Sashe 110
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Idan aka kama ta zata fadi duk ma wanda yake da saka hannu a ciki dan haka yanzu mu saurara mu gani komai yazo qarshw tunda har an samu inda Asalin labarin ya fito" Barr Musa Kallah ya fada se suka mayar da hankali kan Rufaida dake tambayar mutumin zata iya tafiya tunda ta amsa tambayar tasu ya galla mata harara se gashi ta kife kai a Table tana kuka kamar qaramar yarinya abin haushi abin dariya.
Bayan gama tattara bayanai kai tsaye Jami'ai suka kama hanyar gidan su Umaimah. Suna zaune a tsakar gida sun baza babbar Tabarma a qasan Bishiya suna cin gujjiyar da Anty sukaje qauye shekaran jiya ta taho da ita se yanzu da safe Umaimah ta saka jarabar se an dafa. Hira sukeyi abinsu a ranta tana lissafin zuwan Rufaida dan jiya dakyar tayi bacci saboda baqaqen maganganun da Khalil ya yaba mata kawai jira takeyi taji shawarar da zata bata akan yanda zata rama abinda yayi matan.
Salman suka samu a gofar gidan dawowarsa kenan daga Makaranta yaje rubuta jarabawar safe. A darare ya gaisa dasu dan ko hannu da suka bashi ne karba se kallonsu yakeyi yana jiran yaji abinda ya kawo su.
"Kayi mana sallama da me gidan nan mana" daya daga cikin su ya fada, Salman ya kalle shi daga sama har qasa kafin ya shiga cikin gidan, har yayi nisa ya tuna da ai Abban ma baya nan yaje daurin aure Qiru kuma yanzu dai beci ace sun dawo ba se ya juyo da baya daga jikin qofa ya daga murya yanda zasuji shi yace
"Wai baya nan yayi tafiya"
"Toh kayi mana magana da wani babbaa ciki naga alamar kamar kai ka tsorata da ganinmu" Mutumin ya sake fada se ya juya ba tareda yace musu komai ba ya shige gidan. Yanayin da yayi sallama ya saka suka bishi da kallo gaba daya, ya kalli Mama data fi kusa da qofar tsakiyar yace
"Mama wasu mutane sun zo neman Abba na gaya musu baya nan sunce wani babba yaje"
"Kamar Yaya wani babba? Kai din baka isa ka wakilce shi ba zaka taho wani zoqai zoqai dakai" Maman ta fada se yayi ciki yana cewa
"Jami'an tsaro ne, gara dai a cikinku wata ta leqa taji me yake faruwa"
"Ba shakka wato idan ma tafiya za suyi damu shikenan ba, baci gidanku kuwa kai zaka koma kaji abinda ya kawo su" Maman ta fada seya marairaice yana cewa
"Jiya fa na baku labarin case din wayar Hassan idan kuma sune suka biyo nifa dan Allah tunda dai su sukace na turo wani Mama ko Anty kuje, ga Yah Umaimah nan ma ai itama babbace"
Umaimah data bubbude qafafu ta aje ciki tsakiya ta galla masa harara harda murguda bakinta dayayi labcece dan wannan karon sosai ciki ya canza mata kamanni tana kallonsa tace
"Inda ace harkar samu ce ai da bazak shigo kace wani yaje ba ko" Sallamar da aka buga daga gareji ta saka su yin shiru. Mama ta maida Hijabin da tayi sallar Walha ta miqe tana cewa
"Bari na leqa karsu ce an barsu a tsaye".
Bayan sun gaisa ya zaro ID card ya nuna mata yana cewa
" Daga State CID muke, an bamu umarnin mu tafi da Umaimah Sabo".
Mama ta dafe qirji tana kiran sunayen Allah kafin tace
"Umaimah kuma? Ni Malika rigimar wa ta janyo mana"
"Idan munje can Zakuji koma menen Hajiya, ayi mata magana ta fito saboda ana jiran mune bamason bata lokaci" ya sake fada a qagare yana zazzare ido, badan doka ba da cikin gidan ze shiga dakansa ya fito da ita.
Jiki a sabule Mama ta koma ta tarar dasu cirko cirko dan tun Salatin da ta rafka suka jiyota, abinda yazo musu a rai su Abbane sukayi Hatsari amma yanayin data shigo beyi kama da na wadda aka fadawa zancen Mutuwa ba idonta akan Umaimah da ita kadai ce a zaune tace
"Tashi ki sako Hijabinki ana jiranki a waje"
"Ni kuma waye yake nemana?" Ta fada tana kallon Maman, tsawa ta buga mata da seda ta zabura ta miqe babu shiri kafin tace
"Ki wuce kiyi abinda nace, dukma wanda yake nemanki zaki gani tunda kinsan rigimar da kika siyowa kanki".
Sum sum Umaimah ta shige daki ta sako Hijabi, silifas ta zura bata iya tsayawa daukan wayarta ba saboda Tsawar da Mama ta sake buga mata ta fice tana waiwayensu, a garejin taga Mutane sunsha baqar Suit su hudu suna jiranta girjinta ya bada qara Dumm, badai Khalil ne ya turo a tafi da ita ba?
Anty data biyo bayanta ganin qatti har hudu ta kwalawa Mama kira tana cewa
"Na shiga uku ina zasu tafi da ita? Haka kawai kince yarinya ta fita Kallarau fa mutane babu alamar Rahama a fuskarsu su waye wadannan?"
Shiru Mama dake tsaye a bakin qofa tayi mata seta koma ciki da gudu ta sako Hijabi tabi bayansu tuni sun tasa qeyar Umaimah a mota Anty ta sako kwasowa da gudu ta shigo gidan tana cewa
"Sunfa tafi da ita, a zamanin nan Idan wani abu ya samu yarinyar nan me zamu cewa Mijinta"
"Sunce daga CID suke kuma laifi tayi aka turo su tafi da ita" Maman ta fada tamkar ta rusa ihu saboda abinda takeji, Salman ya dora hannu biyu a kai yace
"Mama kika bari suka tafi da ita? Kin tabbatar daga can suke innalillahi, se ya zabura yayi waje yana cewa
"Ku kira Yaya Aminu ku gaya masa bari nabi bayansu naga inda zasuje" ya burga Mashin dinsa ya bisu da gudun tsiya dan har sun fice daga layin. Seda Salman din yayi magana kuma taji wani tsoro ya dirar mata, meyasa ba tayi tunanin kiran Aminun ba kafin su tafi da ita kai ita kam ta shiga boni.
Maganar Anty ta jiyo tana waya da alama da Aminun ne dan taji tace Yayansu seta nemi guri ta zauna kawai a zuciyarta tana Addu'ar Allah ya tsare mata Umaiman yasa tana hannu na gari. Kusan minti goma sha biyar sega Aminun ya shigo daga bakin qofa yace su fito, Anty da Maman suka runtuma har suna ture juna Salma da Yasir zasu bisu ya daka musu tsawa dole suka koma suna hawaye. Har suka isa tambayar junansu suke akan me yake faruwa?
A can suka hadu da Mijin Rufaida da Mamanta wadda Mama ta ganeta saboda sunzo sunan Nuratu da akayi Sati biyu da suka wuce tareda Rufaidan nan suka shiga tambayar juna ba'asi babu me amsar bawa dan uwansa se suka samu guri suka zauna jiran Aminu da aka barshi ya shiga Albarkacin kasancewarsa Jami'in tsaro.
Sanda Khalil ya iso a sannan Aminu yakeyi musu bayanin tuhumar da akeyiwa su Umaiman, Mama dake zaune akan Benci tace
"Yanzu meya hada yaran nan da wata hukumar kare haqqin Mata da har suka kawo su qara kai lamarin Umaimah baze kashe taba.
Umaimah
Tana fitowa daga mota idonta ya sauka akan Isma'il da suka fito daga sallar Azahar. Wani mugun kallon tsana ta bishi dashi ta tuna Marin da yayi mata amma in ta tuno da abinda ta aikata musu se taji ranta yayi sanyi, haka aka tasa qeyarta shi be ma ganta ba suna magana da Barr Kallah tana shiga ta ga Rufaidah a rabe a wani guri tana aikin Kuka fuskarta tayi qozai qozai duk kwalliyar nan ta kama gabanta dan dankwalin dashi take faman goge hawaye tana ganin Umaimah ta miqe tana cewa
"Gata nan wallahi, dan Girman Allah ku sallameni na tafi tunda tazo. Wallahi bani da hannu a ciki ita ta shirya abinta kawai gani nayi ta tura mana".
Turus Umaimah tayi tana kallonta wata mata ta bugawa Rufaidan tsawa tana cewa idan bata rufe mata baki ba zata jefata a Cell saboda ma taga an barta a waje ne take musu surutu criminal din banza kawai seta koma ta zauna jiki na bari tana ci gaba da share hawaye.
Gurinta Umaimah ta nufa wanda ya shigo da ita ya dakatar da ita ya nuna mata wata qofa, batayi musu ba ta tura ta shiga. Dakine babu komai ciki se Table da kujeru guda biyu daya na kallon daya ta nemi guri ta zauna tana kalle kalle. Mutumin da ya tambayi Rufaida ne ya dawo ya qara tamke fuskar nan ta kalleshi take itama ta sake hade tata fuskar ta na muzurai se kawai ya tsaya yana kallonta tsabar mamaki. Ba Mace ba ko Maza manyan Criminals sukayi Arba da fuskarsa shiga taitayinsu suke ballantana wannan da tsaf ze iya hadiyeta tazo tana masa muzurai seya buga takaddun da ya shigo dasu akan Table din Umaimah ta daga kai ta harareshi a fakaice ta kalli qasa.
Hotuna ya watsa mata yana kallonta da jajayen idonsa yace
"Wacece wannan?"
Ta debesu tana dubawa, baki ta tabe irin ko a jikin nan nata kafinta maidasu ta ajiye tana cewa
"Wai sunanta Hadiza kowa"
"Ki shiga taitayinki nan ba gurin wasa bane" Mutum ya fada cikin tsawa yanabuga bencin gabansa. Umaimah ta gyara zama har ranta taji tsoron tsawar daya mata amma ta dake. Kallonsa tayi tace
"To wai ma nan din ina ne kuma menayi da zaka zo ka sani a gaba kana mun Ihu? Nidai karka firgitamun Da a ciki, idan tambayata zakayi salin alin base kayimun hargagi ba".
Dukda dokar da aka bashi ta karya taba lafiyarta besan sanda ya kwasa mata mari da lafcecen hannunsa ba ta fasa ihu tayi baya qiris ya rage ita da kujerar su fadi yayi saurin tareta yana sake buga mata tsawa yace
"Naga alamar bakida kunya kuma baki san a inda kike ba, to ki tattara hankalinki guri guda ki amsamun tambayoyina mu rabu lafiya idan haka ba sena saba miki kamanni kafin ki fita daga nan".
Magana akayi masa ta cikin abinda ya maqala a kunnensa cikin girmamawa yace
"Sorry Sir, yarinyarce bakinta bashi da saiti amma za'a kiyaye" seya juya kan Umaimah shatato hawaye kamar lalataccen famfo ta toshe bakinta da hannu daya tana shafa inda ya mareta da dayan. Murmushin mugunta yayi ya sake tura mata hotunan yana cewa
"Wacece wannan, kuma menene alaqarki da ita?"
Bayan gama tattara bayanai kai tsaye Jami'ai suka kama hanyar gidan su Umaimah. Suna zaune a tsakar gida sun baza babbar Tabarma a qasan Bishiya suna cin gujjiyar da Anty sukaje qauye shekaran jiya ta taho da ita se yanzu da safe Umaimah ta saka jarabar se an dafa. Hira sukeyi abinsu a ranta tana lissafin zuwan Rufaida dan jiya dakyar tayi bacci saboda baqaqen maganganun da Khalil ya yaba mata kawai jira takeyi taji shawarar da zata bata akan yanda zata rama abinda yayi matan.
Salman suka samu a gofar gidan dawowarsa kenan daga Makaranta yaje rubuta jarabawar safe. A darare ya gaisa dasu dan ko hannu da suka bashi ne karba se kallonsu yakeyi yana jiran yaji abinda ya kawo su.
"Kayi mana sallama da me gidan nan mana" daya daga cikin su ya fada, Salman ya kalle shi daga sama har qasa kafin ya shiga cikin gidan, har yayi nisa ya tuna da ai Abban ma baya nan yaje daurin aure Qiru kuma yanzu dai beci ace sun dawo ba se ya juyo da baya daga jikin qofa ya daga murya yanda zasuji shi yace
"Wai baya nan yayi tafiya"
"Toh kayi mana magana da wani babbaa ciki naga alamar kamar kai ka tsorata da ganinmu" Mutumin ya sake fada se ya juya ba tareda yace musu komai ba ya shige gidan. Yanayin da yayi sallama ya saka suka bishi da kallo gaba daya, ya kalli Mama data fi kusa da qofar tsakiyar yace
"Mama wasu mutane sun zo neman Abba na gaya musu baya nan sunce wani babba yaje"
"Kamar Yaya wani babba? Kai din baka isa ka wakilce shi ba zaka taho wani zoqai zoqai dakai" Maman ta fada se yayi ciki yana cewa
"Jami'an tsaro ne, gara dai a cikinku wata ta leqa taji me yake faruwa"
"Ba shakka wato idan ma tafiya za suyi damu shikenan ba, baci gidanku kuwa kai zaka koma kaji abinda ya kawo su" Maman ta fada seya marairaice yana cewa
"Jiya fa na baku labarin case din wayar Hassan idan kuma sune suka biyo nifa dan Allah tunda dai su sukace na turo wani Mama ko Anty kuje, ga Yah Umaimah nan ma ai itama babbace"
Umaimah data bubbude qafafu ta aje ciki tsakiya ta galla masa harara harda murguda bakinta dayayi labcece dan wannan karon sosai ciki ya canza mata kamanni tana kallonsa tace
"Inda ace harkar samu ce ai da bazak shigo kace wani yaje ba ko" Sallamar da aka buga daga gareji ta saka su yin shiru. Mama ta maida Hijabin da tayi sallar Walha ta miqe tana cewa
"Bari na leqa karsu ce an barsu a tsaye".
Bayan sun gaisa ya zaro ID card ya nuna mata yana cewa
" Daga State CID muke, an bamu umarnin mu tafi da Umaimah Sabo".
Mama ta dafe qirji tana kiran sunayen Allah kafin tace
"Umaimah kuma? Ni Malika rigimar wa ta janyo mana"
"Idan munje can Zakuji koma menen Hajiya, ayi mata magana ta fito saboda ana jiran mune bamason bata lokaci" ya sake fada a qagare yana zazzare ido, badan doka ba da cikin gidan ze shiga dakansa ya fito da ita.
Jiki a sabule Mama ta koma ta tarar dasu cirko cirko dan tun Salatin da ta rafka suka jiyota, abinda yazo musu a rai su Abbane sukayi Hatsari amma yanayin data shigo beyi kama da na wadda aka fadawa zancen Mutuwa ba idonta akan Umaimah da ita kadai ce a zaune tace
"Tashi ki sako Hijabinki ana jiranki a waje"
"Ni kuma waye yake nemana?" Ta fada tana kallon Maman, tsawa ta buga mata da seda ta zabura ta miqe babu shiri kafin tace
"Ki wuce kiyi abinda nace, dukma wanda yake nemanki zaki gani tunda kinsan rigimar da kika siyowa kanki".
Sum sum Umaimah ta shige daki ta sako Hijabi, silifas ta zura bata iya tsayawa daukan wayarta ba saboda Tsawar da Mama ta sake buga mata ta fice tana waiwayensu, a garejin taga Mutane sunsha baqar Suit su hudu suna jiranta girjinta ya bada qara Dumm, badai Khalil ne ya turo a tafi da ita ba?
Anty data biyo bayanta ganin qatti har hudu ta kwalawa Mama kira tana cewa
"Na shiga uku ina zasu tafi da ita? Haka kawai kince yarinya ta fita Kallarau fa mutane babu alamar Rahama a fuskarsu su waye wadannan?"
Shiru Mama dake tsaye a bakin qofa tayi mata seta koma ciki da gudu ta sako Hijabi tabi bayansu tuni sun tasa qeyar Umaimah a mota Anty ta sako kwasowa da gudu ta shigo gidan tana cewa
"Sunfa tafi da ita, a zamanin nan Idan wani abu ya samu yarinyar nan me zamu cewa Mijinta"
"Sunce daga CID suke kuma laifi tayi aka turo su tafi da ita" Maman ta fada tamkar ta rusa ihu saboda abinda takeji, Salman ya dora hannu biyu a kai yace
"Mama kika bari suka tafi da ita? Kin tabbatar daga can suke innalillahi, se ya zabura yayi waje yana cewa
"Ku kira Yaya Aminu ku gaya masa bari nabi bayansu naga inda zasuje" ya burga Mashin dinsa ya bisu da gudun tsiya dan har sun fice daga layin. Seda Salman din yayi magana kuma taji wani tsoro ya dirar mata, meyasa ba tayi tunanin kiran Aminun ba kafin su tafi da ita kai ita kam ta shiga boni.
Maganar Anty ta jiyo tana waya da alama da Aminun ne dan taji tace Yayansu seta nemi guri ta zauna kawai a zuciyarta tana Addu'ar Allah ya tsare mata Umaiman yasa tana hannu na gari. Kusan minti goma sha biyar sega Aminun ya shigo daga bakin qofa yace su fito, Anty da Maman suka runtuma har suna ture juna Salma da Yasir zasu bisu ya daka musu tsawa dole suka koma suna hawaye. Har suka isa tambayar junansu suke akan me yake faruwa?
A can suka hadu da Mijin Rufaida da Mamanta wadda Mama ta ganeta saboda sunzo sunan Nuratu da akayi Sati biyu da suka wuce tareda Rufaidan nan suka shiga tambayar juna ba'asi babu me amsar bawa dan uwansa se suka samu guri suka zauna jiran Aminu da aka barshi ya shiga Albarkacin kasancewarsa Jami'in tsaro.
Sanda Khalil ya iso a sannan Aminu yakeyi musu bayanin tuhumar da akeyiwa su Umaiman, Mama dake zaune akan Benci tace
"Yanzu meya hada yaran nan da wata hukumar kare haqqin Mata da har suka kawo su qara kai lamarin Umaimah baze kashe taba.
Umaimah
Tana fitowa daga mota idonta ya sauka akan Isma'il da suka fito daga sallar Azahar. Wani mugun kallon tsana ta bishi dashi ta tuna Marin da yayi mata amma in ta tuno da abinda ta aikata musu se taji ranta yayi sanyi, haka aka tasa qeyarta shi be ma ganta ba suna magana da Barr Kallah tana shiga ta ga Rufaidah a rabe a wani guri tana aikin Kuka fuskarta tayi qozai qozai duk kwalliyar nan ta kama gabanta dan dankwalin dashi take faman goge hawaye tana ganin Umaimah ta miqe tana cewa
"Gata nan wallahi, dan Girman Allah ku sallameni na tafi tunda tazo. Wallahi bani da hannu a ciki ita ta shirya abinta kawai gani nayi ta tura mana".
Turus Umaimah tayi tana kallonta wata mata ta bugawa Rufaidan tsawa tana cewa idan bata rufe mata baki ba zata jefata a Cell saboda ma taga an barta a waje ne take musu surutu criminal din banza kawai seta koma ta zauna jiki na bari tana ci gaba da share hawaye.
Gurinta Umaimah ta nufa wanda ya shigo da ita ya dakatar da ita ya nuna mata wata qofa, batayi musu ba ta tura ta shiga. Dakine babu komai ciki se Table da kujeru guda biyu daya na kallon daya ta nemi guri ta zauna tana kalle kalle. Mutumin da ya tambayi Rufaida ne ya dawo ya qara tamke fuskar nan ta kalleshi take itama ta sake hade tata fuskar ta na muzurai se kawai ya tsaya yana kallonta tsabar mamaki. Ba Mace ba ko Maza manyan Criminals sukayi Arba da fuskarsa shiga taitayinsu suke ballantana wannan da tsaf ze iya hadiyeta tazo tana masa muzurai seya buga takaddun da ya shigo dasu akan Table din Umaimah ta daga kai ta harareshi a fakaice ta kalli qasa.
Hotuna ya watsa mata yana kallonta da jajayen idonsa yace
"Wacece wannan?"
Ta debesu tana dubawa, baki ta tabe irin ko a jikin nan nata kafinta maidasu ta ajiye tana cewa
"Wai sunanta Hadiza kowa"
"Ki shiga taitayinki nan ba gurin wasa bane" Mutum ya fada cikin tsawa yanabuga bencin gabansa. Umaimah ta gyara zama har ranta taji tsoron tsawar daya mata amma ta dake. Kallonsa tayi tace
"To wai ma nan din ina ne kuma menayi da zaka zo ka sani a gaba kana mun Ihu? Nidai karka firgitamun Da a ciki, idan tambayata zakayi salin alin base kayimun hargagi ba".
Dukda dokar da aka bashi ta karya taba lafiyarta besan sanda ya kwasa mata mari da lafcecen hannunsa ba ta fasa ihu tayi baya qiris ya rage ita da kujerar su fadi yayi saurin tareta yana sake buga mata tsawa yace
"Naga alamar bakida kunya kuma baki san a inda kike ba, to ki tattara hankalinki guri guda ki amsamun tambayoyina mu rabu lafiya idan haka ba sena saba miki kamanni kafin ki fita daga nan".
Magana akayi masa ta cikin abinda ya maqala a kunnensa cikin girmamawa yace
"Sorry Sir, yarinyarce bakinta bashi da saiti amma za'a kiyaye" seya juya kan Umaimah shatato hawaye kamar lalataccen famfo ta toshe bakinta da hannu daya tana shafa inda ya mareta da dayan. Murmushin mugunta yayi ya sake tura mata hotunan yana cewa
"Wacece wannan, kuma menene alaqarki da ita?"