Sashe 237
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wata uku cikin wannan yanayi Humaira ta fara zazzabi me zafi da Amai suna zuwa Asibiti gwajin farko aka tabbatar masa da tana da shigar ciki bayan an mata scanning suka sanar masa da watannin cikin uku da kwanaki.
Seda numfashinaa ya tsaya na wani lokaci kafin ya dawo hayyacinsa ya rasa gane yanayin da yake ciki, tambayar kansa ya ringayi tayaya hakan zata kasance Humaira da ciki to yaushe wani abu ya shiga tsakaninsu da ita har da zata iya daukar ciki?
Salati kawai ya ringayi a zuciyarsa da a'uziyya bisa ga tunanin da shaidan yake so ya darsa masa wanda ko kusa baya so ya samu gurbi a ransa yana kyautata mata zato kuma koda gaya masa akayi baze yarda ba dan haka baze taba bari tunanin yayi tasiri a ransa ba. Ita kanta bayan data farka daga bacci saboda ruwa da aka sakata sosai ta tsorata dajin wai ciki ne da ita, yanayin yanda ta firgice din ya sake darsa masa wani abu a ransa seya sulale ya fice daga dakin ba tareda yace mata komai ba zuciyarsa ta ringa bugawa kamar zata fito daga qirjinsa wani bangare kuma yana qoqarin kareta ta hanyar nuna masa ba laifinta bane, shiya kasance me son zuciya daya tilasta mata zama dashi alhalin bashida Lafiya tsayin shekara kusan hudu da yarinytarta tabbas dole cutarwa ta shigo ciki.
Can ya samu waje ya zauna ya rasa kalar tunanin daya kamata yayi, yana zaune a gurin yaji an dafashi ya daga kai suka hada ido da Dr Mahmud daya dade tun daga nesa ya hangoshi ya ringa masa magana amma be amsa ba dalilin daya sa ya qarasa kusa dashi kenan. Cikin kulawa da tausayawa yake kallonsa dan a zatonsa matsalar dake damunsa ce ta sakashi zama haka ko gurinsa yazo baya nan tunda shigowarsa kenan shi dan haka yace masa suje office.
"Khalil na sani akwai damuwa ga mutum lafiyayye ya gamu da ibtila'i irin wannan dole abin ze dameka sosai amma abinda nake so ka gane yawan damuwar kansa matsala ne domin yana iya kawo cikas gurin samun abinda ake buqata" Dr Mahmud ya fada bayanda suka zauna a office din se Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace
"Dr samba wannan ne ya dameni baai tun farko na gaya maka na karbi qaddarata a yanda tazo mun, wannan wani al'amari me me daure kai ya sameni daban, yanzu haka maganar da nakeyi maka Matata tana cikin Asibitin nan munzo bata da lafiya kuma an tabbatar mana tana da shigar ciki har wata uku na kasa gane yanda hakan zata yuwu Dr nida bani da lafiya tsahon shekara uku da wani abu yanzu".
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 81
"Calm down Khalil calm down" Dr Mahmud ya fada kafin yaci gaba da cewa
"kar ka bari shaidan ya jefa maka mummunan zato a zuciya shin baka yarda da matarka ba?" ya fada yana kallonsa cikin nutsuwa, se Khalil ya gyara zama yace
"Dr na yarda da ita ba kuma na kawo tunanin cewar Humaira zata ci Amana ta ba amma yanda abun ya zo nake tunani taya ya haka zata faru Dr?"
Se Dr Mahmud ya janyo system din gabansa ya kunna, File din Khalil ya binciko yayi shiru yana dubawa zuwa wani lokaci kafin ya daga kai yana kallonsa yace
"Idan zan iya tunawa, ranar da kace kaji wani abu akan matarka kamar kace har releasing kayi ko?"
Shiru Khalil yayi kafin a sanyaye yace
"Hakane Dr amma bana tunanin wannan ya isa ace an samu ciki, na gaya maka duka faruwar abun ne wuce minti daya ba, ban samimu dama na shiga jikinta ba and before i know komai ya faru ya tsaya kuma bayan hakan ma ya sake faruwa kuma ko yaushe dai kamar yanda na maka complain wani lokacin sena fara qoqarin yi wani ma kafin nayi attempting nakejin ya fita daga nan kuma zanyi loosing interest da strength dina bana ko iya satisfying nata da romance din yanzu" yanda yayi maganar zaka karanci tsantsar damuwa da fargabar da yake ciki Dr Mahmud ya fadada murmushinsa yana cewa
"To ina so ka yarda abinda ya faru a wancan lokacin dalilin samuwar wannan rabon ne har Allah ya baka qarfin yin abinda kayi. Kuma shi sperm da kake gani yana da matuqar sauri, inhar ya samu hanyar shiga jikin mace ko yaya take shikenan kuma kaga se akayi sa'a ita matar a lokacin a shirye kwanta yake koda yake daman Allah ya shirya faruwar hakan kaga wannan yana maka nuni da kaida Amarya duka sharp shooters ne, kaga Dayan Babyn ma kace sau daya akayi aka dace to ga wani ma idan lafiya ta samu se anyi taka tsan tsan idan ba haka ba Amarya zatayi ta jera babys ne duk shekara" ya qarasa maganar cikin zolaya kuma yayi nasarar saka Khalil din murmushi ya dauke kansa gefe Dr yaci gaba da cewa
"Ka kwantar da hankalinka in sha Allahu waraka zata samu baby kuma naka ne karka kuskura shaidan yasa kayi kokonto akansa kaji ko?" Seya daga masa kai alamar yaji ya kuma samu nutsuwa a zuciyarsa dukda cewar daman baya zarginta da cin Amana amma abin ne yazo masa da rudani sannan kukan da takeyi sanda ya gaya mata tana da cikin ya qara dagula masa lissafi to kenan meye dalilin kukanta ita? Abinda ya kamata ya sani yanzu kenan. Sallama yayi wa Dr Mahmud ya fita, dakin da take ya koma ya tarar da it har sannan tana kukan seya nemi guri kusada ita ya zauna cikin nutsuwa yajata jikinsa yana cewa
"Wai kukan me kikeyi haka ne kuma?"
Lafe masa tayi ta rage kukan tana cewa
"Habibi ciki fa, ni wlh tsoro nakeji baka san wahalar dana sha a haihuwar Aryaan ba ko shekara uku beyi ba na sake haihuwa" ta sake fashewa da wani kukan. Ajiyar zuciya me qarfi ya sauke jin dalilin kukan nata daya fi kama da shirme yana shafa bayanta yace
"Shine kike kuka haka baki san haihuwa baiwa bace ba mutane da yawa nema sukeyi basu samu ba fa Humaira"
"Amma da wahala baka san yanda ake jiba" tayi saurin katseshi se yace mata
"Na sani da wahala amma karki butulcewa Allah ki kalli fa a yanayin da muke ciki amma dukda haka yayi ikonsa ya azurtamu da wannan cikin ai murna ya kamata kiyi ba kuka ba".
Shiru tayi tana qoqarin rage kukanta a zuciyarta tunani takeyi shikenan kawai se a ganta da ciki bayan ita ba wani abu tayi ba wai to shi daman cikin daga sama ake samun sa ko yaya tunda dai na Aryaan tasan sunyi abinda ake samu wannan fa?
"Ki share hawayenki kinji kiyi Addu'a Allah ya raya mana in sha Allahu kuma cikin salama zakiyi rainon cikin ki haifeshi ba tareda wahala ba. Ina son yara da yawa fa Humaira ina da burin na tara zuri'a kamar yara Goma sha haka duk nawa amma daga biyu kin karaya to wa kike so ya tara mun su?" Ya fada yana jan hancinta ta janye daga jikinsa tana cewa
"Nidai uku zanyi tunda Maman Bibi tayi uku ai six sun isheka"
"Ina dozen zakiyi in aka hada da nata ukun kinga 15 kenan s nayi Manaji" ya tsokaneta aiko ta zaro ido tana cewa
"Tabdi qarya da ciwo wlh ba zan iya ba kawai ka haqura da abinda Allah ya baka shikenan banda ma kai biyar din ma ai Allah yasa musu Albarka ko?"
"Haba mana nida nake zaton in kika fara haihuwa har sena ce ki bari kodan kasancewar ke kadai aka haifa a gidanku shine daga biyu zaki ce ba haka ba?" Seta miqe tana sake ce masa
"To ai da dabansan ya cikin yake ba nima goma nace zan haifa idan na girma amma yanzu na fasa" ta shige Toilet ya bita da kallo yana mamakin yanda bakinta ya bude sosai yanzu ta rage shirmen yarintar da takeyi da koda yake tana shekaru Ashirin ne fa yanzu tabbas hankali ya ratsata tasan me take so da wanda bata so a yanzu. Yana zaune ta fito sega Nurse ta shigo dakin itama ta sake dubata ganin zafin jikin ya sauka ta bashi takaddar magungunan da aka rubuta musu da next appointment dinta ta basu.
A mota suna tafe babu me cewa komai lokaci lokaci yake kallonta yanda tayi shiru alamar tayi nisa a tunani seya kama hannunta ta daga kai ta kalleshi ya sakar mata murmushi yana cewa
"Komai zeyi daidai da yardar Allah kinji ki qara haquri"
Murmushi ta maida masa kafin ta kwantar da kanta jikin kujera tana cigaba da tunanin da takeyi a ranta. Da suka isa gidan seda ya rakata ta kwanta kafin ya wuce gurin Hajiya dan da wuri suka fita be samu ya shiga ba bayan sun gaisa take tambayarsa jikin Humairan yace da sauqi yana shafa kai dan be santa yanda ze fadawa Hajiya maganar cikin ba, bari kawai yayi akan idan lokaci yayi da kanta zata gani be jima ba ya wuce office dan ya rigada ya makara ma.
Seda numfashinaa ya tsaya na wani lokaci kafin ya dawo hayyacinsa ya rasa gane yanayin da yake ciki, tambayar kansa ya ringayi tayaya hakan zata kasance Humaira da ciki to yaushe wani abu ya shiga tsakaninsu da ita har da zata iya daukar ciki?
Salati kawai ya ringayi a zuciyarsa da a'uziyya bisa ga tunanin da shaidan yake so ya darsa masa wanda ko kusa baya so ya samu gurbi a ransa yana kyautata mata zato kuma koda gaya masa akayi baze yarda ba dan haka baze taba bari tunanin yayi tasiri a ransa ba. Ita kanta bayan data farka daga bacci saboda ruwa da aka sakata sosai ta tsorata dajin wai ciki ne da ita, yanayin yanda ta firgice din ya sake darsa masa wani abu a ransa seya sulale ya fice daga dakin ba tareda yace mata komai ba zuciyarsa ta ringa bugawa kamar zata fito daga qirjinsa wani bangare kuma yana qoqarin kareta ta hanyar nuna masa ba laifinta bane, shiya kasance me son zuciya daya tilasta mata zama dashi alhalin bashida Lafiya tsayin shekara kusan hudu da yarinytarta tabbas dole cutarwa ta shigo ciki.
Can ya samu waje ya zauna ya rasa kalar tunanin daya kamata yayi, yana zaune a gurin yaji an dafashi ya daga kai suka hada ido da Dr Mahmud daya dade tun daga nesa ya hangoshi ya ringa masa magana amma be amsa ba dalilin daya sa ya qarasa kusa dashi kenan. Cikin kulawa da tausayawa yake kallonsa dan a zatonsa matsalar dake damunsa ce ta sakashi zama haka ko gurinsa yazo baya nan tunda shigowarsa kenan shi dan haka yace masa suje office.
"Khalil na sani akwai damuwa ga mutum lafiyayye ya gamu da ibtila'i irin wannan dole abin ze dameka sosai amma abinda nake so ka gane yawan damuwar kansa matsala ne domin yana iya kawo cikas gurin samun abinda ake buqata" Dr Mahmud ya fada bayanda suka zauna a office din se Khalil ya sauke ajiyar zuciya yace
"Dr samba wannan ne ya dameni baai tun farko na gaya maka na karbi qaddarata a yanda tazo mun, wannan wani al'amari me me daure kai ya sameni daban, yanzu haka maganar da nakeyi maka Matata tana cikin Asibitin nan munzo bata da lafiya kuma an tabbatar mana tana da shigar ciki har wata uku na kasa gane yanda hakan zata yuwu Dr nida bani da lafiya tsahon shekara uku da wani abu yanzu".
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK*
*(UMMU-MAHEER)*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATON*
*(DON CIGABAN ADABIN HAUSA)*
Page 81
"Calm down Khalil calm down" Dr Mahmud ya fada kafin yaci gaba da cewa
"kar ka bari shaidan ya jefa maka mummunan zato a zuciya shin baka yarda da matarka ba?" ya fada yana kallonsa cikin nutsuwa, se Khalil ya gyara zama yace
"Dr na yarda da ita ba kuma na kawo tunanin cewar Humaira zata ci Amana ta ba amma yanda abun ya zo nake tunani taya ya haka zata faru Dr?"
Se Dr Mahmud ya janyo system din gabansa ya kunna, File din Khalil ya binciko yayi shiru yana dubawa zuwa wani lokaci kafin ya daga kai yana kallonsa yace
"Idan zan iya tunawa, ranar da kace kaji wani abu akan matarka kamar kace har releasing kayi ko?"
Shiru Khalil yayi kafin a sanyaye yace
"Hakane Dr amma bana tunanin wannan ya isa ace an samu ciki, na gaya maka duka faruwar abun ne wuce minti daya ba, ban samimu dama na shiga jikinta ba and before i know komai ya faru ya tsaya kuma bayan hakan ma ya sake faruwa kuma ko yaushe dai kamar yanda na maka complain wani lokacin sena fara qoqarin yi wani ma kafin nayi attempting nakejin ya fita daga nan kuma zanyi loosing interest da strength dina bana ko iya satisfying nata da romance din yanzu" yanda yayi maganar zaka karanci tsantsar damuwa da fargabar da yake ciki Dr Mahmud ya fadada murmushinsa yana cewa
"To ina so ka yarda abinda ya faru a wancan lokacin dalilin samuwar wannan rabon ne har Allah ya baka qarfin yin abinda kayi. Kuma shi sperm da kake gani yana da matuqar sauri, inhar ya samu hanyar shiga jikin mace ko yaya take shikenan kuma kaga se akayi sa'a ita matar a lokacin a shirye kwanta yake koda yake daman Allah ya shirya faruwar hakan kaga wannan yana maka nuni da kaida Amarya duka sharp shooters ne, kaga Dayan Babyn ma kace sau daya akayi aka dace to ga wani ma idan lafiya ta samu se anyi taka tsan tsan idan ba haka ba Amarya zatayi ta jera babys ne duk shekara" ya qarasa maganar cikin zolaya kuma yayi nasarar saka Khalil din murmushi ya dauke kansa gefe Dr yaci gaba da cewa
"Ka kwantar da hankalinka in sha Allahu waraka zata samu baby kuma naka ne karka kuskura shaidan yasa kayi kokonto akansa kaji ko?" Seya daga masa kai alamar yaji ya kuma samu nutsuwa a zuciyarsa dukda cewar daman baya zarginta da cin Amana amma abin ne yazo masa da rudani sannan kukan da takeyi sanda ya gaya mata tana da cikin ya qara dagula masa lissafi to kenan meye dalilin kukanta ita? Abinda ya kamata ya sani yanzu kenan. Sallama yayi wa Dr Mahmud ya fita, dakin da take ya koma ya tarar da it har sannan tana kukan seya nemi guri kusada ita ya zauna cikin nutsuwa yajata jikinsa yana cewa
"Wai kukan me kikeyi haka ne kuma?"
Lafe masa tayi ta rage kukan tana cewa
"Habibi ciki fa, ni wlh tsoro nakeji baka san wahalar dana sha a haihuwar Aryaan ba ko shekara uku beyi ba na sake haihuwa" ta sake fashewa da wani kukan. Ajiyar zuciya me qarfi ya sauke jin dalilin kukan nata daya fi kama da shirme yana shafa bayanta yace
"Shine kike kuka haka baki san haihuwa baiwa bace ba mutane da yawa nema sukeyi basu samu ba fa Humaira"
"Amma da wahala baka san yanda ake jiba" tayi saurin katseshi se yace mata
"Na sani da wahala amma karki butulcewa Allah ki kalli fa a yanayin da muke ciki amma dukda haka yayi ikonsa ya azurtamu da wannan cikin ai murna ya kamata kiyi ba kuka ba".
Shiru tayi tana qoqarin rage kukanta a zuciyarta tunani takeyi shikenan kawai se a ganta da ciki bayan ita ba wani abu tayi ba wai to shi daman cikin daga sama ake samun sa ko yaya tunda dai na Aryaan tasan sunyi abinda ake samu wannan fa?
"Ki share hawayenki kinji kiyi Addu'a Allah ya raya mana in sha Allahu kuma cikin salama zakiyi rainon cikin ki haifeshi ba tareda wahala ba. Ina son yara da yawa fa Humaira ina da burin na tara zuri'a kamar yara Goma sha haka duk nawa amma daga biyu kin karaya to wa kike so ya tara mun su?" Ya fada yana jan hancinta ta janye daga jikinsa tana cewa
"Nidai uku zanyi tunda Maman Bibi tayi uku ai six sun isheka"
"Ina dozen zakiyi in aka hada da nata ukun kinga 15 kenan s nayi Manaji" ya tsokaneta aiko ta zaro ido tana cewa
"Tabdi qarya da ciwo wlh ba zan iya ba kawai ka haqura da abinda Allah ya baka shikenan banda ma kai biyar din ma ai Allah yasa musu Albarka ko?"
"Haba mana nida nake zaton in kika fara haihuwa har sena ce ki bari kodan kasancewar ke kadai aka haifa a gidanku shine daga biyu zaki ce ba haka ba?" Seta miqe tana sake ce masa
"To ai da dabansan ya cikin yake ba nima goma nace zan haifa idan na girma amma yanzu na fasa" ta shige Toilet ya bita da kallo yana mamakin yanda bakinta ya bude sosai yanzu ta rage shirmen yarintar da takeyi da koda yake tana shekaru Ashirin ne fa yanzu tabbas hankali ya ratsata tasan me take so da wanda bata so a yanzu. Yana zaune ta fito sega Nurse ta shigo dakin itama ta sake dubata ganin zafin jikin ya sauka ta bashi takaddar magungunan da aka rubuta musu da next appointment dinta ta basu.
A mota suna tafe babu me cewa komai lokaci lokaci yake kallonta yanda tayi shiru alamar tayi nisa a tunani seya kama hannunta ta daga kai ta kalleshi ya sakar mata murmushi yana cewa
"Komai zeyi daidai da yardar Allah kinji ki qara haquri"
Murmushi ta maida masa kafin ta kwantar da kanta jikin kujera tana cigaba da tunanin da takeyi a ranta. Da suka isa gidan seda ya rakata ta kwanta kafin ya wuce gurin Hajiya dan da wuri suka fita be samu ya shiga ba bayan sun gaisa take tambayarsa jikin Humairan yace da sauqi yana shafa kai dan be santa yanda ze fadawa Hajiya maganar cikin ba, bari kawai yayi akan idan lokaci yayi da kanta zata gani be jima ba ya wuce office dan ya rigada ya makara ma.