Sashe 180
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yanzu akan dan wannan abun kike kuka kamar wadda akazo daukar ranta wallahi Umaimah Jidalinki na banza da wofi ne. In banda ke banma san me zan kiraki ba shi aikin ce miki akayi ana yi take yanke yake ci daman se kace wani tsafi? To ai ko tsafi Malama se Aljanun sun samu zama a Jikin mutum kafin su fara aikinsu kuma wannan dinma ai kya jira duk abinda kikayi yabi jikinsu kafin kice zaki fara gwada iko nidai nayi mamaki da a dare daya kika ce aiki har yaci koda yake hayaqin da ya baki na Jinnil Ashiq ne da kwarjini to su babu Mamaki idan kince sun miki aiki amma rufin baki dai se a hankali ai bawai nan take ne zasu kasa musa miki ba. Kawai yanzu ki share hawaye ki dena wannan kukan idan kin samu dama gobe ki fito mu koma gun Malam in kuma ba zaki iya ba zan kirashi ko aikene se yayiwo miki a samu a daidaita a shashantar da maganar auran".
Haka ta ringa lallabata tana sake tabbatar mata da ta kwantar da hankalinta tasan aikin Malam zeci kawai haquri zata koya da danne zuciya nadan lokaci kafin Ludayinta ya hau kan Dawo seda taga ta dan nutsu kafin sukayi sallama akan gobe ita Safinan zataje gurin Malam taji koda abinda ze qara bata tunda ita Umaimah ta kafe bazata koma ba kuma se an biyata kudinta. A nan inda suka gama waya da Safina baccin wahala yayi gaba da ita, bata farka ba se uku da motsi na dare shima wata Azababbiyar Yunwa ce ta tada ta se a sannan tayi sallar Magriba da Ishar da batayi ba.
KHALIL
Tunda ya samu ya haye Sama ba tareda sun sake haduwa da Umaimah ba be sakko ba, yana so yaje gurin Hajiya amma besan me zece mata ba. Matarsa ta zageta ta kirata munafuka amma ya kasa yin komai to da wanne ido ze kalli Hajiyar?
Haka ya kwana saqa da warwara akan abinda ya kamata yayi, wani sashe na zuciyarsa yana ganin beyiwa Humaira Adalci ba da yake shirin janyota cikin wannan rayuwar da yake a ciki inda wani bangare yake tabbatar masa da ita ce warakarsa, za kuma ta fiddashi daga duk wani qunci da damuwa da yake ciki ta maye masa da tarin farinciki da ya dade yana mafarkin samu idan Umaimah ta barsu kenan.
Tunanin raba musu gida ya fado masa yana ganin hakan shine ze kawo masa sauqin da kuma kwanciyar hankali idan ya zamana kowacce tana muhallinta na daban ba kamar yanda Su Jalilah suke fadin ya ajiye Humaira a nan separate part dinsa na Sama da Umaimah ta hanashi amfani dashi hasashenta ya tabbata kenan daman da tace dan wata ya gina gaskiya baya zaton haka zata yuwuwu gara ya gyara tsohon gidansu da suka taso ya ajiye Humairan a can yafi musu kwanciyar hankali daga shi har ita. Yana gama tunanin ya miqe ya dakko Laptop dinsa, seda ya duba lokaci sha biyu ta gota kafin ya bude ya shiga binciko proposal design din dayayi ze maida ginin dan da yayi niyyar ya gyara shi ne ya siyar amma yanzu zeyi masa amfani. Zanen ya duba ya dakko takadda da biro ya shiga lissafin abinda yake ganin ze kashe da tsahon lokacin da ze dauka kafin ya kammalu, a nasa lissafin idan yayi sauri yana ganin ze gama a wata uku in kuma yaja lokaci wata biyar zuwa shida, akan wata shidan ya bari ze gayawa su Baba Abu idan sunje neman auran su saka rana wata shidan zuwa sannan yasan hatta ita Umaiman tayi duk abinda zatayi ta saduda shikenan.
Washe gari bakwai bata qarasa ba ya bar gidan, a waya ya kira Hajiya yayi mata qaryar ya tafi Rano, yanda batayi masa maganar jiya ha shima beyi ba illah ce masa da tayi Jalilah ta kawo kaya jiya idan ya dawo ya shiga ya gani yace mata toh gaba daya beji dadi ba saboda yanda yaji muryarta yasan abinda Umaiman tayi mata ya doketa sosai kawai dai ta shanye ne bata nuna ba. Seda ya kira Habiba ta tabbatar masa Hajiyar na lafiya kawai dai magana ce bata cikayi ba tun jiyan se ta zauna tayi shiru yace mata ta zauna da ita karta ringa bari tana tunanin saboda jininta idan ya dawo ze shigo, haka ya tafi office ya zauna aikin ma ya gagara yi kansa ciwo ya ke masa, shafa ya manta ma jiyan beci abinci ba seda Anwar yazo yake ce masa ko karyawa beyi ba ya fito saboda ya ce masa yana office sannan suka fita tare sukaje cin abinci.
Suna dabda komawa Kiran Baba Abu ya shiga wayarsa, seda gabansa ya fadi ya daga da sallama kamar yanda yayi tunani kuwa ko amsa masa beyi ba ya dira fada ta inda ya shiga ba tanan yake fita ba fadi yake
"Ibrahim wace irin shaidaniya kake zaune da ita a matsayin Matane yanzu ace rashin tarbiyyar yarinyar nan har ya kai ta kalli idon uwarka ta kirata munafuka saboda ta shahara a rashin mutunchi? Wallahi badan dattijantaka irin ta uban ta ba da nace ka sakar musu ita kowa ya huta amma iyayenta mutanen kirki ne, Jarabawa ce da kowanne bawa baya rabo da kalar tasa Allah ya basu wannan yarinya amma dukda haka ba zamu zuba mata ido ta tinga iskanci yanda taga dama a rasa me taka mata burki ba, ina dai akan kiahiya take wannan diban Albarkar ko to kuwa aure babu fashi, da na cewa Hajiyar se qarshen wata zamuje toh na fasa, yanzu zan kira Alhaji Garba da Sabi'u da Imrana tunda dasu zamuje na gaya musu duk su shirya Juma'ar nan mu tafi mu kwana a can Asabar mu juyo, seka shirya dan tare zamuje dakai gu ganka ko ka gaida surukan naka amma wannan mata taka dole ka tashi tsaye ka dauki mataki a kanta, idan ta kama kasa ayita sauke mata qur'ani in makarai ne a kanta masu son tada husuma duk ayi maganinta".
Shidai har Baba Abu ya gama banbaminsa bece komai ba seda yayi shiru kafin yace masa toh, Allah ya kaimu Juma'ar kwanaki uku harda ranar masu zuwa kenan dan suna Talata. Yana gama wayar Anwar da yaji kusan rabin maganar ya kalleshi fuska a sake yace
"Ango kace uwargida tayi bore ta sakw ballowa kanta ruwa to Allah ya fitar da ita"
"Hmm" kawai Khalil yace masa ya wuce Office dinsa zuciyarsa duk babu dadi. Ana cikin wannan halin wane Jalingo zasu tafi kuma itama Jalilah tana da matsala wani lojacin akan me zataje ta gayawa Baba Abu yanzu daya gayawa Hajiya Mansura Matarsa ya tabbata yanzu dangi duk se sunji labari su qara sakata a gaba.
Bayan sun fito sallar Azahar ya duba wayarsa yaga Humaira ta tura masa da saqon ban haquri, murmushi yayi ya kirata tana dagawa ta fasa masa kuka, Khalil ya dafe kansa da daman a cike yake da damuwar Umaimah yace
"Me kuma ya faru?"
"Ba kaine kake fushi dani ba"
"Ni ba fushi nakeyi dake ba tun jiyan nima bana jin dadi shiyasa ban kiraki ba ki dena kukan". Seda yayi aikin rarrashi kafin ta haqura, Humaira akwai shagwaba ya fahimci ma da gayya take masa dan ya rarrasheta shi kuma baya gajiya da lallashin nata dan abin nata burgeshi yakeyi.
"Kina ina naji surutan yara?" Ya tambayeta jin yara na hayaniya a kusa da ita se tace masa
"Ina gidan Anty Unaiza, jiya da daddare da taje Mama tace na bita wai na koma gidan da zama yanzu" ta bashi amsa, se ya bude ido yace
"Toh, me yasa?"
"Nima ban sani ba amma inaga saboda Noor ne dan jiya bayan ka tafi yazo yanata Hayaniya har seda ma sukayi fada da Yaya Habibu, ni tausayi ma ya bani wlh kamar nayi kuka kuma be samu Army dinma bafa wannan karon shiyasa abun yayi masa yawa".
Gimtse fuska Khalil yayi kamar yana gabanta yace
"Oh to tunda ya baki tausayi ai da se kicewa maman ta aura miki shi kawai a haka ko bashida abinyi zaki zauna dashi ko"
"Auw" Humaira ta fada tana riqe baki, Unaizatu data tarar da katobarar da takeyi ta dana mata duka a cinya ta shiga sosawa tana cewa
"Nifa ba haka nake nufi ba, bayan kazo kayi mun Asiri ka rabani da saurayina tun ina yar yarinya" tayi maganar tana zumbura baki se Khalil ya saki murmushin da be shirya ba yace
"Oh Asiri ma nayi miki lallai yarinyar nan wai yaushe bakinki ya bude kika fara magana haka?"
"Oho nima ban sani ba" ta bashi amsa cikin qunquni se ya saki qaramar dariya yace
"Idan na tashi zanzo na ganki, har yanzu a Gandu Unaizatu take ko sun chanza gida?"
"Eh sun chanza amma duk a unguwar ne amma ta layin bayan wancan gidan suka koma"
"Asalin gidan iyayen Mijinta kenan ko? Idan zan tuna sanda ta haifi Danta na farko a can ta zauna Mama tana aiken mu mu kai mata saqo"
"Eh nan" ta fada cikin tabbatarwa se yace mata
"Toh shikenan, zan zo idan nazo layin sena kiraki dan qila an chanzawa gidan fasali bazan gane ba"
"Toh shikenab se kazo"
"Alright babe" ya fada tareda yin shiru amma be kashe wayar ba, kamar daga sama yaji tace
"I love you take care" ko numfashi be aje ba ta kashe wayar shi kadai ya fashe da dariya a ransa ko yanda kasan ta wanke shi da Hypo, wayaga yaushe rabon duniya da Ayyaraye ace masa I Love you tun farkon tarewarsu a sabon gida.
Haka ta ringa lallabata tana sake tabbatar mata da ta kwantar da hankalinta tasan aikin Malam zeci kawai haquri zata koya da danne zuciya nadan lokaci kafin Ludayinta ya hau kan Dawo seda taga ta dan nutsu kafin sukayi sallama akan gobe ita Safinan zataje gurin Malam taji koda abinda ze qara bata tunda ita Umaimah ta kafe bazata koma ba kuma se an biyata kudinta. A nan inda suka gama waya da Safina baccin wahala yayi gaba da ita, bata farka ba se uku da motsi na dare shima wata Azababbiyar Yunwa ce ta tada ta se a sannan tayi sallar Magriba da Ishar da batayi ba.
KHALIL
Tunda ya samu ya haye Sama ba tareda sun sake haduwa da Umaimah ba be sakko ba, yana so yaje gurin Hajiya amma besan me zece mata ba. Matarsa ta zageta ta kirata munafuka amma ya kasa yin komai to da wanne ido ze kalli Hajiyar?
Haka ya kwana saqa da warwara akan abinda ya kamata yayi, wani sashe na zuciyarsa yana ganin beyiwa Humaira Adalci ba da yake shirin janyota cikin wannan rayuwar da yake a ciki inda wani bangare yake tabbatar masa da ita ce warakarsa, za kuma ta fiddashi daga duk wani qunci da damuwa da yake ciki ta maye masa da tarin farinciki da ya dade yana mafarkin samu idan Umaimah ta barsu kenan.
Tunanin raba musu gida ya fado masa yana ganin hakan shine ze kawo masa sauqin da kuma kwanciyar hankali idan ya zamana kowacce tana muhallinta na daban ba kamar yanda Su Jalilah suke fadin ya ajiye Humaira a nan separate part dinsa na Sama da Umaimah ta hanashi amfani dashi hasashenta ya tabbata kenan daman da tace dan wata ya gina gaskiya baya zaton haka zata yuwuwu gara ya gyara tsohon gidansu da suka taso ya ajiye Humairan a can yafi musu kwanciyar hankali daga shi har ita. Yana gama tunanin ya miqe ya dakko Laptop dinsa, seda ya duba lokaci sha biyu ta gota kafin ya bude ya shiga binciko proposal design din dayayi ze maida ginin dan da yayi niyyar ya gyara shi ne ya siyar amma yanzu zeyi masa amfani. Zanen ya duba ya dakko takadda da biro ya shiga lissafin abinda yake ganin ze kashe da tsahon lokacin da ze dauka kafin ya kammalu, a nasa lissafin idan yayi sauri yana ganin ze gama a wata uku in kuma yaja lokaci wata biyar zuwa shida, akan wata shidan ya bari ze gayawa su Baba Abu idan sunje neman auran su saka rana wata shidan zuwa sannan yasan hatta ita Umaiman tayi duk abinda zatayi ta saduda shikenan.
Washe gari bakwai bata qarasa ba ya bar gidan, a waya ya kira Hajiya yayi mata qaryar ya tafi Rano, yanda batayi masa maganar jiya ha shima beyi ba illah ce masa da tayi Jalilah ta kawo kaya jiya idan ya dawo ya shiga ya gani yace mata toh gaba daya beji dadi ba saboda yanda yaji muryarta yasan abinda Umaiman tayi mata ya doketa sosai kawai dai ta shanye ne bata nuna ba. Seda ya kira Habiba ta tabbatar masa Hajiyar na lafiya kawai dai magana ce bata cikayi ba tun jiyan se ta zauna tayi shiru yace mata ta zauna da ita karta ringa bari tana tunanin saboda jininta idan ya dawo ze shigo, haka ya tafi office ya zauna aikin ma ya gagara yi kansa ciwo ya ke masa, shafa ya manta ma jiyan beci abinci ba seda Anwar yazo yake ce masa ko karyawa beyi ba ya fito saboda ya ce masa yana office sannan suka fita tare sukaje cin abinci.
Suna dabda komawa Kiran Baba Abu ya shiga wayarsa, seda gabansa ya fadi ya daga da sallama kamar yanda yayi tunani kuwa ko amsa masa beyi ba ya dira fada ta inda ya shiga ba tanan yake fita ba fadi yake
"Ibrahim wace irin shaidaniya kake zaune da ita a matsayin Matane yanzu ace rashin tarbiyyar yarinyar nan har ya kai ta kalli idon uwarka ta kirata munafuka saboda ta shahara a rashin mutunchi? Wallahi badan dattijantaka irin ta uban ta ba da nace ka sakar musu ita kowa ya huta amma iyayenta mutanen kirki ne, Jarabawa ce da kowanne bawa baya rabo da kalar tasa Allah ya basu wannan yarinya amma dukda haka ba zamu zuba mata ido ta tinga iskanci yanda taga dama a rasa me taka mata burki ba, ina dai akan kiahiya take wannan diban Albarkar ko to kuwa aure babu fashi, da na cewa Hajiyar se qarshen wata zamuje toh na fasa, yanzu zan kira Alhaji Garba da Sabi'u da Imrana tunda dasu zamuje na gaya musu duk su shirya Juma'ar nan mu tafi mu kwana a can Asabar mu juyo, seka shirya dan tare zamuje dakai gu ganka ko ka gaida surukan naka amma wannan mata taka dole ka tashi tsaye ka dauki mataki a kanta, idan ta kama kasa ayita sauke mata qur'ani in makarai ne a kanta masu son tada husuma duk ayi maganinta".
Shidai har Baba Abu ya gama banbaminsa bece komai ba seda yayi shiru kafin yace masa toh, Allah ya kaimu Juma'ar kwanaki uku harda ranar masu zuwa kenan dan suna Talata. Yana gama wayar Anwar da yaji kusan rabin maganar ya kalleshi fuska a sake yace
"Ango kace uwargida tayi bore ta sakw ballowa kanta ruwa to Allah ya fitar da ita"
"Hmm" kawai Khalil yace masa ya wuce Office dinsa zuciyarsa duk babu dadi. Ana cikin wannan halin wane Jalingo zasu tafi kuma itama Jalilah tana da matsala wani lojacin akan me zataje ta gayawa Baba Abu yanzu daya gayawa Hajiya Mansura Matarsa ya tabbata yanzu dangi duk se sunji labari su qara sakata a gaba.
Bayan sun fito sallar Azahar ya duba wayarsa yaga Humaira ta tura masa da saqon ban haquri, murmushi yayi ya kirata tana dagawa ta fasa masa kuka, Khalil ya dafe kansa da daman a cike yake da damuwar Umaimah yace
"Me kuma ya faru?"
"Ba kaine kake fushi dani ba"
"Ni ba fushi nakeyi dake ba tun jiyan nima bana jin dadi shiyasa ban kiraki ba ki dena kukan". Seda yayi aikin rarrashi kafin ta haqura, Humaira akwai shagwaba ya fahimci ma da gayya take masa dan ya rarrasheta shi kuma baya gajiya da lallashin nata dan abin nata burgeshi yakeyi.
"Kina ina naji surutan yara?" Ya tambayeta jin yara na hayaniya a kusa da ita se tace masa
"Ina gidan Anty Unaiza, jiya da daddare da taje Mama tace na bita wai na koma gidan da zama yanzu" ta bashi amsa, se ya bude ido yace
"Toh, me yasa?"
"Nima ban sani ba amma inaga saboda Noor ne dan jiya bayan ka tafi yazo yanata Hayaniya har seda ma sukayi fada da Yaya Habibu, ni tausayi ma ya bani wlh kamar nayi kuka kuma be samu Army dinma bafa wannan karon shiyasa abun yayi masa yawa".
Gimtse fuska Khalil yayi kamar yana gabanta yace
"Oh to tunda ya baki tausayi ai da se kicewa maman ta aura miki shi kawai a haka ko bashida abinyi zaki zauna dashi ko"
"Auw" Humaira ta fada tana riqe baki, Unaizatu data tarar da katobarar da takeyi ta dana mata duka a cinya ta shiga sosawa tana cewa
"Nifa ba haka nake nufi ba, bayan kazo kayi mun Asiri ka rabani da saurayina tun ina yar yarinya" tayi maganar tana zumbura baki se Khalil ya saki murmushin da be shirya ba yace
"Oh Asiri ma nayi miki lallai yarinyar nan wai yaushe bakinki ya bude kika fara magana haka?"
"Oho nima ban sani ba" ta bashi amsa cikin qunquni se ya saki qaramar dariya yace
"Idan na tashi zanzo na ganki, har yanzu a Gandu Unaizatu take ko sun chanza gida?"
"Eh sun chanza amma duk a unguwar ne amma ta layin bayan wancan gidan suka koma"
"Asalin gidan iyayen Mijinta kenan ko? Idan zan tuna sanda ta haifi Danta na farko a can ta zauna Mama tana aiken mu mu kai mata saqo"
"Eh nan" ta fada cikin tabbatarwa se yace mata
"Toh shikenan, zan zo idan nazo layin sena kiraki dan qila an chanzawa gidan fasali bazan gane ba"
"Toh shikenab se kazo"
"Alright babe" ya fada tareda yin shiru amma be kashe wayar ba, kamar daga sama yaji tace
"I love you take care" ko numfashi be aje ba ta kashe wayar shi kadai ya fashe da dariya a ransa ko yanda kasan ta wanke shi da Hypo, wayaga yaushe rabon duniya da Ayyaraye ace masa I Love you tun farkon tarewarsu a sabon gida.