Sashe 185
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hakan kuwa akayi Anwar ya kira ya bashi uzurin bashi da lafiya yayi duk abinda ya kamata, a nan bangaren Hajiya ya wuni daman Itama Umaimah tara bata cika ba ta bar gidan. Sanda Jalilah tazo haka ta sakashi gaba seda suka bude kayan, ya ringa mamakin yanda ta zabo kaya haka kuma Undies da dogayen riguna duk yana tunanin zasuyiwa Humairan se ya kalleta yace
"Wai ya akayi kika san size din yarinyar ne?"
"Kai dai ka zauna anan ai wlh tunda na saka raina akan se kayi auran nan babu abinda bazanyi akai ba, ni yanzu muyi maganar kudi itace a gabana na samu na sallami masu kaya"
"Ai tunda kika siyo bakiyi shawara dani ba se kiyita Addu'a har sanda zan samu kudi na biyaki dan ni banyi lissafin wani lefe a yanzu ba.
Se bayan Isha Umaimah ta dawo gidan yana zaune a compound yana waya da Humaira ta wuce shi ba tareda tayi masa kallo biyu ba. Seda ya gama wayarsa tsaf sannan ya shiga gidan, haka nan yake ji shakkarta ta ragu a zuciyarsa tana zaune a falo tana waya ya haye sama warin Tazargaden da Jalilah ta saka masa duk ya cika gurin dole ya sake bude windows ya kunna Ac. Tunda Hajiya ta labar ta mata abinda ya faru da safen tayi tsalle ta dire akan Umaimah ce
"Toh Hajiya a ina zeje ya shaqo wani abu in ba a gidan sa ba wannan matar tasa fa ta zarce duk yanda kike tunaninta a banza zata dauke wuta haka kema kinsan canza salo tayi ta koma yaqin ta qarqashin qasa kuma ta Allah ba tata ba, ina kowa zan gayawa Abban Sadiq ya hada masa magungunan karya sammu dana tsarin jiki daman ya fara hada naki in Allah ya yarda duk mugun abunta sedai ya koma kanta" haka ta kwashi tazargaden taje ta turara Hajiya na hanata amma taqi ji sa'a daya Umaiman bata nan da Allah kadai yasan yanda za'a kwashe.
Seda ya feffesa freshener kafin ya sake sauka qasan, bata falon ya zauna dan yasan zata fito so yakeyi ya gaya mata zancen tafiyarsa jibi yana nan zauna ta fito tana tura ciki se yamutsa fuska takeyi bata ko kalli inda yake ba ta zauna a qasa tana kiran Ruqayya.
"Idan Allah ya kaimu ranar Friday zamuyi tafiya dasu Baba Abu zamu iya dawowa Saturday ko Sunday ya danganta da yanda muka gama abinda ya kaimu" ya fada a sanyaye qirjinsa na bugawa. Be zata zata kula shi ba se kuma yaji tace
"Ina zaku je?"
"Jalingo" ya bata amsa zuciyarsa kamar ana kodan kwarya dan seda ya fada yayi dana sanin fadar idan kuma tasan garinsu Humairan fa ya sake kunno wata wutar da ze kasa kashewa. Zaman jiran yaji ko zata sake magana yayi amma har Ruqayya ta kawo mata abinci ta shiga cin abinta bata kulashi ba se ya miqe yana sauke ajiyar zuciya yace
"Zan tura miki da saqo ta account" kamar da dutse yake magana haka ta masa banza, ya wuce sama yana sauke Ajiyar zuciya, Umaimah ta bishi da wani matsiyacin kallo kafin taja tsaki a fili tace
"Se inga da qafar da zakaje Jalingon ai Mtsw" ta sake jan tsaki taci gaba da cin abincinta. Seda ta gama tsaf kafin ta koma dakin ta dakko yar robar da Malam ya sake aiko mata da ita bayan ya kira shida kansa ya sanarwa da Safina zancen tafiya neman auran dasu Khalik din zasuyi. A corridor ta tsaya inda yake ajiye takalmin da yake zuwa sallar asuba dashi ta saka leda a hannunta ta debi man dake cikin robar zuciyarta ta rigada ta qeqashe biyan buqata kawai take nema babu bata lokaci ta shafe duka takalman qafa biyu da yake zuwa salla dasu tunda bata san wanda ze saka ba. A sharar waje taje ta yarda ledar da robar maganin ta wanke hannunta tasa kafin ta koma daki ta kwanta, seda ta turawa da Safina saqo a WhatsApp cewar tayi seta maido mata da cewa
"Yawwa qawata, kedai ki ci gaba da jurewa ranar biyan buqata ai rai ba a bakin komai yake ba in Allah ya yarda mune da nasara.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 67
KHALIL
Cikin ikon Allah a daren yayi bacci me dadi wanda har ya iya tashi yayi sallah raka'a hudu kamar yanda ya sabayi a kowanne dare, da yake dab da Asuba ya farka bayan ya idar da sallar be koma bacci ba, Lazumi ya ci gaba dayi har akayi kiran farko kafin ya tashi ya shiga wanka yayi shirin masallaci bayan ya cire kayan da ze saka da sauran abinda zeyi amfani dasu saboda da wuri yake so ya fita, jiya beje office ba kuma akwai abubuwan daya kamata ace yayi dukda Anwar yana nan. A masallaci Baba Musa daya ganshi yake cewa
"Madallah kace jiki yayi kyau gashi yau ka fito da wuri yanda ka saba, toh Allah ya qara kikayewa. Ka nemi ganyan magarya masu kyau ka zuba a ruwa ka tofa Ayoyin nan na karya sihiri kayita sha kana shafe jinka sannan koda yaushe bakinka karya yi shiru daga ambaton Allah duk abinda kake yi ka ringa Istigfari kana hailala kaga Istigfari waraka ne daga duk wata damuwa sannan karka ringa rabo da Karanta Lahaula, ka kuma ringa tofata qafa dari a ruwa kullum kaida Yayanka da Iyalinka kusha ku shafe jikinku duk abin maqiyi sedai yayi amma baze same ku ba da yardar Allah".
Godiya yayiwa Baban suka rabu bayan an idar da sallah ya shiga gida.
Yana tsaye yana saka kaya haka kawai yaji qafarsa ta sage kamar wanda ya taka qanqara, zama yayi akan gado yana duba qafar, shidai baya tunanin yaji ciwo ko ya buge da wani abu a kwanakin nan kuma ko dogon tuqi beyi ba qarqarinsa daga gida ne yaje office idan ma zasu fita site yawanci Anwar ne yake tuqasu. Haka ya qarasa shirin ya fito, dakyar ya iya sauka daga benen ya zauna a falon qasan yana maida numfashi. Takalmin daya saka ya cire hada da safar yana sake duba qafar. Yafi minti goma a zaunen, jin an bude qofa ya sakashi daga kai ya kalli gurin, Umaimah ce tayi masa kallo daya ta nufi hanyar kitchen bata dade ba ta fito da cup a hannunta ta sake wuce shi ta shiga daki.
Haka ya ringa takawa dakyar ya fice daga gidan ya shiga bangaren Hajiya.
"Babana lafiya kake dogara qafa kamar me karaya?" Hajiya ta fada tana kallonsa ganin yanda yake tafiya kamar wani Saqago. Seda ya zauna yana cije baki saboda yanda yake jin qafafun nasa kafin ya shiga gaisheta ta amsa tana cewa
"Me kuma ya samu qafar?"
"Nima ban sani ba Hajiya, ina dawowa daga Masallaci naji ta riqe mun kuma abin qaruwa yakeyi, ba ciwo take mun kawai qashin ya riqe tun daga guiwata har zuwa tafin qafar" ya bawa Hajiyar amsa seta matsa kusa dashi tana duba qafar tace
"Ikon Allah sanyi ne toh, shiyasa nake yawan maka maganar Ac da baka rabo da ita gida da Office irin wannan sanyin qashin nake gudar maka wani baya tashi tambayarka se girma yazo musamman ku da daman kuna da Gadonsa kana kallo Mahaifinku harya rasu yana yana fama da ciwon qafa toh Allah ya taqaita, bari na dakko man zafi na shafa maka ko zata saki in yaso kaje Asibiti su baka magani daga baya".
Sama ta wuce ta dawo da qananan robobi na Man Mainasara da kuma kwalbar Aboniki, da kanta ta shafe masa qafafun tun daga guiwar har tafin qafa. Seda ya karya a bangaren Hajiyar kafin ya fita zuwa sannan qafar ta saki dukda ba gaba daya ba haka ya wuce office. A can dinma aikin yana yi yana hutawa saboda yanda qafar take riqewa se kuma ta saki. Rigima Humaira ta saka masa akan tanason ta ganshi kamar ba jiya yaje gurinta ba, babu yanda ya iya haka ya biya Gidan Unaizatu bayan ya tashi aiki. Be shiga ciki ba a qofar gida suka tsaya. Cikin kulawa Humaira ta kalleshi ganin yanda yake cije baki yana canza tsayuwa tace
"Yah Khalil meya sami qafarka naga ka kasa tsayuwa da kyau?"
"Babu komai dan ciwo takeyi mun amma yanzu idan na tafi daga nan zan biya naga Likita inaga nayi over working kaina ne shi yasa nake ta jin babu dadi a jikina" ya bata amsa seta sake narke fuska kamar zatayi masa kuka tace
"Wayyo sannu Allah ya baka lafiya, ciwon qafa babu dadin ina gani idanya tasarwa Mama ko bacci bata iyayi amma idan na tofa mata Fatiha se kaga ta dan samu sauqin ciwon kaima idan kaje gida kacewa Anty Umaimah ta tofa maka".
Kallon ta yakeyi har ta kai qarshe yayi dan murmushi yace
"Ashe kin san sunan matata amma shine kullum kika tashi magana sedai naji kince Matarka?"
Tura baki tayi ta kalli gefe ba tareda ta tanka masa ba ya sakeyin murmushin qarfin hali dan sosai qafar ta matsa masa ya ce mata
"Bari naje Baby, zamuyi waya idan na isa gida kinji" seta daga masa kai tace
"Toh, Allah ya qara sauqi yanzu a haka kuma gobe zakayi doguwar tafiya?"
Shaf ya manta ma da wai gobe zasuyi tafiya, se ya sake yi mata murmushi yace
"Eh mana ko bakya so naje?"
"Aa kaga fa qafarka na ciwo ka bari kawai se next week se kuje saboda zaman mota fa da wahala ko baka ciwon qafa daga nan zuwa Jalingo se kaji jiki ballantana kuma kana fama da qafa"
"Wai ya akayi kika san size din yarinyar ne?"
"Kai dai ka zauna anan ai wlh tunda na saka raina akan se kayi auran nan babu abinda bazanyi akai ba, ni yanzu muyi maganar kudi itace a gabana na samu na sallami masu kaya"
"Ai tunda kika siyo bakiyi shawara dani ba se kiyita Addu'a har sanda zan samu kudi na biyaki dan ni banyi lissafin wani lefe a yanzu ba.
Se bayan Isha Umaimah ta dawo gidan yana zaune a compound yana waya da Humaira ta wuce shi ba tareda tayi masa kallo biyu ba. Seda ya gama wayarsa tsaf sannan ya shiga gidan, haka nan yake ji shakkarta ta ragu a zuciyarsa tana zaune a falo tana waya ya haye sama warin Tazargaden da Jalilah ta saka masa duk ya cika gurin dole ya sake bude windows ya kunna Ac. Tunda Hajiya ta labar ta mata abinda ya faru da safen tayi tsalle ta dire akan Umaimah ce
"Toh Hajiya a ina zeje ya shaqo wani abu in ba a gidan sa ba wannan matar tasa fa ta zarce duk yanda kike tunaninta a banza zata dauke wuta haka kema kinsan canza salo tayi ta koma yaqin ta qarqashin qasa kuma ta Allah ba tata ba, ina kowa zan gayawa Abban Sadiq ya hada masa magungunan karya sammu dana tsarin jiki daman ya fara hada naki in Allah ya yarda duk mugun abunta sedai ya koma kanta" haka ta kwashi tazargaden taje ta turara Hajiya na hanata amma taqi ji sa'a daya Umaiman bata nan da Allah kadai yasan yanda za'a kwashe.
Seda ya feffesa freshener kafin ya sake sauka qasan, bata falon ya zauna dan yasan zata fito so yakeyi ya gaya mata zancen tafiyarsa jibi yana nan zauna ta fito tana tura ciki se yamutsa fuska takeyi bata ko kalli inda yake ba ta zauna a qasa tana kiran Ruqayya.
"Idan Allah ya kaimu ranar Friday zamuyi tafiya dasu Baba Abu zamu iya dawowa Saturday ko Sunday ya danganta da yanda muka gama abinda ya kaimu" ya fada a sanyaye qirjinsa na bugawa. Be zata zata kula shi ba se kuma yaji tace
"Ina zaku je?"
"Jalingo" ya bata amsa zuciyarsa kamar ana kodan kwarya dan seda ya fada yayi dana sanin fadar idan kuma tasan garinsu Humairan fa ya sake kunno wata wutar da ze kasa kashewa. Zaman jiran yaji ko zata sake magana yayi amma har Ruqayya ta kawo mata abinci ta shiga cin abinta bata kulashi ba se ya miqe yana sauke ajiyar zuciya yace
"Zan tura miki da saqo ta account" kamar da dutse yake magana haka ta masa banza, ya wuce sama yana sauke Ajiyar zuciya, Umaimah ta bishi da wani matsiyacin kallo kafin taja tsaki a fili tace
"Se inga da qafar da zakaje Jalingon ai Mtsw" ta sake jan tsaki taci gaba da cin abincinta. Seda ta gama tsaf kafin ta koma dakin ta dakko yar robar da Malam ya sake aiko mata da ita bayan ya kira shida kansa ya sanarwa da Safina zancen tafiya neman auran dasu Khalik din zasuyi. A corridor ta tsaya inda yake ajiye takalmin da yake zuwa sallar asuba dashi ta saka leda a hannunta ta debi man dake cikin robar zuciyarta ta rigada ta qeqashe biyan buqata kawai take nema babu bata lokaci ta shafe duka takalman qafa biyu da yake zuwa salla dasu tunda bata san wanda ze saka ba. A sharar waje taje ta yarda ledar da robar maganin ta wanke hannunta tasa kafin ta koma daki ta kwanta, seda ta turawa da Safina saqo a WhatsApp cewar tayi seta maido mata da cewa
"Yawwa qawata, kedai ki ci gaba da jurewa ranar biyan buqata ai rai ba a bakin komai yake ba in Allah ya yarda mune da nasara.
*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼
Page 67
KHALIL
Cikin ikon Allah a daren yayi bacci me dadi wanda har ya iya tashi yayi sallah raka'a hudu kamar yanda ya sabayi a kowanne dare, da yake dab da Asuba ya farka bayan ya idar da sallar be koma bacci ba, Lazumi ya ci gaba dayi har akayi kiran farko kafin ya tashi ya shiga wanka yayi shirin masallaci bayan ya cire kayan da ze saka da sauran abinda zeyi amfani dasu saboda da wuri yake so ya fita, jiya beje office ba kuma akwai abubuwan daya kamata ace yayi dukda Anwar yana nan. A masallaci Baba Musa daya ganshi yake cewa
"Madallah kace jiki yayi kyau gashi yau ka fito da wuri yanda ka saba, toh Allah ya qara kikayewa. Ka nemi ganyan magarya masu kyau ka zuba a ruwa ka tofa Ayoyin nan na karya sihiri kayita sha kana shafe jinka sannan koda yaushe bakinka karya yi shiru daga ambaton Allah duk abinda kake yi ka ringa Istigfari kana hailala kaga Istigfari waraka ne daga duk wata damuwa sannan karka ringa rabo da Karanta Lahaula, ka kuma ringa tofata qafa dari a ruwa kullum kaida Yayanka da Iyalinka kusha ku shafe jikinku duk abin maqiyi sedai yayi amma baze same ku ba da yardar Allah".
Godiya yayiwa Baban suka rabu bayan an idar da sallah ya shiga gida.
Yana tsaye yana saka kaya haka kawai yaji qafarsa ta sage kamar wanda ya taka qanqara, zama yayi akan gado yana duba qafar, shidai baya tunanin yaji ciwo ko ya buge da wani abu a kwanakin nan kuma ko dogon tuqi beyi ba qarqarinsa daga gida ne yaje office idan ma zasu fita site yawanci Anwar ne yake tuqasu. Haka ya qarasa shirin ya fito, dakyar ya iya sauka daga benen ya zauna a falon qasan yana maida numfashi. Takalmin daya saka ya cire hada da safar yana sake duba qafar. Yafi minti goma a zaunen, jin an bude qofa ya sakashi daga kai ya kalli gurin, Umaimah ce tayi masa kallo daya ta nufi hanyar kitchen bata dade ba ta fito da cup a hannunta ta sake wuce shi ta shiga daki.
Haka ya ringa takawa dakyar ya fice daga gidan ya shiga bangaren Hajiya.
"Babana lafiya kake dogara qafa kamar me karaya?" Hajiya ta fada tana kallonsa ganin yanda yake tafiya kamar wani Saqago. Seda ya zauna yana cije baki saboda yanda yake jin qafafun nasa kafin ya shiga gaisheta ta amsa tana cewa
"Me kuma ya samu qafar?"
"Nima ban sani ba Hajiya, ina dawowa daga Masallaci naji ta riqe mun kuma abin qaruwa yakeyi, ba ciwo take mun kawai qashin ya riqe tun daga guiwata har zuwa tafin qafar" ya bawa Hajiyar amsa seta matsa kusa dashi tana duba qafar tace
"Ikon Allah sanyi ne toh, shiyasa nake yawan maka maganar Ac da baka rabo da ita gida da Office irin wannan sanyin qashin nake gudar maka wani baya tashi tambayarka se girma yazo musamman ku da daman kuna da Gadonsa kana kallo Mahaifinku harya rasu yana yana fama da ciwon qafa toh Allah ya taqaita, bari na dakko man zafi na shafa maka ko zata saki in yaso kaje Asibiti su baka magani daga baya".
Sama ta wuce ta dawo da qananan robobi na Man Mainasara da kuma kwalbar Aboniki, da kanta ta shafe masa qafafun tun daga guiwar har tafin qafa. Seda ya karya a bangaren Hajiyar kafin ya fita zuwa sannan qafar ta saki dukda ba gaba daya ba haka ya wuce office. A can dinma aikin yana yi yana hutawa saboda yanda qafar take riqewa se kuma ta saki. Rigima Humaira ta saka masa akan tanason ta ganshi kamar ba jiya yaje gurinta ba, babu yanda ya iya haka ya biya Gidan Unaizatu bayan ya tashi aiki. Be shiga ciki ba a qofar gida suka tsaya. Cikin kulawa Humaira ta kalleshi ganin yanda yake cije baki yana canza tsayuwa tace
"Yah Khalil meya sami qafarka naga ka kasa tsayuwa da kyau?"
"Babu komai dan ciwo takeyi mun amma yanzu idan na tafi daga nan zan biya naga Likita inaga nayi over working kaina ne shi yasa nake ta jin babu dadi a jikina" ya bata amsa seta sake narke fuska kamar zatayi masa kuka tace
"Wayyo sannu Allah ya baka lafiya, ciwon qafa babu dadin ina gani idanya tasarwa Mama ko bacci bata iyayi amma idan na tofa mata Fatiha se kaga ta dan samu sauqin ciwon kaima idan kaje gida kacewa Anty Umaimah ta tofa maka".
Kallon ta yakeyi har ta kai qarshe yayi dan murmushi yace
"Ashe kin san sunan matata amma shine kullum kika tashi magana sedai naji kince Matarka?"
Tura baki tayi ta kalli gefe ba tareda ta tanka masa ba ya sakeyin murmushin qarfin hali dan sosai qafar ta matsa masa ya ce mata
"Bari naje Baby, zamuyi waya idan na isa gida kinji" seta daga masa kai tace
"Toh, Allah ya qara sauqi yanzu a haka kuma gobe zakayi doguwar tafiya?"
Shaf ya manta ma da wai gobe zasuyi tafiya, se ya sake yi mata murmushi yace
"Eh mana ko bakya so naje?"
"Aa kaga fa qafarka na ciwo ka bari kawai se next week se kuje saboda zaman mota fa da wahala ko baka ciwon qafa daga nan zuwa Jalingo se kaji jiki ballantana kuma kana fama da qafa"