← Book details Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 145 OF 267

Sashe 145

Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

[8/18, 9:52 PM] KYAUTA: *TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGE WA DA WANNAN SAIWOWIN ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*AKWAI MAGANIN SANYI SADIDAN*.
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY* .

*HALIN KISHI*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*WANNAN LITTAFIN KUDINE, KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*

*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SAI A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*A BIYA A KARANTA CIKIN SALAMA* 🙌🏼🙌🏼

Page 55

Kallonsa Baba Absullahi kawai Abba yakeyi baki bude saboda mamaki koda yake be kamata ma yayi mamakin ba sanin waye Baba Abdullahin ai daman shi Umaimah ta gado kuma da ace Mace ne shi daman Hassana da Hussaina zasu zama gurinjaye jayen bala'i kpda yake yanzun ma ya aka qare rigima ai se wadda ya manta ce baya janyowa kuma saboda halinsa sedai a haqura a barshi dan ko bashida gaskiya se ya san yanda ya ci galaba akanka.

Miqewar daya ga yana qoqarin yi ce tasa ya dakatar dashi dan har yana qoqarin hambarr da abincin da Anty ta kawo Abban yace
"Zauna Abdullahi, magana na kiraka muyi ba yawon tafiya gurin yan sanda ba".
Baba Abdullahi ya zauna Abba yaci gaba da cewa
"Nima a wannan gabar abinda ya faru beyimun dadi ba dan kaga ba'afi wata bafa nan ma suka yi wata rigimar har Asibiti ta kwanta dalilin daya sa Laure qanwar Malika take zama da ita yanzun kenan saboda anyi mata daurin Mahaifa kuma sukaqi fadar abinda ya hadasu daga shi har itan shiyasa ma ban tsaurara ba saboda nasan da tana da gaskiya zata fadi abinda ya hadasu..." Baba Abdullahi yayi saurin katse shi da cewa

"Au bama wannanne na farko ba ashe kaga ya daketa na farko yaci banza dole ya yanzu ya qara kuma da zakace bata da gaskiya ta ya akayi ka sani?"

"Koma menene yanzu dai anzo gabar da dole muyi interfering, duk abinda ze faru ya faru amma bazan dauki duba ba. Ban taba daga hannu na daki yar wasu ba dan haka nima baza'a dakar mun tawa yar ba yanzu abinda nake so dakai ai kana da Number Iyayensa ka kirasu ka sanar musu da halin da ake ciki, yanda aka qulla dasu haka za'a warwareta dasu dan daman a baya idan sunyi rigimarsu gurin Marigayi yake zuwa yanzu babu shi shine ze ringa daukar mataki a hannunsa to bazan lamunta ba" Abba ya fada, Baba Abdullahi ya ciji yatsa tareda yin qwafa kafin ya zaro wayarsa ya shiga kiran Alhaji Garba.

Tiryan tiryan ya kora masa jawabi kamar a gabansa akayi Alhaji Garba ya ringa salati ya shiga bashi haquri akan sam be sanda labarin nan ba amma yanzu ze kira Alhaji Abubakar zasu zo tsakanin yau ko gobe dan Allah suyi haquri. Ya kashe wayar yana cewa
"Ahto gara dai suzo, kuma sena rama mata marinta dan ma yaji da jinsa da gatanta" Abba dai murmushi yayi suka shiga karyawa Baba Abdullahi nata Mita har seda Abba ya gaji yace fita zeyi sannan ya tashi suka fita tare bayan sun gaisa da Mama itama ya dira mata Mitar ta shige daki ta barshi.
"Ke daga yau karki sake zuwa gidan nan duk abinda ya hadaku kije can gidana ki gaya mun, kina kallom wannan uwar taki kamar ma tafi sonsa akanki, ji ina mata magana yanda ta hade rai wato an tabo Zuciyarta haka kawai ba dole ma ya ringa jibgarji yanda yaso ba uwar data haifeki ma ta nuna masa bata qaunarki" Baba Abdullahi ya fada yana kallon Umaimah dake zaune har sannan a gaban Murhu Anty Laure kuwa ta cafe tace

"Kai ma ka fada Baban Nabila yo dan ma bakaji abinda take fada bane gaba daya fa ta toshe kunne fadi take haka kawai baze daki Umaimah ba dole da abinda ta masa ni na taba ganin inda ake haka ace ka zabi bare akan naka? Ai ko naka keda laifi kamata yayi ka mora masa baya in yaso a gefe ka nuna masa kuskurensa". Jin ya samu yar tayi se ya fasa tafiya yaja kujerar zama ya kafa suka dora Abba dai yayiwa matansa sallama ya fice a ransa yana cewa
"Ga inda Umaimah ta gado halinta su biyun nan basa son gaskiya qiri qiri suna kallo zasu take abu indai bayazo daidai da ra'ayinsu ba".

KHALIL
Bayanda ya iya haka yaje suka rankaya zuwa gidansu Umaimah. Yana tuqin ji yake kamar ya tsayar da motar yace su sauka saboda yanda suka rufeshi da fada wannan nayi wancan nayi a haka har suka qarasa qofar gidan. Salman daya hango su ya taho da sauri cikin ladabi ya gaida dattijan kafin Khalil ya miqa masa hannu suka gaisa yana tambayarsa Abba yana nan

"Suna ciki, Baba Abdullahi ya hada chamber guda ka shirya yau zakasha Rapping" Salman ya Fada Khalil yayi yar dariya yace
"Tare dakai zamu shiga ka tayani ji"
"Wani, bari dai na gaya masa kunzo" Salman ya fada yana gwalo ido kafin ya juya ya shiga gidan.

A palour Abba ko kamar yanda Salman ya fada yanda kasan wani taron daurin auran Bazawara Haka Baba Abdullahi ya tattago yan uwansu da Aminan Abba samada mutum bakwai, suna zaune yana qara zayyana musu qarya da gaskiyar da Anty Laure ta kora masa, Abba dai takaici ya hanasa magana kallonsa kawai yakeyi Baba Liman Aminin Abba ya kalli Baba Abdullahi yace
"Kai amma kuwa ban zaci yaron nan haka yake ba, ina masa kallon mutumin kirki shiyasa fa tsananta bincike nada kyau amma kaga duk sanda rigima ta taso se mu taru mu goya masa baya ba'a ma neman jin ta bakinta ashe dai shima da nasa halin".

Bude baki Abba yayi zeyi magana Salman ya doko sallama, sanar musu yayi da zuwan su Khalil Abba yace su shigo Baba Abdullahi aka gyara zama harda qara tamke fuska shi ala dole zeyi rashin M dan ya rantse ko an sasanta kafin Umaimah ta koma seya rama mata marin da aka mata ai ba jaka suka aura masa ba.

A qasa Khalil ya samu guri ya zauna ya shiga gaishe su, wasu suka amsa faran faran irinsu Baba Abdullahi da Baba Munzali kuwa iyayen daukar dumi da harara suka bishi shima be damu ba ya sake duqar dakai yana jira su gama gaishe gaishen ayi wadda za'ayi ya tafi amma fa duk bala'i badai Umaiamah ta koma masa gida yau ba.

Baba Abdullahi ya zabura ze fara magama Baba Liman ya dafe hannunsa ya girgiza masa kai dole ya koma yayi shiru Alhaji Abubakar yayi sallama tateda bude taro da Addu'a kafin ya fara koro bayanin ban haquri ya ringayi kafin Alhaji Garba ya karba shima ya dora nasa jawabin ban haqurin tareda roqon Alfarmar komai ya wuce yanzu Umaimah ta shirya ta koma dakinta. Yanda suka sadda kai suna bada haqurin ya saka jikin kowa yayi sanyi yan korar Baba Abdullahi da sukayi shirin yin tijara jiki yayi sanyi. Alhaji Abubakar ya kalli Khalil yace
"Kayi shiru, ga surukanka nan ka basu haquri ka dauki matarka ku koma shikenan magana ta wuce" kafin ma yace wani abu Baba Abdullahi yayi caraf yace

"Ai bazeyi magana ba, tunda ya daketa ya daki banza anzo ana bada haquri su koma kaga ya samu lasisi gobe ma ya qara. To wallahi bari kaji, ka sake ko dungurar mun Ya Three quater zan saka nazo na casaka har cikin gidan naka dan ka sani tambaye su kaji tsohon dan Dambe ne ni ban kuma manta komai ba balle ka dauka na fara tsufa zan kasa lallasaka". Dariya palour ya dauka banda Khalil daya daga kai ya kalle shi yana hasaso wai shi Baba Abdullahi ze daka, ai ko yanzu yake da ganiyar quruciya yasan qirar ba daya ba, lallasashi zeyi ya watsar balle yanzu da shegiyar rigimarsa ta tsufar dashi lokacinsa beyi ba dan idan ka ganshi seka dauka ya girmi Abban.

"Kayi shiru kuwa ana magana" Alhaji Garba ya fada a fusace jin Khalil din bece komai ba, seya dago da kansa a hankali ya kalli Abba da shima shi yake kallo ya sake maida idonsa qasa yace
"Abba kuyi haquri, amma kafin a yanke kowanne hukunci ina so a kira Umaimah tazo a gaban kowa ta fadi gaskiyar abinda ya faru, idan ina da laifi zan nemi yafiyarta da taku mu tafi kamar yanda kuka ce..."
"Idan kuma ba haka ba fa?" Sarkin katsalandan Baba Abdu ya tareshi harda miqewa tsaye kamar ze rufeshida duka se Alhaji Badaru wanda yake bin Abba yayi saurin tareshi shima yana cewa

"Aa Abdullahi maganarsa gaskiya ce ai ba'a shari'a da shaidar bangare daya, a kirata tazo din kamar yanda ya buqata itace shari'a ta gaskiya".
Ajiyar zuciya Khalil ya sauke dan baze sake daukar wani dakon laifin da beyi ba gara tazo in ma wata qaryar ta shirga ta warwareta da kanta kuma in har ta domin Allah za'ayi babu Wanda zece ta kyauta da abinda tayi masa.
Chapter 145 · 0% Book details