Sashe 3
Halin Kishi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Basu bar gurin kwalliya ba dai qarshe seda akayi sallar Magriba ko kafin su Isa Gurin Kamun ma takwas saura dan da tafiya daga gurin kwalliyar zuwa can. Ruma kamar zatayi kuka, ita ba kanta ma takeji ba dan a gida ta fada daman zasu iya kaiwa Zuwa Takwas haka kuma an barta amma Umaimah take jiwa dan yanda Mama ta ringa jaddada mata kar tayi Magriba awaje idan ba haka ba zata hadu da Abban su tasan akwai abinda ta aikata da ya saka ake horata.
Sun tarar da Anties din Amarya da daman tun suna gurin kwalliya ake doka mata waya, wata daga ciki ta tare su da wani mulmulallan Ashar tana cewa
"Banda tsabar iskanci Kamu ba dinner ba ki tafi ki share guri kiyi zamanki har takwas uban waye ze zauna yana jiranki? Kwalliyar da kika bata kudi kikayi ta tashi a banza dan rabin mutane sun kama gabansu su kansu dangin mijin naki gasu can har sun fito zasu tafi dakyar aka lallabasu suka zauna shegiya kuma baki kyau bama"
Amarya Halima ta tura baki dan daman tasan se Anty Mara tayi masifa dan tafi kowa fada a cikin Anties din nata, haka suka rankaya suka shiga Yammata na take mata baya. Amarya na zama a kujerarta Rumah ta zagaya aka musu hoto kafin ta rada mata a kunne ta tafi se gobe zata zo gidansu daurin aure da yini. Da sauri ta qarasa inda Su Umaimah suka zauna tana ce mata
"Kije kuyi sallama da Halima mu tafi Umaimah takwas fa keda aka ce kar kiyi magriba a waje".
"Kuje ina haba malama kema ba inda zakije nemi guri ki zauna yanzu fa zaa fara biki ki wani ce ku tafi baza ku tafin ba" Fannah ta fada tana qoqarin zaunar da ita seta turje tana cewa
"Barni Fannah tafiya zamuyi Umaimah muje dan Allah dare na dada yi".
"In zaki tafi ga hanya nan ban riqe ki ba amma ni kam se naga kwal uwar daka, daga zuwan mu kice mu tafi ba wannan maganar" tana rufe baki kiran Mama ya shigo wayarta data ajiye akan Table
"Kin gani ko gashi nan Mama tana kiranki kar ki jawa kanki wani Fadan ki tashi kawai mu tafi" Rumah ta fada a rikice kamar ita ce tayi laifin
"Ai se kiyi, kona koma yanzu ko ban koma ba duk daya fada ne sena sha shi toh in zaki zauna ki zauna idan kuma tafiya ce a sauka lafiya" ta bata amsa tana kashe wayarta gaba daya dan tasan Mama yanzu idanta dosa mata kira ba haqura zatayi ba, kuma dai laifi ne dai ta rigada tayi tunda kafin Magriba akace ta dawo gashi har isha ta wuce bata komaba.
©️2️⃣0️⃣2️⃣3️⃣
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*👹🥰
*And now*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE*
*KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA*
*07061838488*
*A BIYA A KARANTA*
Free page 2
Biki yayi biki, an raqashe anci an sha yammata sunyi rawa, Umaimah bata an kare da lokaci ba seda aka tashi ta kunna waya lokacin qarfe goma harda rabi tayi, daga gurin zuwa gidansu kuwa taci kusan Minti talatin a qiyasi dai sha daya ce zata kaita gida lallai kam yau ta taro Match me zafi dan tasan ma kafin taje tuni an kulle gida.
A motar Mijin Fannah suka tafi da yake hanyar su daya, ita bayin daren ne yafi daga mata hankali ba, Aa Abayar data saka da zata fito ta barota a gidan Maman Nana saboda bazata shiga jakarta ba kuma batayi zaton zasuyi dare har haka ba.
Cikin taraddadin abinda zata tarar suka sauketa a qofar gidan su, jiki a sabule ta sauka tana gyara yafen dan babban mayafin data samu sukayi musanye da Fannah ko ta dan qara rufe jikinta. A darare ta qarasa jikin qaramar qofar Get din da niyyar bugawa dan tasan dai an kulle se taji takun takalma a bayan ta.
A mugun zabure ta matsa, Abbane, da torchlight a hannunsa saboda an dauke wuta yayi mata kallo daya kafin ya saka muqulli ya bude gidan ya shiga ba tareda ya ce mata komai ba haka ta bishi zugui zugui a baya, ganin yayi kamar ma besan da wanzuwarta ba yasa ta kwasa da saurin gaske tayi ciki tana qara godewa Allah da ya saka babu hasken Nepa kuma be haska jikinta da fitilar hannunsa ba balle yaga irin shigar da tayi.
Dan dama daman da ta sake ji dayaga dawowarta ba ita kadai ba dan seda Fannah ta fito ta bude mata murfin motar da ya samu matsala, yanzu da ace saurayi ne ya ajiyeta a daren nan tana ga kawai tsirenta za suyi su huta.
Dakinsu ta fada tana sauke numfashi, bata tsaya ba seda ta tube kayan ta jefa can cikin wardrobe kafin tayi maza ta fada bandaki ta watsa ruwa tareda Alwala. Tayi mamakin ganin harta idar da sallah babu wanda ya biyo sahunta, amma tasan tarko ne. Tana jin yunwa haka nan ta haye gado ta kwanta, tunda dai ta shigo gidan zance ya qare duk wacce zaayi ayi da safe ai.
Washe gari ta kama Asabar, yanda taga babu wanda ko a fuska ya nuna mata tayi laifi jiyan ya fara daga mata hankali, tana so ta tafi gidan su Halima Daurin aure tana tsoron abinda tambayar hakan ze janyo mata.
Wuraren 11 tana zaune a dakinsu, tsoro take ta fita tsakar gidan su hadu da wani daga cikin Mama ko Abban ga Yunwar data kwana da ita ta hadu da ta safiya tana ta sakudarta. Nuratu Yayarta da take bima ta shiga dakin da farantin qosai da kofin da ta zubo kunun gyada ta nemi gefen gadonta ta zauna tana aikawa da Umaiman harara dan daman tun Asuba data farka ta ganta bata ce mata komai ba sedai idan sun hada ido ta maka mata harara kawai.
Ganin qosan da kunu ya qara wutar rura yunwar da take ji amma yanayin fuskar Yaya Nuratun yasa ta kasa ce mata zata ci, gashi babu motsin kowa a tsakar gidan qannensu duk sun tafi Tahfiz bare ta yafito wani ta saka ya debo mata. Ganinfa tana neman illata kanta dan damanita bame jumurin yubwa bace yasa ta yunqura da niyyar ta roqi yayar tata sega sallamar Qaninta.
Daga bakin qofar yace
" Yaya Umaimah kije inji Abba yana kiranki" ya juya abinsa. Seda cikinta ya bada wani qulululu, ashe ba kyaketa akayi ba jira suke gari ya gama wayewa tas ayi mata taron dangi dan taji shigowar Baba Abdullahi da Yaya Aminu babban Yayansu gidan.
"Yaya Nuratu dan Allah ki bani ko kunun ne nasha wallahi banajin zan iya tafiya ma yunwa nake ji" ta fada a marairaice dan gara ta karya bille ta roqeta, bata sani ba ko baa girka da ita ba kar taje garin diba ta qarayin wani laifin.
Banza Nuratun ta mata seda ta sake roqonta kafin ta turo mata kwanon qosan da kunun da ko rabi bata ci ba dan tana yi tana duba wani texbook nasu na yan medicine tace mata
"Gashinan Mayya se kici ai"
"Idan ni mayyace ke ma ai mayyar ce" Umaimah ta fada cikin qunquni ta ja kayan ta fara ci hannu baka hannu kwarya cikin dan lokaci ta cinye tas ta zura dogon Hijab har qasa ta fita tana nanata La'ilaha illah anta subhanaka innikuntu minazzalimin a zuciyarta harta isa qofar Sitting room din Abbansu.
Ta shiga da sallama kai a qasa kamar ta Allah ta rabe a bakin qofa tana gaishe su ba tare data bari sun hada ido da kowa a cikin su ba. Yaya Aminu ne ya daka mata tsawa yace
"Zaki matso ciki ne kose na zo nan na tattaka ki mara jin magana kawai"
"Barta Aminullahi fada da hargagi baya gyara, nasihar dai ita zaa ci gaba har sanda Allah ze sa ta dena abinda takeyi" Taji Muryar Baba Liman Aminin Abbansu ta katse hargagin da Yaya Aminu ya fara yi mata. Wata nutsuwa taji ta dan saukar mata dan ko ba komai akwai me kareta dan baze bari su mata komai ba amma da ta gama saddaqarwa yau kashinta ya bushe dan daga Yaya Aminun har Baba Abdullahi babu me sauqi, Abba kuwa zuba ido zeyi su caskalata babu abinda ya masa zafi.
"Ina wayarki take?" Baba Abdullahi ya fada cikin zafin nan nasa, seta daga kai ta kalleshi aranta tana cewa
"Toh takunkumi zaa sakamun kenan a hanani fita a karbe mun waya tab aikuwa da sake"
"Ba magana ake miki ba?" Aminu ya sake zaburowa, qasa qasa ta harare shi kafin tace
"Tana cikin gida"
"Kije ki dakkota da duk wani abu da kika san Qasim ya mallaka miki ki kawo nan" Baba Liman ya fada.
"Duk abinda tasan nasa ne ko tsinke ne ta hado" wani mutum da sam bata lura da shi a palour bama ya fada se faman girgiza qafa yake kamar ana yaqi, Se ta dago tana kallon shi dason jin qarin bayani, amma yanayin da tagani akan fuskar Abbanta da irin hararar daya watsa mata tasa ta miqe babu shiri.
Sabuwar Iphone din da Qasim ya siya mata bayan kawo kudin auran su da kwana biyu ta dakko tana jujjuyawa, to me ya faru me zasuyi da wayar? Kuma ai ce mata aka yi ta dakko duk abinda ya mallaka mata kenan ba wai kwace wayar zaayi ba wani abun ne daban.
Tunanin me dame ma Qasim din ya taba siya mata ta shiga yi, shi ba gwanin siyan kaya bane gara dai kayan maqulashe duk zuwa da abinda ze kawo mata. Wardrobe ta bude ta zaro lesina guda biyu daya dinkakke ne dayan baa dinka ba se Atamfa guda daya itama dinkakkiya kayan toshin wannan qaramar sallar da yayi matane, ta saka Atamfar Leshin kuma daman yau tayi niyyar saka shi.
Ragowar tarkacen Jaka da takalmi da mayafai ta debo ta hada cikin babbar Leda, ta kalli turarukan dake kan Mudubin su wanda suma a cikin kayan take ta tabe baki a fili tace
Sun tarar da Anties din Amarya da daman tun suna gurin kwalliya ake doka mata waya, wata daga ciki ta tare su da wani mulmulallan Ashar tana cewa
"Banda tsabar iskanci Kamu ba dinner ba ki tafi ki share guri kiyi zamanki har takwas uban waye ze zauna yana jiranki? Kwalliyar da kika bata kudi kikayi ta tashi a banza dan rabin mutane sun kama gabansu su kansu dangin mijin naki gasu can har sun fito zasu tafi dakyar aka lallabasu suka zauna shegiya kuma baki kyau bama"
Amarya Halima ta tura baki dan daman tasan se Anty Mara tayi masifa dan tafi kowa fada a cikin Anties din nata, haka suka rankaya suka shiga Yammata na take mata baya. Amarya na zama a kujerarta Rumah ta zagaya aka musu hoto kafin ta rada mata a kunne ta tafi se gobe zata zo gidansu daurin aure da yini. Da sauri ta qarasa inda Su Umaimah suka zauna tana ce mata
"Kije kuyi sallama da Halima mu tafi Umaimah takwas fa keda aka ce kar kiyi magriba a waje".
"Kuje ina haba malama kema ba inda zakije nemi guri ki zauna yanzu fa zaa fara biki ki wani ce ku tafi baza ku tafin ba" Fannah ta fada tana qoqarin zaunar da ita seta turje tana cewa
"Barni Fannah tafiya zamuyi Umaimah muje dan Allah dare na dada yi".
"In zaki tafi ga hanya nan ban riqe ki ba amma ni kam se naga kwal uwar daka, daga zuwan mu kice mu tafi ba wannan maganar" tana rufe baki kiran Mama ya shigo wayarta data ajiye akan Table
"Kin gani ko gashi nan Mama tana kiranki kar ki jawa kanki wani Fadan ki tashi kawai mu tafi" Rumah ta fada a rikice kamar ita ce tayi laifin
"Ai se kiyi, kona koma yanzu ko ban koma ba duk daya fada ne sena sha shi toh in zaki zauna ki zauna idan kuma tafiya ce a sauka lafiya" ta bata amsa tana kashe wayarta gaba daya dan tasan Mama yanzu idanta dosa mata kira ba haqura zatayi ba, kuma dai laifi ne dai ta rigada tayi tunda kafin Magriba akace ta dawo gashi har isha ta wuce bata komaba.
©️2️⃣0️⃣2️⃣3️⃣
*DAGA ALQALAMIN MARYAM FAROUK (UMMU-MAHEER)*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*👹🥰
*And now*
*HALIN KISHI LITTAFIN KUDI NE*
*KI TURA DA 500 ZUWA ASUSUN*
*8142548705*
*OPAY DIGITAL SERVICE*
*MARYAM UMAR FAROUK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA*
*07061838488*
*A BIYA A KARANTA*
Free page 2
Biki yayi biki, an raqashe anci an sha yammata sunyi rawa, Umaimah bata an kare da lokaci ba seda aka tashi ta kunna waya lokacin qarfe goma harda rabi tayi, daga gurin zuwa gidansu kuwa taci kusan Minti talatin a qiyasi dai sha daya ce zata kaita gida lallai kam yau ta taro Match me zafi dan tasan ma kafin taje tuni an kulle gida.
A motar Mijin Fannah suka tafi da yake hanyar su daya, ita bayin daren ne yafi daga mata hankali ba, Aa Abayar data saka da zata fito ta barota a gidan Maman Nana saboda bazata shiga jakarta ba kuma batayi zaton zasuyi dare har haka ba.
Cikin taraddadin abinda zata tarar suka sauketa a qofar gidan su, jiki a sabule ta sauka tana gyara yafen dan babban mayafin data samu sukayi musanye da Fannah ko ta dan qara rufe jikinta. A darare ta qarasa jikin qaramar qofar Get din da niyyar bugawa dan tasan dai an kulle se taji takun takalma a bayan ta.
A mugun zabure ta matsa, Abbane, da torchlight a hannunsa saboda an dauke wuta yayi mata kallo daya kafin ya saka muqulli ya bude gidan ya shiga ba tareda ya ce mata komai ba haka ta bishi zugui zugui a baya, ganin yayi kamar ma besan da wanzuwarta ba yasa ta kwasa da saurin gaske tayi ciki tana qara godewa Allah da ya saka babu hasken Nepa kuma be haska jikinta da fitilar hannunsa ba balle yaga irin shigar da tayi.
Dan dama daman da ta sake ji dayaga dawowarta ba ita kadai ba dan seda Fannah ta fito ta bude mata murfin motar da ya samu matsala, yanzu da ace saurayi ne ya ajiyeta a daren nan tana ga kawai tsirenta za suyi su huta.
Dakinsu ta fada tana sauke numfashi, bata tsaya ba seda ta tube kayan ta jefa can cikin wardrobe kafin tayi maza ta fada bandaki ta watsa ruwa tareda Alwala. Tayi mamakin ganin harta idar da sallah babu wanda ya biyo sahunta, amma tasan tarko ne. Tana jin yunwa haka nan ta haye gado ta kwanta, tunda dai ta shigo gidan zance ya qare duk wacce zaayi ayi da safe ai.
Washe gari ta kama Asabar, yanda taga babu wanda ko a fuska ya nuna mata tayi laifi jiyan ya fara daga mata hankali, tana so ta tafi gidan su Halima Daurin aure tana tsoron abinda tambayar hakan ze janyo mata.
Wuraren 11 tana zaune a dakinsu, tsoro take ta fita tsakar gidan su hadu da wani daga cikin Mama ko Abban ga Yunwar data kwana da ita ta hadu da ta safiya tana ta sakudarta. Nuratu Yayarta da take bima ta shiga dakin da farantin qosai da kofin da ta zubo kunun gyada ta nemi gefen gadonta ta zauna tana aikawa da Umaiman harara dan daman tun Asuba data farka ta ganta bata ce mata komai ba sedai idan sun hada ido ta maka mata harara kawai.
Ganin qosan da kunu ya qara wutar rura yunwar da take ji amma yanayin fuskar Yaya Nuratun yasa ta kasa ce mata zata ci, gashi babu motsin kowa a tsakar gidan qannensu duk sun tafi Tahfiz bare ta yafito wani ta saka ya debo mata. Ganinfa tana neman illata kanta dan damanita bame jumurin yubwa bace yasa ta yunqura da niyyar ta roqi yayar tata sega sallamar Qaninta.
Daga bakin qofar yace
" Yaya Umaimah kije inji Abba yana kiranki" ya juya abinsa. Seda cikinta ya bada wani qulululu, ashe ba kyaketa akayi ba jira suke gari ya gama wayewa tas ayi mata taron dangi dan taji shigowar Baba Abdullahi da Yaya Aminu babban Yayansu gidan.
"Yaya Nuratu dan Allah ki bani ko kunun ne nasha wallahi banajin zan iya tafiya ma yunwa nake ji" ta fada a marairaice dan gara ta karya bille ta roqeta, bata sani ba ko baa girka da ita ba kar taje garin diba ta qarayin wani laifin.
Banza Nuratun ta mata seda ta sake roqonta kafin ta turo mata kwanon qosan da kunun da ko rabi bata ci ba dan tana yi tana duba wani texbook nasu na yan medicine tace mata
"Gashinan Mayya se kici ai"
"Idan ni mayyace ke ma ai mayyar ce" Umaimah ta fada cikin qunquni ta ja kayan ta fara ci hannu baka hannu kwarya cikin dan lokaci ta cinye tas ta zura dogon Hijab har qasa ta fita tana nanata La'ilaha illah anta subhanaka innikuntu minazzalimin a zuciyarta harta isa qofar Sitting room din Abbansu.
Ta shiga da sallama kai a qasa kamar ta Allah ta rabe a bakin qofa tana gaishe su ba tare data bari sun hada ido da kowa a cikin su ba. Yaya Aminu ne ya daka mata tsawa yace
"Zaki matso ciki ne kose na zo nan na tattaka ki mara jin magana kawai"
"Barta Aminullahi fada da hargagi baya gyara, nasihar dai ita zaa ci gaba har sanda Allah ze sa ta dena abinda takeyi" Taji Muryar Baba Liman Aminin Abbansu ta katse hargagin da Yaya Aminu ya fara yi mata. Wata nutsuwa taji ta dan saukar mata dan ko ba komai akwai me kareta dan baze bari su mata komai ba amma da ta gama saddaqarwa yau kashinta ya bushe dan daga Yaya Aminun har Baba Abdullahi babu me sauqi, Abba kuwa zuba ido zeyi su caskalata babu abinda ya masa zafi.
"Ina wayarki take?" Baba Abdullahi ya fada cikin zafin nan nasa, seta daga kai ta kalleshi aranta tana cewa
"Toh takunkumi zaa sakamun kenan a hanani fita a karbe mun waya tab aikuwa da sake"
"Ba magana ake miki ba?" Aminu ya sake zaburowa, qasa qasa ta harare shi kafin tace
"Tana cikin gida"
"Kije ki dakkota da duk wani abu da kika san Qasim ya mallaka miki ki kawo nan" Baba Liman ya fada.
"Duk abinda tasan nasa ne ko tsinke ne ta hado" wani mutum da sam bata lura da shi a palour bama ya fada se faman girgiza qafa yake kamar ana yaqi, Se ta dago tana kallon shi dason jin qarin bayani, amma yanayin da tagani akan fuskar Abbanta da irin hararar daya watsa mata tasa ta miqe babu shiri.
Sabuwar Iphone din da Qasim ya siya mata bayan kawo kudin auran su da kwana biyu ta dakko tana jujjuyawa, to me ya faru me zasuyi da wayar? Kuma ai ce mata aka yi ta dakko duk abinda ya mallaka mata kenan ba wai kwace wayar zaayi ba wani abun ne daban.
Tunanin me dame ma Qasim din ya taba siya mata ta shiga yi, shi ba gwanin siyan kaya bane gara dai kayan maqulashe duk zuwa da abinda ze kawo mata. Wardrobe ta bude ta zaro lesina guda biyu daya dinkakke ne dayan baa dinka ba se Atamfa guda daya itama dinkakkiya kayan toshin wannan qaramar sallar da yayi matane, ta saka Atamfar Leshin kuma daman yau tayi niyyar saka shi.
Ragowar tarkacen Jaka da takalmi da mayafai ta debo ta hada cikin babbar Leda, ta kalli turarukan dake kan Mudubin su wanda suma a cikin kayan take ta tabe baki a fili tace