Sashe 43
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga nan gidan Hajiyarsa suka biya, beyi zaton Jalila zata gaya mata zancen cikin ba seda sukaje kunya tsakanin shida Umaimah aka rasa wanda ze boye wani ita kuwa Hajiya ko a jikinta jan Umaiman take tana gwada mata hanyoyin da zata kula da kanta da abubuwan da zata ringayi. A gidan sukayi sallar Magriba da Isha sukaci Tuwon da Hajiyar tayi da kanta kafin ta zuba musu wani suka tafi dashi ko zasuyi dumame tana sake jaddadawa Umaiman ta kula da kanta ta kuma ringa Addu'a, karta yi wasa da Azkar din safe da yamma dana kwanciya bacci idan an kwana biyu zatazo gidan zata taho mata da saqo da haka sukayi sallama bayan data hada ta da tarin kayan kwalamar da akasan masu ciki dasu, zuciyar Umaimah fal da soyayyar Dattijuwar, yanda take ji da ita take nuna mata qauna ko Mamanta data haifeta bata nuna haka a fili ita kam me zatacewa Allah banda godiya.
Suna tafe a hanya tana duba waya, abin da ta lura da sababbin yan group din nasu basu fiya hira da rana ba seda daddare, koda yake daga jiyan zuwa yau ta fahimci da yawan su manyan mata ne ma'aikata da kuma yan kasuwa shiyasa basu da lokaci da rana se dare lokacin kowa ya gama uzurinsa.
"Nifa wayar nan taki ta fara shiga haqqina gaskiya, shikenan yanzu bazakiyi hira dani ba sedai kiyi ta danna waya kina dariya ke kadai" Khalil ya fada yana tabata ganin yana ta magana shikadai bata ma san yanayi ba.
Dagowa tayi ta kalle shi tayi murmushi tace
"Kasan na dade bani da waya yanzu ina dokinta ne"
"Nidai ban yarda ba daga yanzu indai muna tare karbe ta zan ringayi na yarda idan bana nan kiyita chatting dinki amma indai ina nan dukka lokacinki nawa ne" Ya sake fada daidai sanda suke karya kwanar gidansu, seta kashe data ta zura wayar a jaka tace
"An gama yallabai ka gani ma na kashe ta bazan sake kunna Data ba se Allah ya kaimu gobe"
"Yawwa na tuna gobe Saturday ko may be zamuje Kaduna akwai aikin da zan duba ban dai gama tabbatar da tafiyar ba tukunna amma dai ki kwanta cikin shiru saboda tsaro"
"Allah ya kaimu, yanzu se na hada kaya kwana nawa zamuyi?" Ta tambaye shi dukda qasan ranta bata so dan ita haka Allah yayita bata son tafiye tafiye ba kuma tayi zaton idan sunyi aure da ita ze ringa yawon gari garin da yakeyi duba aiki ba.
"Karki damu kawai kiyi parking abubuwa masu muhimmanci, kayan sawa idan munje zamu siya dan nima ban san kwana nawa zanyi ba kinga daman bamu je honeymoon ba daga can kawai se muyi can muyita zaga gari har se an ganmu kawai" ya fada yana kashe mata ido daidai sanda ya paka mota a qofar gida, seta jefa masa hararar wasa ya fita ya bude Get ya dawo yana cewa
"Kinga da kin iya mota kawai shigo da ita zakiyi amma yanzu se naje na kuma dawowa"
"Uhm" Umaimah tace, ta gaji sosai dan haka suna shiga wanka ta farayi da ruwa me zafi sosai ta gasa jikinta, cikin kayan da Hajiya ta bata ta lalubo tsami gaye ta zauna tana sha saboda jin bakinta da tayi babu dadi, wai yanzu cikine da ita itama zata haifi Da tab lallai akwai bidiri ranar.
Da wuri suka kwanta saboda tafiyar da aka tabbatar masa zeyi a goben, Umaimah dake kwance lamo kamar me bacci ta miqe a hankali bayan data tabbatar da baccin Khalil din yayi nisa.
Palour ta koma ta kwanta ta hau WhatsApp lokacin qarfe goma da yan mintina a sannan kasuwar gidan Qasaitacciyar Mace ta faraci.
Hira tayi dadi ita da ta fito da niyyar tadan duba abinda aka tattauna ta koma se gashi ta shantake se jin muryar Khalil tayi a kanta yana tambayar me takeyi a nan cikin daren nan?
Assalamu Alaikum mutanen Kwarai👍
Shin kina son kwarewa fannin girke girken zamani,snacks da sauransu
Hajiya ta💃 ga dama ta samu Mun bude online class wanda zamu koyar da girkin zamani yanda ake sarrafasu ta hanyoyi da dama…Akan kudi qalilan 200 ga mutane 10…daga bisano ze koma 300 kacal kedai kawai tura kudin ki ta wann acct din…..
1509536481
Rabiatu Nuhu Aliyu
Access bank
https://chat.whatsapp.com/IL3QnKmFxojAATF6WkzGxK
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 21
"Na kasa bacci, shine na fito nan saboda bana so na tashe ka kaga zakayi Driving da safe" ta fada tana tura wayarta qasan pillow. Se daya karanci yanayinta na wasu seconds kafin ya qarasa kusa da ita yana cewa
"Shine zaki fito cikin dare ki zauna ke kadai kina dariya? Me yasa baki tashe ni ba ko ki zauna a cikin dakin?"
"Bana so na katse maka baccinka kuma kwanciyar ce naji bazan iya ba shiyasa na fito nan kar motsina yayita damunka" ta sake marairaicewa,
"Hmm" Khalil yace dan beyarda sam da maganar ta ba amma ya share ya ruqo hannunta yana cewa
"Tashi muje ki kwanta kuma ko ba yau ba karki sake tashi cikin dare ki fito ki zauna ko dan saboda lafiyarki da abinda yake cikinki".
Seda tayi Addu'a ta kwanta kafin ya kashe musu fitila shima ya kwanta a gefenta, ji yayi baccin da yaje idonsa ya tafi dan daman ruwa ya farka ze sha ya duba be ganta ba abinda yasa ya fita nemanta kenan.
Wannan sabuwar Dabi'ar tata ta chatting din dare ta fara damunsa dan shi a rayuwarsa duk inda qarfe goma take ya sauka Online, ko kafin ya aureta haka suke goma nayi sukeyin sallama kenan idan ya kashe Data ita ci gaba takeyi da chatting dinta har tsakar dare kenan?
"Wai ma dawa take chatting din?" Zuciyarsa ta jefo masa tambayar, baya so ta dasa mata zargin wani abu a ransa amma qaryar da takeyi masa da yanda take boye waya duk sanda ya kamata yasa yaji yana son ganin menene a cikin wayar tata.
Kallon Umaimah da bacci yayi awon gaba da ita daga kwanciyarta tana sauke numfashi hankali kwance yayi, a nutse ya miqe dan ma karta ji qarar qofa daya bude se ya tokareta ya barta a bid ya wuce kan kujerar data bar wayar ya dauka.
Da contacts dinta ya fara daga farko har qarshe numbobin tarkaceb qawayentane babu adadi sena yan uwa dan ze iya irgi number dayaga sunan namiji akai. Bangaren kira ya koma nan ma yawanci kiransa ne sena yan gidansu da kuma Hajiyarsa, haka yayi ta shige da fice yana bincike a wayar har WhatsApp da Facebook dinta seda ya duba babu wani abu na rashin gaskiya a ciki, lokacin qarfe biyu harta gota da yake a kunne tabar Datar yana kallon messages nata shigowa daga wasu groups daya tabbatar da abinda yake sakata raba dare tana chat din kenan, to kuwa tabbas ze taka mata burki be hanata hira da kowa ba da rana amma duk inda ya dawo gida lokacinta nasa ne dole ta ajiye kowa da komai ta fuskance shi idan ba haka ba kuma ya kwace wayar kowa ya huta tunda ita batajin magana.
Kashe mata Datar yayi ya jona a chaji kafin ya koma ya kwanta, da Asuba dukkansu suka makara tashi saboda rashin komawa bacci da wurin da basuyi ba, shiya ja su jam'i, suna idarwa Umaimah ta kwanta a gurin dan wani bacci takeji sosai.
"Ki tashi kin san muna da tafiya a gabanmu" Khalil ya fada murya a daure, seta miqe zaune tana tura baki, be kulata ba ya shige bandaki tana jin alamar zubar ruwa tasan wanka yake seta fice daga dakin tana qunquni
"Se kace ni nace ina so naje ni da zakayi tafiyarka ka barni ma da nafi son haka" ta wuce kitchen ta dora ruwan shayi ta soya kwai tunda akwai bread.
Qarfe takwas suka kama hanyar Kaduna, shi yake tuqi tana zaune a gefensa tasha kwalliya da wata farar Abaya fuskarta se walwali takeyi suna tafe suna yar hira jefi jefi har Khalil ya gaji da yanda idan yayi magana daya seta dauki lokaci kafin ta bashi amsa saboda hankalinta gaba daya yana kan wayar ta se yayi mata shiru ya kunna radio kawai a ransa yana ayyana yanda zero magance wannan danne dannen wayar tata.
Qarfe sha biyu saura suka shiga Kaduna, kai tsaye hotel din daya rigada yayi musu booking daki ya nufa da ita, a gurguje ya karbi mukulli ya rakata dakin ya nuna mata wayar tafi da gidanka da zata kira idan tana da buqatar wani abun a kawo mata kafin ya wuce Site din da zeyi aiki dan tun suna hanya suke kiransa a waya.
Khalil na fita ta zare doguwar rigar jikinta ya rage skin tight da vest da ta saka a qasa ta haye kan gadon daya sha shimfida bayan data ware Ac ta duqufa kan wayarta tana sana'ar Chatting.
Rufaida ce tayi mata magana tana mata qorafin bata shiga barka ba kwana biyu bata online ma bata nemeta ba se Umaimahn ta bata haquri da uzurin bata gari amma da sun dawo zata shigo.
"Ai naga kin zama yar gida a Group har cigiyarki ake idan anjiki shiru" Rufaidan ta turo mata, se Umaimah tayi murmushi kafin ta mayar mata da cewa
"Ai group din naku akwai qaruwa kullum ana kawo topics masu ma'ana da dole kaima se ka bayarda taka gudummawar"
"Wai me yasa ma kika fita daga wancan group din bayan abubuwan qaruwa ake turowa? Kinsan fa zamanin nan dole seka tashi tsaye ka zama karuwa a cikin gidanka idan kina so ki kama mijinki a hannu dab dai kinsan yanda yanzu maza suka baci da yawon biye biye, to duk irin abubuwan da matan wajen suke musu kenan mu na gida kace kunya ka kasa sakewa ka bawa miji farinciki. Wani ma ko baya biye biye zakiga yana kallo a waya se ya zama kome zakiyi masa da yar qaramar wayewarki ba zaki burge shi ba" Rufaidah ta turo mata da voice.
Suna tafe a hanya tana duba waya, abin da ta lura da sababbin yan group din nasu basu fiya hira da rana ba seda daddare, koda yake daga jiyan zuwa yau ta fahimci da yawan su manyan mata ne ma'aikata da kuma yan kasuwa shiyasa basu da lokaci da rana se dare lokacin kowa ya gama uzurinsa.
"Nifa wayar nan taki ta fara shiga haqqina gaskiya, shikenan yanzu bazakiyi hira dani ba sedai kiyi ta danna waya kina dariya ke kadai" Khalil ya fada yana tabata ganin yana ta magana shikadai bata ma san yanayi ba.
Dagowa tayi ta kalle shi tayi murmushi tace
"Kasan na dade bani da waya yanzu ina dokinta ne"
"Nidai ban yarda ba daga yanzu indai muna tare karbe ta zan ringayi na yarda idan bana nan kiyita chatting dinki amma indai ina nan dukka lokacinki nawa ne" Ya sake fada daidai sanda suke karya kwanar gidansu, seta kashe data ta zura wayar a jaka tace
"An gama yallabai ka gani ma na kashe ta bazan sake kunna Data ba se Allah ya kaimu gobe"
"Yawwa na tuna gobe Saturday ko may be zamuje Kaduna akwai aikin da zan duba ban dai gama tabbatar da tafiyar ba tukunna amma dai ki kwanta cikin shiru saboda tsaro"
"Allah ya kaimu, yanzu se na hada kaya kwana nawa zamuyi?" Ta tambaye shi dukda qasan ranta bata so dan ita haka Allah yayita bata son tafiye tafiye ba kuma tayi zaton idan sunyi aure da ita ze ringa yawon gari garin da yakeyi duba aiki ba.
"Karki damu kawai kiyi parking abubuwa masu muhimmanci, kayan sawa idan munje zamu siya dan nima ban san kwana nawa zanyi ba kinga daman bamu je honeymoon ba daga can kawai se muyi can muyita zaga gari har se an ganmu kawai" ya fada yana kashe mata ido daidai sanda ya paka mota a qofar gida, seta jefa masa hararar wasa ya fita ya bude Get ya dawo yana cewa
"Kinga da kin iya mota kawai shigo da ita zakiyi amma yanzu se naje na kuma dawowa"
"Uhm" Umaimah tace, ta gaji sosai dan haka suna shiga wanka ta farayi da ruwa me zafi sosai ta gasa jikinta, cikin kayan da Hajiya ta bata ta lalubo tsami gaye ta zauna tana sha saboda jin bakinta da tayi babu dadi, wai yanzu cikine da ita itama zata haifi Da tab lallai akwai bidiri ranar.
Da wuri suka kwanta saboda tafiyar da aka tabbatar masa zeyi a goben, Umaimah dake kwance lamo kamar me bacci ta miqe a hankali bayan data tabbatar da baccin Khalil din yayi nisa.
Palour ta koma ta kwanta ta hau WhatsApp lokacin qarfe goma da yan mintina a sannan kasuwar gidan Qasaitacciyar Mace ta faraci.
Hira tayi dadi ita da ta fito da niyyar tadan duba abinda aka tattauna ta koma se gashi ta shantake se jin muryar Khalil tayi a kanta yana tambayar me takeyi a nan cikin daren nan?
Assalamu Alaikum mutanen Kwarai👍
Shin kina son kwarewa fannin girke girken zamani,snacks da sauransu
Hajiya ta💃 ga dama ta samu Mun bude online class wanda zamu koyar da girkin zamani yanda ake sarrafasu ta hanyoyi da dama…Akan kudi qalilan 200 ga mutane 10…daga bisano ze koma 300 kacal kedai kawai tura kudin ki ta wann acct din…..
1509536481
Rabiatu Nuhu Aliyu
Access bank
https://chat.whatsapp.com/IL3QnKmFxojAATF6WkzGxK
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 21
"Na kasa bacci, shine na fito nan saboda bana so na tashe ka kaga zakayi Driving da safe" ta fada tana tura wayarta qasan pillow. Se daya karanci yanayinta na wasu seconds kafin ya qarasa kusa da ita yana cewa
"Shine zaki fito cikin dare ki zauna ke kadai kina dariya? Me yasa baki tashe ni ba ko ki zauna a cikin dakin?"
"Bana so na katse maka baccinka kuma kwanciyar ce naji bazan iya ba shiyasa na fito nan kar motsina yayita damunka" ta sake marairaicewa,
"Hmm" Khalil yace dan beyarda sam da maganar ta ba amma ya share ya ruqo hannunta yana cewa
"Tashi muje ki kwanta kuma ko ba yau ba karki sake tashi cikin dare ki fito ki zauna ko dan saboda lafiyarki da abinda yake cikinki".
Seda tayi Addu'a ta kwanta kafin ya kashe musu fitila shima ya kwanta a gefenta, ji yayi baccin da yaje idonsa ya tafi dan daman ruwa ya farka ze sha ya duba be ganta ba abinda yasa ya fita nemanta kenan.
Wannan sabuwar Dabi'ar tata ta chatting din dare ta fara damunsa dan shi a rayuwarsa duk inda qarfe goma take ya sauka Online, ko kafin ya aureta haka suke goma nayi sukeyin sallama kenan idan ya kashe Data ita ci gaba takeyi da chatting dinta har tsakar dare kenan?
"Wai ma dawa take chatting din?" Zuciyarsa ta jefo masa tambayar, baya so ta dasa mata zargin wani abu a ransa amma qaryar da takeyi masa da yanda take boye waya duk sanda ya kamata yasa yaji yana son ganin menene a cikin wayar tata.
Kallon Umaimah da bacci yayi awon gaba da ita daga kwanciyarta tana sauke numfashi hankali kwance yayi, a nutse ya miqe dan ma karta ji qarar qofa daya bude se ya tokareta ya barta a bid ya wuce kan kujerar data bar wayar ya dauka.
Da contacts dinta ya fara daga farko har qarshe numbobin tarkaceb qawayentane babu adadi sena yan uwa dan ze iya irgi number dayaga sunan namiji akai. Bangaren kira ya koma nan ma yawanci kiransa ne sena yan gidansu da kuma Hajiyarsa, haka yayi ta shige da fice yana bincike a wayar har WhatsApp da Facebook dinta seda ya duba babu wani abu na rashin gaskiya a ciki, lokacin qarfe biyu harta gota da yake a kunne tabar Datar yana kallon messages nata shigowa daga wasu groups daya tabbatar da abinda yake sakata raba dare tana chat din kenan, to kuwa tabbas ze taka mata burki be hanata hira da kowa ba da rana amma duk inda ya dawo gida lokacinta nasa ne dole ta ajiye kowa da komai ta fuskance shi idan ba haka ba kuma ya kwace wayar kowa ya huta tunda ita batajin magana.
Kashe mata Datar yayi ya jona a chaji kafin ya koma ya kwanta, da Asuba dukkansu suka makara tashi saboda rashin komawa bacci da wurin da basuyi ba, shiya ja su jam'i, suna idarwa Umaimah ta kwanta a gurin dan wani bacci takeji sosai.
"Ki tashi kin san muna da tafiya a gabanmu" Khalil ya fada murya a daure, seta miqe zaune tana tura baki, be kulata ba ya shige bandaki tana jin alamar zubar ruwa tasan wanka yake seta fice daga dakin tana qunquni
"Se kace ni nace ina so naje ni da zakayi tafiyarka ka barni ma da nafi son haka" ta wuce kitchen ta dora ruwan shayi ta soya kwai tunda akwai bread.
Qarfe takwas suka kama hanyar Kaduna, shi yake tuqi tana zaune a gefensa tasha kwalliya da wata farar Abaya fuskarta se walwali takeyi suna tafe suna yar hira jefi jefi har Khalil ya gaji da yanda idan yayi magana daya seta dauki lokaci kafin ta bashi amsa saboda hankalinta gaba daya yana kan wayar ta se yayi mata shiru ya kunna radio kawai a ransa yana ayyana yanda zero magance wannan danne dannen wayar tata.
Qarfe sha biyu saura suka shiga Kaduna, kai tsaye hotel din daya rigada yayi musu booking daki ya nufa da ita, a gurguje ya karbi mukulli ya rakata dakin ya nuna mata wayar tafi da gidanka da zata kira idan tana da buqatar wani abun a kawo mata kafin ya wuce Site din da zeyi aiki dan tun suna hanya suke kiransa a waya.
Khalil na fita ta zare doguwar rigar jikinta ya rage skin tight da vest da ta saka a qasa ta haye kan gadon daya sha shimfida bayan data ware Ac ta duqufa kan wayarta tana sana'ar Chatting.
Rufaida ce tayi mata magana tana mata qorafin bata shiga barka ba kwana biyu bata online ma bata nemeta ba se Umaimahn ta bata haquri da uzurin bata gari amma da sun dawo zata shigo.
"Ai naga kin zama yar gida a Group har cigiyarki ake idan anjiki shiru" Rufaidan ta turo mata, se Umaimah tayi murmushi kafin ta mayar mata da cewa
"Ai group din naku akwai qaruwa kullum ana kawo topics masu ma'ana da dole kaima se ka bayarda taka gudummawar"
"Wai me yasa ma kika fita daga wancan group din bayan abubuwan qaruwa ake turowa? Kinsan fa zamanin nan dole seka tashi tsaye ka zama karuwa a cikin gidanka idan kina so ki kama mijinki a hannu dab dai kinsan yanda yanzu maza suka baci da yawon biye biye, to duk irin abubuwan da matan wajen suke musu kenan mu na gida kace kunya ka kasa sakewa ka bawa miji farinciki. Wani ma ko baya biye biye zakiga yana kallo a waya se ya zama kome zakiyi masa da yar qaramar wayewarki ba zaki burge shi ba" Rufaidah ta turo mata da voice.