Sashe 245
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kina nufin ba zaki iya ba kenan?" Umaimah ta fada cikin kuka domin Maman Asad dince kadai dogaronta da zata iya nema mata gafara a gurin Khalil da Hajiya a madadinta, se Maman Asad ta kama hannunta tana cewa
"Ba haka nake nufi ba Umaimah. Kece mafi cancanta da ki nemi yafiyarsu abinda nale nufi kici gaba da addu'a har zuwa sanda komai ze daidaita ki samu damar neman yafiyarsu da kanki" seta sassauta kukan tana kallon Hajiyayyen tace
"Kina ganin zasu yafe mun?"
"Meze hana, a rayuwata ban taba ganin mutane masu karamci kamarsu ba Umaimah na tabbatar ko a yanzu sun yi miki afuwa tunda har suka bar Yaranki suke zuwa gurinki hakan yana nuna fushin da sukeyi dake ya ragu, kici gaba da addu'a yanadaga cikin tasirinta" Maman Asad ta fada kafinta miqe tana cewa
"Bari naje saqo na kawowa Mama daman se ranar Juma'a in Allah ya kaimu duk zamu zo Naziyya ma tana tafe ranar Alhamis kuma idan tazo karki kuskura ta sake barin garin nan baku warware gabar dake tsakaninku ba"
"Toh ai ba laifina bane, cewa tayi bata yafe ba idan na sake yi mata magana babu ita babu ni ni kuma naga haqqoqin da suke kaina da yawa balle na sake daukar wani shi yasa na rabu da ita amma Allah ya gani ni ba gaba nakeyi da ita ba maslaharta na duba" Umaiman ta fada tana miqewa tsaye itama seta juya ta fita tana cewa
"Nidai na gaya miki kuma ki fitar da kayayyakinki wanda suka miki yawanki bayar akai gidan Mama Nana ta rage miki ki dena yawo kamar wata Yar gudun Hijira"
"Kiyi haquri amma bazan kai kayana gidanta ba, ita ta ringa yawo dani a unguwar nan tana fadar abinda ya faru da Wanda ma be faru ba dayawanmasu shigowa siyan zobo fa badan Allah suke zuwa ba se dan kawai suga yanda na koma. Baki ga tururuwar da aka ringayi ba sanda Salman ya fita dashi yace an dawo yin Zobo a gidan nan, harda Maza A gulma Maman Asad ba kunya suke shigowa da girmansu wai siyan zobo ni wlh har fargabar ranar da zan sake fita daga gidan nan nakeyi nasan gaba daya labarina ya karade ko ina qila har Film da Novel anyi a kaina ko? Inaga bazan sake fita daga gidan nan ba gara nayi zamana nayita istigfari ina hailala har ranar da ubangiji ze dauki raina kawai bazaniya fita ba ina tsoron tozarcin da zan fuskanta idanna fita waje" Umaimah ta fada tana shirin sake fashewa da kuka se Maman Asad taja tsaki tana cewa
"Ai sekiyi, duk me cikakken Imani ya yarda da qaddara me kyau ko mara kyau dan haka idan ya ganta akan dan uwansa ba dariya zeyi masa ba sedai ya nema masa sauqi gurin Allah ya kuma nemi kariya daga afkawa irinta ki nemi yardar Allah kawai shine mafita a gareki ni bari naje yara sun kusa tasowa" daga haka ta fice ta barta. Komawa tayi ta kwanta tana cigaba da tunanin da ya zame mata jiki yake kuma neman zauta mata tunani. Ranar Juma'a su kazo kamar yanda ta gaya mata, Naziyya tazo tun Alhamis amma kamar yanda suka saba tun bayan dawowarta gida ta shata mata layin babu ita babu ita wannan karon ma haka akayi. Ranar Juma'ar da suka takura mata akan tayi haquri ta janye gabar ko babu komai ita babbace tayiwa qanwarta uzuri Kuka ta fasa musu kai tsaye tace
"Babu uzurin da zan mata ai da hankalinta ba mahaukaci bace ita kuma tana sane ta aikata duk abinda tayi ba tareda tayiwa kowa uzuri ba. Ni nasan girma da darajar Iyayena dan haka bazan taba shiri da wanda ya wukaqanta su ba, Yanda ta saka su cikin tasku ta jefe su da maganganu har tayi sanadiyyar zubar hawayensu bazan taba yafe mata ba kuma zata gani, itama ta haifa da ranta dan cikinta seya gwada mata abinda tayi koma wanda ya fishi, haqqin Khalil dana sauran mutanen da kika dauka Umaimah baze taba bari ki zauna lafiya ba".
Gaba dayansu suka dauki salati Cikin tsananin tashin hankali Umaimah ta rushe musu da kuka, Mama ta sallame sallar La'asar da takeyi babu bata lokaci ta dauke Naziyyan da mari tana cewa
"Wace irin zuciya gareki Naziyya dagani har mahaifinku bamu kasance masu taurin kai da kafaffiyar zuciya ba a ina kuka samo taku? taskun da yar uwarki take ciki be isheki ba se kin bita da mugun baki akan me? muda tayiwa laifin munce mun yafe se kece zaki qullaceta ki ja mata mugun Alkaba'i to ahiri dinki kuma idan na isa dake ki janye kalamanki kuma ki shirya da yar uwarki. Iyakar bakin data dibarwa kanta ya isheta base kin bita da naki ba Allah ka shiga lamarin Zuri'ar mu karka saukar da rabuwar kai a tsakaninsu" Maman ta qarasa tana fashewa da kuka itama. Tashin hankalin Umaimah ya qaru, yanda falon ya rikice da kuka kuma ita ce sila. Ta ringa wani irin kuka danta gagara cewa komai, nadamar rayuwarta ta sake daureta, tun usuli itace matsalarsu, itace kukansu duk wani jaye jayen rigima itace bata taba barin zukatansu su huta gashi yanzu tana neman zama silar rugujewar zumunchinsu Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.
Dakyar take tafiya saboda yanda idonta ya rufe bata gani ta samu ta fada kan gadon dakin da take, Nuratu data bi bayanta tana kuka itama ta dagota tana cewa
"Ki kwantar da hankalinki, karki bari maganganunta suyi tasiri a zuciyarki"
"Gaskiya ta fada Nuratu nima kuma na sani, duk abinda yake faruwa a yanzu na tabbata ba komai bane domin tsiyar dana shuka ta zarci na fuskanci iyakar wannan matsin a matsayin sakayya na sani dole haqqi seya bibiyeni amma dan Allah ku tayani roqon Allah kar Yarana su kangare, bana so laifina ya shafesu bana fatan su tashi da mummunar dabi'a irin tawa" ta qarasa tana fashewa da kukan dayafi na farko rauni ta fada jikin Nuratu suka rungume juna suna kukan tare, yanda jikin Umaiman yake rawa ya sakat tsayar da nata kukan dole ta ringa bata baki, dakyar ta dena kukan itama tace mata ta kwanta bata musa ba ta kwanta maganganun Naziyya na mata yawo akai yar uwarta ta jini kenan to inaga wani bare? Wane irin maganganu mutane suke fada akanta? Wace irin tarba zata samu idan ta sake fita duniyar mutane?
Nuratu data fita ce ta koma dakin da ruwa da kwayar magani guda biyu ahannu ta bata, bata musa ba tasha dukda bata san kona menene ba amma tana da buqatar abinda zegusar mata da hankali a yanzu koda bacci ne ta samu tayi kafin zuciyarta ta ida tarwatsewa, kanta sara mata yakeyi kamar ze rabe biyu ga bugun da zuciyarta takeyi ya wuce qa'ida jikinta kansa rawa yakeyi. Tana sha ta mayar da idonta ta kulle bata dauki minti biyar ba bacci me nauyin gaske yayi gaba da ita se sannan Nuratu ta sauke ajiyar zuciya ta fita.
A falon Mama ko kukan da takeyi ya daga musu hankali Matuqa har Anty da hayaniyarsu taja hankalinta ta shiga tayasu kukan, ta kalli Naziyya dake kuka itama tamkar tace
"Kinga ai kun zama daya keda ita har gara ita dan yanzu tana qoqarin goge duk laifukanta ta hanyar farantawa Mahaifiyarku amma ke yanzu me kikayi? Kinyi sanadiyyar zubar hawayenta kin baqanta mata zuciya a zatonki abinda kikeyiwa yar uwarki dadi zataji ko kuwa kin dauka ta dena sonta ne kamar ku? A yanzu babu abinda ze faranta mata illah taga hadin kanku amma a maimakon hakan kina nema ki haifar da sabon tashin hankali a cikin gidan nan iya wanda muka gani a baya ya isa ina roqonku dan girman Allah ku sararawa rayukanku ku rungumi yar uwarku da qaddarar data afka mata dan bata da kowa sama daku.
Idan Umaimah nada laifi kuma kuna dashi saboda baku da wata hujja da zaku kafa data saka kuka barwa Duniya ita kuka zame hannunku daga al'amuranta qarqari kuce bata jin shawararku shiyasa kuka wofantar da ita, da ace kun cigaba da naci da cusa kanku cikin lamuranta da ko baku san komai ba dole zaku san da yawa daga abubuwan da suke faruwa da ita amma kuka barta a hannun qawayen banza da suka kaita suka baro a yanzu babu wanda ze zage su kudin dai ku za'a zaga akan idonku qanwarku ta lalace take abubuwa tamkar bata da kowa a duniya da ze nuna mata daidai. Ke kanki Mama yau zan fada miki kina da naki laifi domin ke kika fara bada qofar da Umaimah ta samu damar yin duk abubuwan da takeyi. Tunda kika san Umaimah zuma ce seda wuta be kamata kiyi mata sako sakon da har zata ringa aiwatar da abubuwa yanda taga dama ba.
Dukkan mu nan shaida ne duk sanda kika murde kika nuna mata fin qarfi tana lankwasuwa tayi abinda kikeso koda ace ba'a dadin rai ba amma zatayi idan kuma kika bata umarni bata qetarewa koda kuwa ranta be so ba, da ace kinci gaba da bibiyar rayuwarta kamar yanda kikeyi da farko da abubuwa da yawa basu faru ba amma se kema kikayi fushin zuciya kika zuba mata ido Alhalin kin san Umaimah tana cikin zubin Halittar da ubangiji yayi basu da tunanin kansu suna amfani da duk abinda suka gani ko sukaji kuma yayi daidai da qawa zucinsu basu duba kyautuwa ko rashin dacewar abu muddin yayi daidai da ra'ayinsu shikenan kinga kenan kamata yayi ace kinci gaba da zama tunaninta kamar yanda kika fara tun farko kina tursasata tabi ra'ayinki koda bata so da yanzu wata maganar akeyi ba wannan ba. Nida nake janta a jiki tana wulaqantani ai ba zuciya ce bani da ita ba data sa na shanye naci gaba jibantar lamuranta nayi hakan ne saboda karta rasa kowa cikin rayuwarta.
"Ba haka nake nufi ba Umaimah. Kece mafi cancanta da ki nemi yafiyarsu abinda nale nufi kici gaba da addu'a har zuwa sanda komai ze daidaita ki samu damar neman yafiyarsu da kanki" seta sassauta kukan tana kallon Hajiyayyen tace
"Kina ganin zasu yafe mun?"
"Meze hana, a rayuwata ban taba ganin mutane masu karamci kamarsu ba Umaimah na tabbatar ko a yanzu sun yi miki afuwa tunda har suka bar Yaranki suke zuwa gurinki hakan yana nuna fushin da sukeyi dake ya ragu, kici gaba da addu'a yanadaga cikin tasirinta" Maman Asad ta fada kafinta miqe tana cewa
"Bari naje saqo na kawowa Mama daman se ranar Juma'a in Allah ya kaimu duk zamu zo Naziyya ma tana tafe ranar Alhamis kuma idan tazo karki kuskura ta sake barin garin nan baku warware gabar dake tsakaninku ba"
"Toh ai ba laifina bane, cewa tayi bata yafe ba idan na sake yi mata magana babu ita babu ni ni kuma naga haqqoqin da suke kaina da yawa balle na sake daukar wani shi yasa na rabu da ita amma Allah ya gani ni ba gaba nakeyi da ita ba maslaharta na duba" Umaiman ta fada tana miqewa tsaye itama seta juya ta fita tana cewa
"Nidai na gaya miki kuma ki fitar da kayayyakinki wanda suka miki yawanki bayar akai gidan Mama Nana ta rage miki ki dena yawo kamar wata Yar gudun Hijira"
"Kiyi haquri amma bazan kai kayana gidanta ba, ita ta ringa yawo dani a unguwar nan tana fadar abinda ya faru da Wanda ma be faru ba dayawanmasu shigowa siyan zobo fa badan Allah suke zuwa ba se dan kawai suga yanda na koma. Baki ga tururuwar da aka ringayi ba sanda Salman ya fita dashi yace an dawo yin Zobo a gidan nan, harda Maza A gulma Maman Asad ba kunya suke shigowa da girmansu wai siyan zobo ni wlh har fargabar ranar da zan sake fita daga gidan nan nakeyi nasan gaba daya labarina ya karade ko ina qila har Film da Novel anyi a kaina ko? Inaga bazan sake fita daga gidan nan ba gara nayi zamana nayita istigfari ina hailala har ranar da ubangiji ze dauki raina kawai bazaniya fita ba ina tsoron tozarcin da zan fuskanta idanna fita waje" Umaimah ta fada tana shirin sake fashewa da kuka se Maman Asad taja tsaki tana cewa
"Ai sekiyi, duk me cikakken Imani ya yarda da qaddara me kyau ko mara kyau dan haka idan ya ganta akan dan uwansa ba dariya zeyi masa ba sedai ya nema masa sauqi gurin Allah ya kuma nemi kariya daga afkawa irinta ki nemi yardar Allah kawai shine mafita a gareki ni bari naje yara sun kusa tasowa" daga haka ta fice ta barta. Komawa tayi ta kwanta tana cigaba da tunanin da ya zame mata jiki yake kuma neman zauta mata tunani. Ranar Juma'a su kazo kamar yanda ta gaya mata, Naziyya tazo tun Alhamis amma kamar yanda suka saba tun bayan dawowarta gida ta shata mata layin babu ita babu ita wannan karon ma haka akayi. Ranar Juma'ar da suka takura mata akan tayi haquri ta janye gabar ko babu komai ita babbace tayiwa qanwarta uzuri Kuka ta fasa musu kai tsaye tace
"Babu uzurin da zan mata ai da hankalinta ba mahaukaci bace ita kuma tana sane ta aikata duk abinda tayi ba tareda tayiwa kowa uzuri ba. Ni nasan girma da darajar Iyayena dan haka bazan taba shiri da wanda ya wukaqanta su ba, Yanda ta saka su cikin tasku ta jefe su da maganganu har tayi sanadiyyar zubar hawayensu bazan taba yafe mata ba kuma zata gani, itama ta haifa da ranta dan cikinta seya gwada mata abinda tayi koma wanda ya fishi, haqqin Khalil dana sauran mutanen da kika dauka Umaimah baze taba bari ki zauna lafiya ba".
Gaba dayansu suka dauki salati Cikin tsananin tashin hankali Umaimah ta rushe musu da kuka, Mama ta sallame sallar La'asar da takeyi babu bata lokaci ta dauke Naziyyan da mari tana cewa
"Wace irin zuciya gareki Naziyya dagani har mahaifinku bamu kasance masu taurin kai da kafaffiyar zuciya ba a ina kuka samo taku? taskun da yar uwarki take ciki be isheki ba se kin bita da mugun baki akan me? muda tayiwa laifin munce mun yafe se kece zaki qullaceta ki ja mata mugun Alkaba'i to ahiri dinki kuma idan na isa dake ki janye kalamanki kuma ki shirya da yar uwarki. Iyakar bakin data dibarwa kanta ya isheta base kin bita da naki ba Allah ka shiga lamarin Zuri'ar mu karka saukar da rabuwar kai a tsakaninsu" Maman ta qarasa tana fashewa da kuka itama. Tashin hankalin Umaimah ya qaru, yanda falon ya rikice da kuka kuma ita ce sila. Ta ringa wani irin kuka danta gagara cewa komai, nadamar rayuwarta ta sake daureta, tun usuli itace matsalarsu, itace kukansu duk wani jaye jayen rigima itace bata taba barin zukatansu su huta gashi yanzu tana neman zama silar rugujewar zumunchinsu Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un.
Dakyar take tafiya saboda yanda idonta ya rufe bata gani ta samu ta fada kan gadon dakin da take, Nuratu data bi bayanta tana kuka itama ta dagota tana cewa
"Ki kwantar da hankalinki, karki bari maganganunta suyi tasiri a zuciyarki"
"Gaskiya ta fada Nuratu nima kuma na sani, duk abinda yake faruwa a yanzu na tabbata ba komai bane domin tsiyar dana shuka ta zarci na fuskanci iyakar wannan matsin a matsayin sakayya na sani dole haqqi seya bibiyeni amma dan Allah ku tayani roqon Allah kar Yarana su kangare, bana so laifina ya shafesu bana fatan su tashi da mummunar dabi'a irin tawa" ta qarasa tana fashewa da kukan dayafi na farko rauni ta fada jikin Nuratu suka rungume juna suna kukan tare, yanda jikin Umaiman yake rawa ya sakat tsayar da nata kukan dole ta ringa bata baki, dakyar ta dena kukan itama tace mata ta kwanta bata musa ba ta kwanta maganganun Naziyya na mata yawo akai yar uwarta ta jini kenan to inaga wani bare? Wane irin maganganu mutane suke fada akanta? Wace irin tarba zata samu idan ta sake fita duniyar mutane?
Nuratu data fita ce ta koma dakin da ruwa da kwayar magani guda biyu ahannu ta bata, bata musa ba tasha dukda bata san kona menene ba amma tana da buqatar abinda zegusar mata da hankali a yanzu koda bacci ne ta samu tayi kafin zuciyarta ta ida tarwatsewa, kanta sara mata yakeyi kamar ze rabe biyu ga bugun da zuciyarta takeyi ya wuce qa'ida jikinta kansa rawa yakeyi. Tana sha ta mayar da idonta ta kulle bata dauki minti biyar ba bacci me nauyin gaske yayi gaba da ita se sannan Nuratu ta sauke ajiyar zuciya ta fita.
A falon Mama ko kukan da takeyi ya daga musu hankali Matuqa har Anty da hayaniyarsu taja hankalinta ta shiga tayasu kukan, ta kalli Naziyya dake kuka itama tamkar tace
"Kinga ai kun zama daya keda ita har gara ita dan yanzu tana qoqarin goge duk laifukanta ta hanyar farantawa Mahaifiyarku amma ke yanzu me kikayi? Kinyi sanadiyyar zubar hawayenta kin baqanta mata zuciya a zatonki abinda kikeyiwa yar uwarki dadi zataji ko kuwa kin dauka ta dena sonta ne kamar ku? A yanzu babu abinda ze faranta mata illah taga hadin kanku amma a maimakon hakan kina nema ki haifar da sabon tashin hankali a cikin gidan nan iya wanda muka gani a baya ya isa ina roqonku dan girman Allah ku sararawa rayukanku ku rungumi yar uwarku da qaddarar data afka mata dan bata da kowa sama daku.
Idan Umaimah nada laifi kuma kuna dashi saboda baku da wata hujja da zaku kafa data saka kuka barwa Duniya ita kuka zame hannunku daga al'amuranta qarqari kuce bata jin shawararku shiyasa kuka wofantar da ita, da ace kun cigaba da naci da cusa kanku cikin lamuranta da ko baku san komai ba dole zaku san da yawa daga abubuwan da suke faruwa da ita amma kuka barta a hannun qawayen banza da suka kaita suka baro a yanzu babu wanda ze zage su kudin dai ku za'a zaga akan idonku qanwarku ta lalace take abubuwa tamkar bata da kowa a duniya da ze nuna mata daidai. Ke kanki Mama yau zan fada miki kina da naki laifi domin ke kika fara bada qofar da Umaimah ta samu damar yin duk abubuwan da takeyi. Tunda kika san Umaimah zuma ce seda wuta be kamata kiyi mata sako sakon da har zata ringa aiwatar da abubuwa yanda taga dama ba.
Dukkan mu nan shaida ne duk sanda kika murde kika nuna mata fin qarfi tana lankwasuwa tayi abinda kikeso koda ace ba'a dadin rai ba amma zatayi idan kuma kika bata umarni bata qetarewa koda kuwa ranta be so ba, da ace kinci gaba da bibiyar rayuwarta kamar yanda kikeyi da farko da abubuwa da yawa basu faru ba amma se kema kikayi fushin zuciya kika zuba mata ido Alhalin kin san Umaimah tana cikin zubin Halittar da ubangiji yayi basu da tunanin kansu suna amfani da duk abinda suka gani ko sukaji kuma yayi daidai da qawa zucinsu basu duba kyautuwa ko rashin dacewar abu muddin yayi daidai da ra'ayinsu shikenan kinga kenan kamata yayi ace kinci gaba da zama tunaninta kamar yanda kika fara tun farko kina tursasata tabi ra'ayinki koda bata so da yanzu wata maganar akeyi ba wannan ba. Nida nake janta a jiki tana wulaqantani ai ba zuciya ce bani da ita ba data sa na shanye naci gaba jibantar lamuranta nayi hakan ne saboda karta rasa kowa cikin rayuwarta.