Sashe 257
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Pillows da suka watso qasa ta shiga diba tana jefa masa tana kukan shagwaba, tunda ta dawo daga wankan Abid abubuwa suka qarasa warwarewa Khalil din ya dawo garau kamar wanda aka canzawa inji, tun tan jin dadin abin seda ta fara kuka tana neman mafaka dan kamar me biyan bashi haka ya ri ga gurzarta kullum babu daga qafa kamar abinci seda ta fara rama kafin ya tattara hankalinsa guri guda ya fara saurara mata, shikansa ya ringa mamakin inda ya samo wannan qarfin da Lafiyar amma ya danganta hakan harda tsoron rasata daya fara tunda har ta nuna qiri qiri ta gajiya da halin da yake ciki tofa shikenan rayuwa ta qara armashi, Humairan riritashi take kamar Gwal shi kuma yana kasheta da kalolin soyayyarsa masu tsayawa a rai. Sunyi kyau dasu da yayansu gidansu na cike da walwala a kullum cikin godewa Allah yake bisa ni'imar da yayi masa. Watan Abid din goma sha takwas ta haife yan biyu Mace da Namiji wanda basu san da cikinsu bama seda yayi wata kusan uku sannan, yasha daru da ita, dukda bata ce bata so ba amma kullum cikin kukan danta jariri ne ko yayeshi batayi ba ace ciki haka ya ringa lallabata da aka ce musu biyu ne nan ta sake rigimewa qarshe se Mama ce ta dauke mata Abid dinda cikin yayi wata bakwai saboda ta samu sauqin abubuwa haka kuwa akayo ta turawa har Allah ya rabasu lafiya aka cire mata Hauwa (Jiddah) da Takwaran da yayiwa kansa suna ce masa Adil.
Yau din kwananta shida da dawowa daga wanka dan wannan karon ma gidan Mama ta koma bisa umarnin Hajiya Khalil kuwa ya ringa bala'i kamar ze ari baki saboda masifa akan me za'ace haihuwa ta uku ta tafi gida Hajiya tayi masa banza a cewarta lafiyar Humairan tafi komai ga aiki ga rainon yan biyu idan ta zauna a gidan fitinarsa kadai ba zata barta ta warke ba gara taje gida haka kuwa ya haqura qarshe ma ya qirqiri tafiyar dole ya bar qasar seda ya rage saura kwana uku ta dawo sannan shima ya dawo, tunda ta dawo din kuwa yake murzarta son ransa da sunan hukuncin yarda ta tafi gida da tayi, ita kuwa tadawo da shirin tarairayar mijinta dakyau, zata jurewa yanayinsa a kowanne hali ba zata gajiya ba.
Seda yayi dogon rarrashi kafin ya barta ya shiga wanka saboda buga qofa da akayi yan biyu na kuka. Ta shirya shi kuma ya shiga wanka, seda ya fito ya lura da lokacin daya bata qarfe goma yake so ya fita gashi har goman tayi da kusan minti ashirin. A gurguje ya shirya ko karyawa be tsaya ba ya fita saboda akwai baqin da zeyi kuma sha daya zasuzo shiyasa yaso fita tun goma ya sake duba takaddun da zeyi amfani dasu. Qarfe sha dayan daidai baqin suka iso, kai tsaye Conference room dinsu Anwar ya kaisu. Seda ya hada duk abinda zeyi amfani dashi kafin ya shiga, fuskarsa a washe ya shiga yi musu maraba yana kuma basu haqurin jiran da sukayi ya zauna akan kujerarsa idonsa ya sauka akan Umaimah data sunkuyar da kai da alama wani abu takeyi a wayarta take zuciyarsa ta buga har seda wayarsa ta subuce Anwar yayi saurin taro masa ita yana duba abinda Khalil din yake kallo da har yasa ya saki wayar be sani ba.
Seda yayi qoqarin tattara nutsuwarsa kafin ya zauna yana qoqarin kore abinda ya taso masa. Umaimah data gama turawa da sabon Bazawarin da tayi me suna Abdulwahab saqo danya kirata ne ta katse ta sanar masa sun fita wani uzuri idanta gama zata kira ta ajiye wayar bayan ta sakata a Silent kafin ta dago ganin dakin ya danyi duhu an kunna projecter karaf suka hada ido da Khalil da duk yanda yaso ya hana kansa kallonta ya kasa.
Jikinta ya dauki rawa zuciyarta ta ringa bugawa da sauri da sauri seta hade hannayenta biyu ta runtse idonta ji takeyi kamar ta tashi ta fice daga gurin, mamakin yanda ganinsa ya rudata haka ma ya kamata dan ba yau ne karon farko data ganshi ba bayan sun rabu, sun sha haduwa a gida a kusa kusa ma ba kamar yanzu da suke da tazarar gurin zama ba dukta ringaji mema yasa ta rako Hajiya Hudan. Aikin sabunta ginin Ma'aikatarsu za'ayi sun rubuta gwamnati ta sahale musu Hajiya Huda ce ta nemo musu Falcon Bridge construction company din a matsayin wadanda zasuyi musu aikin dan haka yau din tace tazo suje tareda wanda suke kula da bangaren kudi dan au qarasa qulla yarjejeniyar.
Har akaci aka cinye ba zatace ta gane abu daya da sukayi a gurin ba, muryar Anwar dake ta zuba bayani kawai takeji dan Khalil din shiya bawa takaddun ganin kamar Khalil din baya cikin nutsuwarsa yakashi karba kawai ba tareda yace wani abu ba ya jagoranci yarjejeniyar har aka gama suka saka hannu a takaddu Umaimah na ganin Hajiya Huda ta miqe itama ta miqe dan jinta takeyi kamar akan qaya, karo sukaci da Khalil da shima yake shirin fita tayi baya zata fadi ya tarota kafin ya saketa da sauri ya fice kamar wanda ya tuna wani abu.
A mota da Hajiya Huda ta tambayeta meya sameta ta birkice haka take ta fashe mata da kukan da take ta riqewa. Idan za'a saka mata wuqa ba zatace ga dalilin kukan ba, duk ta rikitasu, Aminu Sani daya daga cikin ma'aikatan da suka tafi tare, irin mutanen nan ne masu dan banzan surutu da saka ido, seya kalli Hajiyar yana gyara zama ya ce
"Hajiya kamar da sanayya tsakaninta da Shugaban kamfanin nan dan naga suna hada ido gaba dayansu suka rikice, shima bakiga a yanda ya fita ba? Hajiya Umaimah ko tsohon masoyi ne kun fitar da ran sake haduwa yau kuka gamu?"
Daga Umaiman har Hajiya Huda babu Wanda ya kulashi, ita tana cigaba da kuka qasa qasa ita kuma Hajiyar tunanin maganganunsa takeyi a zuciyarta tana tunanin to ko shine tsohon Mijin nata? Tabbas ta lura da yanda ya rasa nutsuwarsa ba kamar yanda ya shigo da farko ba kafin ya lura da Umaiman, irin kallon da ya ringayi mata duk tana ankare har ta ringa ayyana Allah sa tsuntsun soyayya ne ya dirar musu da kuwa Umaiman tayi Miji to amma yanzu ta gasgata maganar Aminu duk yanda akayi shine Mijinta da suka rabu inko hakane dole tayi kuka domin ya kai Mijin da wani ma ze maka takaicin rabuwa dashi balle ita da ta zauna tare dashi dan tasan shi sosai, Abokin qaninta ne tana jin labarin kirkinsa a gurinsa dan har akwai wata qanwarsu da qanin nata ya ringa cusa masa lokacin Khalil din yaqi yace shi yana son matarsa baze mata kishiya ba.
Da suka koma office din jiki a sabule ta dauki kayanta data bari bayan ta dauraye fuskarta ta gyara dukda haka idan ka kalleta seka san tayi kuka. Abdulwahab daya isheta da waya ya iso ze dauketa, Kyakykyawan Farin bafulatani Matashi ne da zasuyi sa'anni da Khalil ko ya dan girme shi da kadan. Ma'aikaci ne a hukumar yaqi da cin hanci da rashawa (EFCC) kusan Hadiza ce ta hadasu dan a office dinta suka fara haduwa yaje gurin itama Umaiman ranar taje suka gaisa har sukayi yar hira a gurin kafin suka rabu kwana biyu a tsakani Hadizan ta kirata tana sanar mata da cewar ya nemi number ta kuma ta bashi.
"Mutumin kirki ne Umaimah, na sanshi tunda dadewa munyi aiki tare yana da mata daya Khadija da yara hudu kuma ya tabbatar mun dagaske yakeyi idan kun daidaita kafin Azumi ma yake so ayi aure nan da wata hudu kenan. Dan Allah ki kwantar da hankalinki ki bashi dama, nasan harda rashin bude zuciyarki da bakiyi ba yasa duk cikin wadanda suke zuwa kika rasa wanda yayi miki amma nasan in kika bawa Abdul dama zaki ce na gaya miku, halayensa suna kamanceceniya dana Khalil zaki so shi a hankali kuma ki tsananta addu'a" Hadizan ta gaya mata. Badan taso ba kuna dan karta ga tayi rashin kyautawa dan ita bama tason farin Namini amma a haka ta fara kula Abdulwahab.
Se gashi cikin qasa da sati daya sabo ya fara shiga tsakaninsu kamar yanda Hadizan ta fada halayensa suna kamanceceniya dana Khalil, yana da matuqar kirki da sanyin hali ga shi ya iya kula da tarirayar mace. A sati dayan kullum se sunyi waya ya kuma sanar mata da duk wani abu daya kamat ace ta sani akansa hatta da hoton matarsa da yaransa ya tura mata, ya gaya mata Hadiza ta gaya masa komai akanta kuma ya gamsu dan haka shi da gaske yakeyi auranta yake so yayi kuma daya dawo Kano dan a Abuja yake aiki zezo kuma da yayi zuwa daya yana so na biyu ya zama iyayensa ne zasuje nema masa auranta.
Gaban Umaimah ya ringa dukan dari dari da cewa da yayi Hadiza ta gaya masa komai akanta. Tana so ta tambayeshi yasan komai harda mugun HALIN KISHInta amma ta gagara, tsoro takeyi karta tono abinda zesa shima ya gudu dan zuciyarta ta fara amincewa dashi amma ba zataso ace su qulla magana akan qarya ko kuskuren tunani ba. Zata so ace yasan komai akanta kamar yanda tasani akanshi sannan ya yarda ze zauna da ita a hakan tana tsoron kar yaji wani abu daga baya yasaka shi canza ra'ayi dan haka ta qudure duk in suka hadu ita da bakinta zata fayyace masa komai. Kafin yaji a bakin yan unguwar da suke kore mata maneman gara yaji gaskiya daga bakinta akan wannan shawarar ta tsaya.
Yau din kwananta shida da dawowa daga wanka dan wannan karon ma gidan Mama ta koma bisa umarnin Hajiya Khalil kuwa ya ringa bala'i kamar ze ari baki saboda masifa akan me za'ace haihuwa ta uku ta tafi gida Hajiya tayi masa banza a cewarta lafiyar Humairan tafi komai ga aiki ga rainon yan biyu idan ta zauna a gidan fitinarsa kadai ba zata barta ta warke ba gara taje gida haka kuwa ya haqura qarshe ma ya qirqiri tafiyar dole ya bar qasar seda ya rage saura kwana uku ta dawo sannan shima ya dawo, tunda ta dawo din kuwa yake murzarta son ransa da sunan hukuncin yarda ta tafi gida da tayi, ita kuwa tadawo da shirin tarairayar mijinta dakyau, zata jurewa yanayinsa a kowanne hali ba zata gajiya ba.
Seda yayi dogon rarrashi kafin ya barta ya shiga wanka saboda buga qofa da akayi yan biyu na kuka. Ta shirya shi kuma ya shiga wanka, seda ya fito ya lura da lokacin daya bata qarfe goma yake so ya fita gashi har goman tayi da kusan minti ashirin. A gurguje ya shirya ko karyawa be tsaya ba ya fita saboda akwai baqin da zeyi kuma sha daya zasuzo shiyasa yaso fita tun goma ya sake duba takaddun da zeyi amfani dasu. Qarfe sha dayan daidai baqin suka iso, kai tsaye Conference room dinsu Anwar ya kaisu. Seda ya hada duk abinda zeyi amfani dashi kafin ya shiga, fuskarsa a washe ya shiga yi musu maraba yana kuma basu haqurin jiran da sukayi ya zauna akan kujerarsa idonsa ya sauka akan Umaimah data sunkuyar da kai da alama wani abu takeyi a wayarta take zuciyarsa ta buga har seda wayarsa ta subuce Anwar yayi saurin taro masa ita yana duba abinda Khalil din yake kallo da har yasa ya saki wayar be sani ba.
Seda yayi qoqarin tattara nutsuwarsa kafin ya zauna yana qoqarin kore abinda ya taso masa. Umaimah data gama turawa da sabon Bazawarin da tayi me suna Abdulwahab saqo danya kirata ne ta katse ta sanar masa sun fita wani uzuri idanta gama zata kira ta ajiye wayar bayan ta sakata a Silent kafin ta dago ganin dakin ya danyi duhu an kunna projecter karaf suka hada ido da Khalil da duk yanda yaso ya hana kansa kallonta ya kasa.
Jikinta ya dauki rawa zuciyarta ta ringa bugawa da sauri da sauri seta hade hannayenta biyu ta runtse idonta ji takeyi kamar ta tashi ta fice daga gurin, mamakin yanda ganinsa ya rudata haka ma ya kamata dan ba yau ne karon farko data ganshi ba bayan sun rabu, sun sha haduwa a gida a kusa kusa ma ba kamar yanzu da suke da tazarar gurin zama ba dukta ringaji mema yasa ta rako Hajiya Hudan. Aikin sabunta ginin Ma'aikatarsu za'ayi sun rubuta gwamnati ta sahale musu Hajiya Huda ce ta nemo musu Falcon Bridge construction company din a matsayin wadanda zasuyi musu aikin dan haka yau din tace tazo suje tareda wanda suke kula da bangaren kudi dan au qarasa qulla yarjejeniyar.
Har akaci aka cinye ba zatace ta gane abu daya da sukayi a gurin ba, muryar Anwar dake ta zuba bayani kawai takeji dan Khalil din shiya bawa takaddun ganin kamar Khalil din baya cikin nutsuwarsa yakashi karba kawai ba tareda yace wani abu ba ya jagoranci yarjejeniyar har aka gama suka saka hannu a takaddu Umaimah na ganin Hajiya Huda ta miqe itama ta miqe dan jinta takeyi kamar akan qaya, karo sukaci da Khalil da shima yake shirin fita tayi baya zata fadi ya tarota kafin ya saketa da sauri ya fice kamar wanda ya tuna wani abu.
A mota da Hajiya Huda ta tambayeta meya sameta ta birkice haka take ta fashe mata da kukan da take ta riqewa. Idan za'a saka mata wuqa ba zatace ga dalilin kukan ba, duk ta rikitasu, Aminu Sani daya daga cikin ma'aikatan da suka tafi tare, irin mutanen nan ne masu dan banzan surutu da saka ido, seya kalli Hajiyar yana gyara zama ya ce
"Hajiya kamar da sanayya tsakaninta da Shugaban kamfanin nan dan naga suna hada ido gaba dayansu suka rikice, shima bakiga a yanda ya fita ba? Hajiya Umaimah ko tsohon masoyi ne kun fitar da ran sake haduwa yau kuka gamu?"
Daga Umaiman har Hajiya Huda babu Wanda ya kulashi, ita tana cigaba da kuka qasa qasa ita kuma Hajiyar tunanin maganganunsa takeyi a zuciyarta tana tunanin to ko shine tsohon Mijin nata? Tabbas ta lura da yanda ya rasa nutsuwarsa ba kamar yanda ya shigo da farko ba kafin ya lura da Umaiman, irin kallon da ya ringayi mata duk tana ankare har ta ringa ayyana Allah sa tsuntsun soyayya ne ya dirar musu da kuwa Umaiman tayi Miji to amma yanzu ta gasgata maganar Aminu duk yanda akayi shine Mijinta da suka rabu inko hakane dole tayi kuka domin ya kai Mijin da wani ma ze maka takaicin rabuwa dashi balle ita da ta zauna tare dashi dan tasan shi sosai, Abokin qaninta ne tana jin labarin kirkinsa a gurinsa dan har akwai wata qanwarsu da qanin nata ya ringa cusa masa lokacin Khalil din yaqi yace shi yana son matarsa baze mata kishiya ba.
Da suka koma office din jiki a sabule ta dauki kayanta data bari bayan ta dauraye fuskarta ta gyara dukda haka idan ka kalleta seka san tayi kuka. Abdulwahab daya isheta da waya ya iso ze dauketa, Kyakykyawan Farin bafulatani Matashi ne da zasuyi sa'anni da Khalil ko ya dan girme shi da kadan. Ma'aikaci ne a hukumar yaqi da cin hanci da rashawa (EFCC) kusan Hadiza ce ta hadasu dan a office dinta suka fara haduwa yaje gurin itama Umaiman ranar taje suka gaisa har sukayi yar hira a gurin kafin suka rabu kwana biyu a tsakani Hadizan ta kirata tana sanar mata da cewar ya nemi number ta kuma ta bashi.
"Mutumin kirki ne Umaimah, na sanshi tunda dadewa munyi aiki tare yana da mata daya Khadija da yara hudu kuma ya tabbatar mun dagaske yakeyi idan kun daidaita kafin Azumi ma yake so ayi aure nan da wata hudu kenan. Dan Allah ki kwantar da hankalinki ki bashi dama, nasan harda rashin bude zuciyarki da bakiyi ba yasa duk cikin wadanda suke zuwa kika rasa wanda yayi miki amma nasan in kika bawa Abdul dama zaki ce na gaya miku, halayensa suna kamanceceniya dana Khalil zaki so shi a hankali kuma ki tsananta addu'a" Hadizan ta gaya mata. Badan taso ba kuna dan karta ga tayi rashin kyautawa dan ita bama tason farin Namini amma a haka ta fara kula Abdulwahab.
Se gashi cikin qasa da sati daya sabo ya fara shiga tsakaninsu kamar yanda Hadizan ta fada halayensa suna kamanceceniya dana Khalil, yana da matuqar kirki da sanyin hali ga shi ya iya kula da tarirayar mace. A sati dayan kullum se sunyi waya ya kuma sanar mata da duk wani abu daya kamat ace ta sani akansa hatta da hoton matarsa da yaransa ya tura mata, ya gaya mata Hadiza ta gaya masa komai akanta kuma ya gamsu dan haka shi da gaske yakeyi auranta yake so yayi kuma daya dawo Kano dan a Abuja yake aiki zezo kuma da yayi zuwa daya yana so na biyu ya zama iyayensa ne zasuje nema masa auranta.
Gaban Umaimah ya ringa dukan dari dari da cewa da yayi Hadiza ta gaya masa komai akanta. Tana so ta tambayeshi yasan komai harda mugun HALIN KISHInta amma ta gagara, tsoro takeyi karta tono abinda zesa shima ya gudu dan zuciyarta ta fara amincewa dashi amma ba zataso ace su qulla magana akan qarya ko kuskuren tunani ba. Zata so ace yasan komai akanta kamar yanda tasani akanshi sannan ya yarda ze zauna da ita a hakan tana tsoron kar yaji wani abu daga baya yasaka shi canza ra'ayi dan haka ta qudure duk in suka hadu ita da bakinta zata fayyace masa komai. Kafin yaji a bakin yan unguwar da suke kore mata maneman gara yaji gaskiya daga bakinta akan wannan shawarar ta tsaya.