baki ta fara kuka me hade da ihu ya sake tunzura Maman ta ringa caula mata carbi ta ko ina seda ya tsinke kafin ta rabu da ita tana haki tace
"Ke dan ubanki baki san ki ambaci Allah ba a duk sanda kike cikin tsanani se ihu da kwaroroto kamar diyar Arna? Ihun ne ze miki maganin damuwarki ko me, se yaushe zakiyi hankali Umaimah ki maida Al'amuranki zuwa ga Allah sannan ki ringa neman agajinsa akan duk abinda ya dameki? Kullum cikin yi miki tunatarwa nake akan duk a abinda ya sameki ki nemi taimakon Allah ki lazumci karanta Hasbunallahu wani'imal wakeel da sannu Allah ze kawo miki rangwame da salama cikin lamuranki, sannan ki riqe 'La'ilaha illah anta subhanaka inni kuntu minazzalimin' duk tsanani da yardar Allah zaki samu mafita amma inase ihu da kururuwa kadai kika sani babu Istigfari babu hailala babu salatin Annabi babu karatun Alqur'ani se Kuka da tagumi kika qulla aure dasu tayaya zakiga daidai a sha'ani ki Umaimah? Tun lokaci be qure miki ba ki gyara badan wani ba sedan ke a karan kanki kodan kiji dadin sauran rayuwar data rage miki Umaimah ki kama Allah" daga haka ta juya ta bar mata dakin Umaimah da tayi luqus jikinta gaba daya radadin dukan carbin data sha yakeyi amma maganganun Maman tabbas sun shigeta matuqa.